← Book details Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 58

Sashe 25

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ba ta ƙarisa ba na ɗauki pillown kujerar na jefa mata ta fice cikin sauri tana ƙyalƙyala dariya. Tsaki na ja kafin na tashi na shiga ɗaki wajen Umma tana tsaye tana duba cikin kayanta na iske ta da alama wani kayan take nema. Na tsuguna kafin na ce"Umma ga can abinci na gama a kawo miki nan ne, ko za ki fito?". Kamar ba za ta amsa mini ba sai can kuma ta yi magana kamar wacce aka yi wa dole.
"Me ye kika dafa?".
"Taliya". Na amsa da shi kaina yana ƙasa.

"Ba na jin sha'awar cin taliya ki je ki cinye kawai. Idan Manniru ya dawo sai ya je ya sayo min fankasau da miya".

"Fankasau kuma Umma? A cikin wannan daren a ina za a samu a nan kusa". Na yi maganar da ban san lokacin da ya fito daga bakina tsabar kaÉ—uwar da na yi da zancen. Ta bar abin da take yi ta juyo tana kallo na kamar wacce ta yi tozali da wani abun al'ajabi.
"Amatullah ba ni da ƴancin cin abin da raina yake so kenan a cikin gidana?". Na jijjiga mata kaina"a'a Umma amma wallahi ba a sayar da irin wannan nau'in abincin a nan kusa. Kuma kin ga Abba idan ya dawo yana buƙatar hutu, don Allah ki yi haƙuri ko awara ce sai na karɓo miki a wajen Amira....".

Kafin na rufe bakina na ji sauƙar mari a kuncina da ya gigita ni da na yi zaman dirshan. Cikin kauraran amo ta soma magana tana nuno ni da ƴar manuniyar ƴatsata.
"Na yi miki iyaka da shi shiga abin da babu ruwanki mussamman abin da ya shafi tsakanina da mahaifinki. Duk abin da zan yi a cikin gidana na ki ido ne, idan kuwa kin yi kunnen uwar shegu da zancen ai jiki magayi".

"Ki yi haƙuri Umma ban yi don na ɓata miki rai ba. Don Allah ki yafe mini". Rufe bakina ya yi daidai da sa'ilin da Abba ya shigo cikin ɗakin idanuna suka sauƙa a kansa, da hakan ba wa hawayen da suka wadaci koramar idanuna damar kwaranya kamar an kunna burɗaɗɗan famfon burtsatse.

"Lafiya na gan ku haka duk a hargitse?".

Umma ta buga wani uban tsaki tamkar wacce ta yi arba da kashi, ta juya ta ci gaba da abin da take yi. Na tashi ina yi Abba sannu da zuwa na kai hannu zan amshi ledar da yake hannunsa ya dakatar da ni.
"A'a wannan saƙon Ummanki ne". Ya juya yana fuskantar inda take kafin ya zarce da cewa"Hafsatu ga abin da kika buƙata na taho miki da shi".Ta ɗaura hannu aka ta buga salati da sallallami.

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un! Ni kam na shiga tara ma ba uku ba, wai a cikin ɗakina ma ba za a bar ni na huta ba. Manniru me ye kake so da ni ne? Kai ƙaramin yaro ne ko mene ne. Don ka sayo min kilishi shi ne sai na amsa da hannu ko me ye kake so da ni? To ba na cin kilisin fankasau da miya raina yake so".

"Fankasau kuma Hafsatu?".

"Ƙwarai kuwa".

Ya yi shuru yana jijjiga kansa bai ce komai ba ta juya ya fita daga ɗakin. Dole ni ma na tashi na fita na yi sauri na cimma Abba a zaure yana ƙoƙarin fita.
"Don Allah Abba ka koma ka huta yanzu fa ka dawo cikin gidan, bai dace ka ƙara fita ko'ina ba. Ka ba ni kuɗin ni zan je na nemo mata fankasau ko a ina ne a cikin garin nan".

Ya tsaya kawai yana kallo hasken farin watan da ya gauraye ko'ina shi take ba ni damar kallon fuskarsa tar.
"Amatullah ni ya dace na fita na nemo mata, don haka ki koma ciki ki zauna. Ki kwantar da hankalinki babu abin da zai faru da ni". Zan yi magana ya É—aga mini hannu"ki koma kawai".
Muna cikin haka Amira ta shigo ta gaishe da Abba ya amsa mata a taƙaice da ido na yi mata alama akan babu lafiya. Hakan ya sa tambayar Abba ko lafiya.

"Lafiya lau Amira zan É—an fita ne amma yanzu zan dawo".

"Abba idan wani abun kake buƙata ka ba mu mana sai mu je mu nemo maka..". Tun kafin ta ƙarisa ya taka mata burki"ku shiga gida kawai na ce".
"Ko mun shiga hankalinmu ba zai kwanta ba matuƙar muka bar ka fita yanzu. Abba tun safe fa kake aiki kamata ya yi yanzu ka zauna ka huta, yayin da mu kuma za yi maka hidima". Ya yi ɗan jim yana kallon ta sai dai bai ce ko kanzil ba.
"Me ye amfaninmu idan ba za mu iya samar maka da nutsuwa ba. Amfanin haihuwar kenan fa Abbanmu, ka sanar da ni abin da za a sayo maka matuƙar akwai shi a cikin garin nan sai na kawo maka shi gabanka kafin ka kwanta bacci".

Ya ja dogon numfashi ta fesar kafin ya ce"to shikenan fankasau da miya nake so, amma kar ku bata lokaci idan ba ku samu ba ku dawo kawai". Ya kai aya yana zaro naira dubu ɗaya daga aljihunsa ya miƙa mata ta ƙarba kana shi kuma ya koma ciki. Tana wucewa ta ja hannuna muka fita waje muka tsaya.
"Sanar da ni me ye yake faruwa ne?".
"Amira mu fara neman fankasau ɗin tukunna. Yanzu a ina kike ganin za a samu?". Ta yi shuru kamar mai nazarin wani abun kafin can ta ce"zo mu je akwai inda nake da yaƙinin za mu samu".

"To soyar awaran fa?".

"Na gama don yau na fita a sa'a. Tun kafin na fara soyawa aka saye ta dukka". Tana kai wa aya ta ja hannuna da ƙarfi muka bar wajen.
[8/10, 3:10 PM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*

©️ Maimuna Tijjani Iyam

_____________________________________

Page 2️⃣0️⃣

Tafiya muka soma yi bar cikin layin gabaɗaya muka tsaya a bakin kwalta, zan iya rantsuwa akan cewar tun da uwata ta haife ni ban taɓa fitowa wajen a irin wannan lokacin ba sai ga shi yau ƙaddara ta jayo ni inda ƙafafuna ba su taɓa tunanin zuwa ba.
Na cika da mamakin ganin yadda Æ´an mata da samari suke ta wucewa daga wajen yayin da wasu kuma suke hira har da masu yin hoto.
"Amira yau ina za mu je da muka zo nan muka tsaya?".
"Fankasau za mu nema mana Amatullah". Na tsayar da idona akan ta"ban ga alamar abin da abin da kika faÉ—a ba"
Ta fito da wayarta ta soma latsawa tana ƙiran wani layi bugun farko aka ɗaga aka fara magana.
"Amira zah big girl yaya aka yi".

"Babe gani a bakin hanya ka fito in kana kusa".
"To ranki ya daɗe". Ya amsa da shi a taƙaice yana kashe wayar, mintuna kaɗan tsakani ya iso waje sosai na tsorita da ganin yanayinsa don babu alamar nutsuwa ko kaɗan a tattare da shi balle a yi zaton samun sanin hukuncin addini a tattare da shi.
"Bane ya me ye da akwai ne?". Ta shagwaɓe fuska kafin ta soma cewa"fankasau nake son ci a cikin daren nan". Ya waro idanu waje kafin ya fashe da dariya har da tafa hannun.
"Fankasau kuma Babe? Yanzu ina zan sama fankasau a cikin daren nan. Ni tukunnan ma me ye wannan fankasau É—in nan ne da ya É—ag miki hankali cikin daren nan har kika fito?".

"Ni dai wallahi ji nake yi kamar zuciyata za ta fashe idan ban ci fankasau ɗin nan ba". Bai ce komai ba illa dariyar da ya ci gaba da yi yana tafa hannu tare da shafa ƙasuban da ya yi wa fuskarsa ƙawanya.
Ta riƙo hannuna ta riƙe gam a cikin nata tana dubansa ta ce"dole ka tisa ni gaba kana yi min dariya ai tun da kana magana da mahaukaciya wacce ba ta san abin da nake yi ba, duk duniya kai ɗaya na zaɓo kamar tumu. Tun ka nuna gazawarka a gare ni na gode Almustapha".

Za mu wuce kawai na ga ya riƙo ɗayan hannun natan ya riƙe. Na cika da mamakin ganin ba ta dakatar da shi ba balle ta yi wani yunƙurin tsawatar masa.
"Common Babe ai duk inda fankasau yake a cikin garin nan sai na nemo miki shi. Ina zan tsoma raina na ji sanyi ahalin kina fushi da shi, bari na É—auko mota sai mu je global delight na san babu abin da za a rasa a nan".

Ta yi banza da shi ba tare da ta tanka masa ba. Ya wuce ya bar wajen da hakan ya ba ni damar furzar da abin da ya tokare mini ƙirjina.
"Ke wai ina zamu je har da mota? Ki rufa mana asiri Amira".
"Nan kusa ne fa yanzu za mu dawo ai". Kafin na yi wani magana tunin har ya iso wajen da mota ta ja hannuna muka isa wajen muka shiga gidan bayan saboda akwai abokinsa zaune a kujerar mai zaman banza. Muna shiga cikin motar ya fige ta tamkar zai tashi sama ya cilla motar a bisa titi.

"Babe wannan ƙawar takin ba ta magana ne?".

Kalamansa suka dawo da ni cikin duniyar zahiri daga na tunanin da na faÉ—a.
"Amatullah ba ta cika magana ba ne shi yasa".

Abokin nasan ya amshe zancen"au sunanta Amatullah kenan? Sunan a dace da ita. Kyakkyawan sunan da kyakykyawar halitta ya dace daman". Ban kula su saboda tsoron da ya gama cika ni duk gudun da yake yi ji nake yi kamar ba sauri, ban ce komai ba har sai da na ga ya tsaya ya faka motar a cikin wani babban fili gefe guda ina hango wani babban wajen da aka rubuta sunan wajen da manyan harrufa suna wani walwal da wuta yana sauya kala daga ja zuwa shuÉ—i.
"To Babe mu je ko". Almustapha ya furta yana ɓalle murfin motar ya fita Amira ita ta fita, ya rage daga ni sai abokinsa a cikin motar. Zuciyata sai bugawa take yi haka siddan na gaza gano dalilin harbawanta fiye da kima.

"Ƴan matan mu yi amfani da wannan lokacin mana kafin su fito".
Chapter 25 · 0% Book details