Sashe 54
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wai kurame kuka zama ne ko kuwa? Cikinku babu wanda zai amsa min tambayoyina". Anty Sawwama ta ƙara buga musu wani tambayar muryarta har ta na harɗewa waje guda.
"Umma ku shiga ciki za a shigo da shi". Ina yin wannan furucin na Yaya Alhassan na zabura tamkar wacce aka tsigarawa alluran doki. Na miƙe har ina ƙoƙarin faɗuwa na fito waje daidai lokacin da wasu maza biyu suka shigo da mutum cikin lulluɓi farin ƙyale, Amir ya ɗauko tabarma ya shimfiɗa suka kwantar da shi, mazan suka fita ya rage daga m sai ya mu.
"Wane ne wannan Alhassan? Alhassan kar ka ce min gawan Manniru ne kwance a nan. Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Daman da kuke cewa za ga ku nan za ku dawo ɗin gawarsa za ku dawo da shi". Anty Sawwama ta yi kalaman cikin tsananin ruɗani da kaɗuwa, Anty Zulaihatu kam ta kasa magana sai kukan da nake yi, ganin yadda na tsaya a waje ɗaya na kasa gaba balle baya ya sa ta iso gare ni ta riƙo ni.
"Amatullah sai dai mu yi haƙuri". Tun kafin ta gama maganar na fizge jikina daga riƙon da ta yi mini kamar mai aljanu ko iskokai haka na ƙanƙame ta ƙam ta gaza motsawa balle ta yi wani yunƙurin ƙwacewa.
"Abba bai rasu ba, ba shi ba ne bari na buÉ—e miki ki gani ba shi ba ne fa Anty Sawwama ku daina wannan kukan".
Na kai aya ina jan ƙafafuna da nake ɗagawa da ƙyar na je zan buɗe gawan Yaya Alhassan ya riƙe hannuna jikina har wani jijjiga yake yi tamkar mazari.
"Kar ka hana ta Alhassan ka bar ta ta buɗe". Anty Sawwama ta furta dole yaya Alhassan ya cika ni na je na durƙushe a gaban gawar haka kawai tun kafin na buɗe na ji ƙirjina yana tsananta bugu tamkar zai faso allon ƙirjin ya bayyano waje ya daka rawar disko. Duk yadda hawaye suka wadai kurmin idanuna ƙarfi hali da bushewar da zuciyata ta yi ya hana sa zuba, don ba na son na gaskata abun da su Anty Sawwama suke yi wa kuka. Jikina gabaɗaya yana rawa na kai hannu na buɗe dirsham na zame na yi zaman ƴan bori hawayen da nake riƙewa suka zama lasisin yin gudun famfalaƙi a bisa fuskata.
"Abba don girman Allah ka tashi kar ka tafi ka bar ni a cikin wannan yanayin. Abba kar ka yi mini haka ni kuwa ina zan tsoma kaina idan na waiga ban ganka a kusa da ni ba, don Allah ka buɗe idanunka ka tashi kar ka tafi". Na kifa kaina a saman ƙirjinsa ina kuka ji nake yi numfashi yana cushewa tamkar an ɗaure mini wuyana da ya kasance hanyar shiga da fitan numfashina.
"Amatullah haƙuri za mu yi Kawu kuma lokaci ya yi wanda ya fi mu sonsa ya karɓe rayuwarsa. Sai dai mu yi masa addu'ar Allah ya kyautata makwancinsa idan lokacin mu ya yi mu kuma Allah ya ba sa mu cika da imani".
Raɗau na ji maganar a na'urar naɗan sautina sai dai na kasa tantance waye mamallakin murya. Kukan kawai nake yi duk da hawaye ba sa fita daga idanuna amma ina jin zafi a cikin ƙirjina tamkar ana watsa mini garwashin wuta, na ji an ɗago ni sai dai na kasa tsayiwa akan ƙafafuna ana ɗago ni nake faɗuwa, aka Anty Zulaihatu ta riƙe ni muka shiga cikin ɗaki take numrashina ya soma ɗauke wa. Jikina ya soma jijjiga sai da ta dafa kaina tana karanto karatun suratul baƙara tana tofa mini a hankali na soma yi kamar an warware mini tirniƙin da ya zarge mini maƙoshina. Na koma kamar gunki babu wani gaɓa a jikina da yake motsawa face idanuna da suka kafe babu ɗigon baƙi a kaɗan a cikinsa ya juya zuwa launin fari fat. Sai da ta nem ruwa ta yi tofi a ciki ta shafa mini a jikina da ya sake ba shi da maraba da bishiyar da ta baza jijiyoyinta a ƙarƙashin ƙasa. Ba ta gushe ta na yi mini har sai da na ji nauyin da ƙirjina ya yi mini ya taguwa har na iya tashi da kaina na zauna. Na kasa kuka da hawaye illa na zuci da nake yi.
Anty Sawwama ta shiga tararradin yadda za a sanarwa Ummata labarin rasuwar Abba, daga ƙarshen dai aka yanke shawarar aika Umar ya je ya ƙira ta. Babu jimawa suka dawo tare Anty Sawwama ta zaunar da ita ta yi mata dukkan nasiha cikin sigar mai jan hankali kafin daga ƙarshe ta sanar da ita labarin rasuwar. Ban ga tsananin kaɗuwa a fuskarta ba illa miƙe wa da ta yi ta nufo ni, na yi zaton runguma na za ta yi na ji ɗumin jikinta ko zan ji sauƙi yanayin da nake ciki sai dai na ci karo da saɓanin tunani da hashashena.
Ta wanke ni da wani mahaukacin marin da har sai da ɗan kunnena ya faɗi ƙasa na dafe kuncina.
"Amatullah shikenan hankalinki ya kwanta kin yi silar mutuwarsa. Ya tafi ya bar miki duniyar sai ki yi yadda kike so....". Na riƙe ƙafarta ina kuka mai haɗe da magiya.
"Don Allah ki taimake ni ki taimaki rayuwata kar ki yi silar rugujewan ta gabaɗaya". Ban ta ce da ni komai ba ta zare ƙafarta daga riƙon da na yi mata ta juya tana fuskantar Anty Sawwama.
"Ku yi zaman makokinku anan ni ma zan je na yi nawa a can."
"Haba Hafsatu me ya yi zafi haka shi ba wuta ba?. Me zai hana duk mu zauna a nan tunda nan É—in ma ya fi fili".
A zafafe Umma ta mayar mata da martani"in kun ga dama ku tafi bangon duniya ku yi na ku zaman makokin amma ni a É—akina zan yi. Babu dalilin da zai sa na zo na tare a gidanku tun da wanda ya haÉ—a ya raba".
"Haba! Anty Hafsatu ki yi haƙuri mana da nan da can ɗin ai duk ɗaya ne. Kar ki manta fa ga Kawu can a kwance ko kai sa ba ayi ba kike wannan maganar". Amir ya yi zancen hawaye suna ciko masa kurmin idaniya, tsaki Umma ta buga bayan ta gama jifan mu da harara ta sa kai za ta fice, Yaya Alhassan ya dakatar da ita ta hanyar faɗin" za ki tsaya dai ku yi bankwana da shi ki yi masa kallon ƙarshe tare da addu'o'i".
"Zan iya masa addu'a daga duk inda nake kuma ta iske shi har cikin kushewarsa". Tana dasa aya a nan ta yi ficewar. Kalmar innalillahi wa inna ilahirin raji'un kawai Anty Sawwama take ta maimata jiri ya ɗebe ta za ta faɗi Amir ya riƙe ya zaunar da ita.
"Umma a ina za a yi jana'izar kenan?".
"Amir ya ya muka iya dole mu yi yadda take so, tun da a wancan unguwan aka san shi kuma a can yake zaune aje can kawai a yi masa salla a ƙofan gidan. Allah ya jiƙanka Manniru Allah ya kyautata makwancinka halinka na gari ya fita".
"Amin ya Allah" .
Duk muka haɗe baki wajen furta, Yaya Alhassan da Amir suka fita suka nemo mota aka tafi da gawar can unguwanmu Umar ya sanar da dangi labarin rasuwar, muka bi bayan su mu ma zuwa can unguwanmu. Muna karyo kwanar gidan na ga an kafa rumfuna har guda uku a ƙofar gidanmu ga mutane maƙil a wajen wasu suna zaune, wasu suna alwala wasu kuma su na tsaye jikina gabaɗaya ya yi sanyi ƙalau. Ban taɓa zaton haka mutuwa take da zafi ba sai yau da ta raba ni da jigon rayuwata.
Muna shiga cikin gidan muka tarar da taron mata, yau ne rana ɗaya tal da na ga nutsuwa a tattare da matan gidan kowacce tana zaune a ƙofar ɗakinta cikin jimami har da masu kuka wiwi da hawaye don a tsawon shekarun da muka yi a gidan Abba ya zauna da kowa lafiya cikin aminci da girmamawa.
Amira ta taso muka rungume juna muna kuka kowa sai da ya tausaya mana, aka ce mu shiga cikin muka shiga É—akin Ummanta don É—akinmu ya cika da mutane babu masaka tsinke. Mun daÉ—e muna kukan har sai da na kasa buÉ—e idanuna saboda yadda suka kumbura ji nake yi tamkar ni ma ba zan kai zuwa yamma a raye ba.
Umman Amira ta shigo ta ce mu zo mu yi wa Abba addu'a za a tafi da shi, ko da na fita na kasa taɓuka komai illa kwantar da kaina da na yi a jikin makaran, bakina ya kasa cewa komai addu'ar ma a cikin zuciyata na dinga yi masa.
Da ƙyar aka ɓaɓɓare ni daga jikin makarar, ina da ilmin cewar mamaci ba a nuna masa ƙauna da hanyar yi masa kuka. Wannan dalilin ya sanya yi ƙarfafa zuciyata na dinga karatun duk wani addu'ar da ya zo bakina a lokacin ina yi. Ban yi aune ba na ji an rufe ni da duka ta ko'ina tun ina kare kaina har na sadadu na baje a ƙasa. Idanuna suka soma gano mini Umma da ta kau saman ruwan cikina tana ta jibga duk da yadda mutane suka yi tururuwa suna janye ta amma ba ta fasa abin da ta yi niyya ba.
"Ku bar ni na kashe matsiyaciya wacce ba ta yi gadon abin azirki ba. Ku bar ni na kashe ta don babu amfani rayuwarta gwara na kawar da ita".
Da ƙyar mutane suka taru suka janye Umma daga kaina, lokacin har na fita daga cikin hayyacina na ji ɗumin wani abu mai ruwa yana bin tsakanin cinyoyina yana sauƙar har izuwa dugadugaina. Aka ɗaga ni na kasa tsayiwa na lu na faɗi.
Tun daga sa'ilin nan ban ƙara sanin inda kaina yake ba sai farkawa na yi na ganni a gadon asibiti da Anty Zulaihatu da Amira a kusa da ni, ina buɗe ido suka soma yi mini sannu wani bin wani kana Amira ta je ta ƙira likita ya zo ya ƙara duba ya kuma tabbatar da cewar babu wani damuwan.
"Umma ku shiga ciki za a shigo da shi". Ina yin wannan furucin na Yaya Alhassan na zabura tamkar wacce aka tsigarawa alluran doki. Na miƙe har ina ƙoƙarin faɗuwa na fito waje daidai lokacin da wasu maza biyu suka shigo da mutum cikin lulluɓi farin ƙyale, Amir ya ɗauko tabarma ya shimfiɗa suka kwantar da shi, mazan suka fita ya rage daga m sai ya mu.
"Wane ne wannan Alhassan? Alhassan kar ka ce min gawan Manniru ne kwance a nan. Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Daman da kuke cewa za ga ku nan za ku dawo ɗin gawarsa za ku dawo da shi". Anty Sawwama ta yi kalaman cikin tsananin ruɗani da kaɗuwa, Anty Zulaihatu kam ta kasa magana sai kukan da nake yi, ganin yadda na tsaya a waje ɗaya na kasa gaba balle baya ya sa ta iso gare ni ta riƙo ni.
"Amatullah sai dai mu yi haƙuri". Tun kafin ta gama maganar na fizge jikina daga riƙon da ta yi mini kamar mai aljanu ko iskokai haka na ƙanƙame ta ƙam ta gaza motsawa balle ta yi wani yunƙurin ƙwacewa.
"Abba bai rasu ba, ba shi ba ne bari na buÉ—e miki ki gani ba shi ba ne fa Anty Sawwama ku daina wannan kukan".
Na kai aya ina jan ƙafafuna da nake ɗagawa da ƙyar na je zan buɗe gawan Yaya Alhassan ya riƙe hannuna jikina har wani jijjiga yake yi tamkar mazari.
"Kar ka hana ta Alhassan ka bar ta ta buɗe". Anty Sawwama ta furta dole yaya Alhassan ya cika ni na je na durƙushe a gaban gawar haka kawai tun kafin na buɗe na ji ƙirjina yana tsananta bugu tamkar zai faso allon ƙirjin ya bayyano waje ya daka rawar disko. Duk yadda hawaye suka wadai kurmin idanuna ƙarfi hali da bushewar da zuciyata ta yi ya hana sa zuba, don ba na son na gaskata abun da su Anty Sawwama suke yi wa kuka. Jikina gabaɗaya yana rawa na kai hannu na buɗe dirsham na zame na yi zaman ƴan bori hawayen da nake riƙewa suka zama lasisin yin gudun famfalaƙi a bisa fuskata.
"Abba don girman Allah ka tashi kar ka tafi ka bar ni a cikin wannan yanayin. Abba kar ka yi mini haka ni kuwa ina zan tsoma kaina idan na waiga ban ganka a kusa da ni ba, don Allah ka buɗe idanunka ka tashi kar ka tafi". Na kifa kaina a saman ƙirjinsa ina kuka ji nake yi numfashi yana cushewa tamkar an ɗaure mini wuyana da ya kasance hanyar shiga da fitan numfashina.
"Amatullah haƙuri za mu yi Kawu kuma lokaci ya yi wanda ya fi mu sonsa ya karɓe rayuwarsa. Sai dai mu yi masa addu'ar Allah ya kyautata makwancinsa idan lokacin mu ya yi mu kuma Allah ya ba sa mu cika da imani".
Raɗau na ji maganar a na'urar naɗan sautina sai dai na kasa tantance waye mamallakin murya. Kukan kawai nake yi duk da hawaye ba sa fita daga idanuna amma ina jin zafi a cikin ƙirjina tamkar ana watsa mini garwashin wuta, na ji an ɗago ni sai dai na kasa tsayiwa akan ƙafafuna ana ɗago ni nake faɗuwa, aka Anty Zulaihatu ta riƙe ni muka shiga cikin ɗaki take numrashina ya soma ɗauke wa. Jikina ya soma jijjiga sai da ta dafa kaina tana karanto karatun suratul baƙara tana tofa mini a hankali na soma yi kamar an warware mini tirniƙin da ya zarge mini maƙoshina. Na koma kamar gunki babu wani gaɓa a jikina da yake motsawa face idanuna da suka kafe babu ɗigon baƙi a kaɗan a cikinsa ya juya zuwa launin fari fat. Sai da ta nem ruwa ta yi tofi a ciki ta shafa mini a jikina da ya sake ba shi da maraba da bishiyar da ta baza jijiyoyinta a ƙarƙashin ƙasa. Ba ta gushe ta na yi mini har sai da na ji nauyin da ƙirjina ya yi mini ya taguwa har na iya tashi da kaina na zauna. Na kasa kuka da hawaye illa na zuci da nake yi.
Anty Sawwama ta shiga tararradin yadda za a sanarwa Ummata labarin rasuwar Abba, daga ƙarshen dai aka yanke shawarar aika Umar ya je ya ƙira ta. Babu jimawa suka dawo tare Anty Sawwama ta zaunar da ita ta yi mata dukkan nasiha cikin sigar mai jan hankali kafin daga ƙarshe ta sanar da ita labarin rasuwar. Ban ga tsananin kaɗuwa a fuskarta ba illa miƙe wa da ta yi ta nufo ni, na yi zaton runguma na za ta yi na ji ɗumin jikinta ko zan ji sauƙi yanayin da nake ciki sai dai na ci karo da saɓanin tunani da hashashena.
Ta wanke ni da wani mahaukacin marin da har sai da ɗan kunnena ya faɗi ƙasa na dafe kuncina.
"Amatullah shikenan hankalinki ya kwanta kin yi silar mutuwarsa. Ya tafi ya bar miki duniyar sai ki yi yadda kike so....". Na riƙe ƙafarta ina kuka mai haɗe da magiya.
"Don Allah ki taimake ni ki taimaki rayuwata kar ki yi silar rugujewan ta gabaɗaya". Ban ta ce da ni komai ba ta zare ƙafarta daga riƙon da na yi mata ta juya tana fuskantar Anty Sawwama.
"Ku yi zaman makokinku anan ni ma zan je na yi nawa a can."
"Haba Hafsatu me ya yi zafi haka shi ba wuta ba?. Me zai hana duk mu zauna a nan tunda nan É—in ma ya fi fili".
A zafafe Umma ta mayar mata da martani"in kun ga dama ku tafi bangon duniya ku yi na ku zaman makokin amma ni a É—akina zan yi. Babu dalilin da zai sa na zo na tare a gidanku tun da wanda ya haÉ—a ya raba".
"Haba! Anty Hafsatu ki yi haƙuri mana da nan da can ɗin ai duk ɗaya ne. Kar ki manta fa ga Kawu can a kwance ko kai sa ba ayi ba kike wannan maganar". Amir ya yi zancen hawaye suna ciko masa kurmin idaniya, tsaki Umma ta buga bayan ta gama jifan mu da harara ta sa kai za ta fice, Yaya Alhassan ya dakatar da ita ta hanyar faɗin" za ki tsaya dai ku yi bankwana da shi ki yi masa kallon ƙarshe tare da addu'o'i".
"Zan iya masa addu'a daga duk inda nake kuma ta iske shi har cikin kushewarsa". Tana dasa aya a nan ta yi ficewar. Kalmar innalillahi wa inna ilahirin raji'un kawai Anty Sawwama take ta maimata jiri ya ɗebe ta za ta faɗi Amir ya riƙe ya zaunar da ita.
"Umma a ina za a yi jana'izar kenan?".
"Amir ya ya muka iya dole mu yi yadda take so, tun da a wancan unguwan aka san shi kuma a can yake zaune aje can kawai a yi masa salla a ƙofan gidan. Allah ya jiƙanka Manniru Allah ya kyautata makwancinka halinka na gari ya fita".
"Amin ya Allah" .
Duk muka haɗe baki wajen furta, Yaya Alhassan da Amir suka fita suka nemo mota aka tafi da gawar can unguwanmu Umar ya sanar da dangi labarin rasuwar, muka bi bayan su mu ma zuwa can unguwanmu. Muna karyo kwanar gidan na ga an kafa rumfuna har guda uku a ƙofar gidanmu ga mutane maƙil a wajen wasu suna zaune, wasu suna alwala wasu kuma su na tsaye jikina gabaɗaya ya yi sanyi ƙalau. Ban taɓa zaton haka mutuwa take da zafi ba sai yau da ta raba ni da jigon rayuwata.
Muna shiga cikin gidan muka tarar da taron mata, yau ne rana ɗaya tal da na ga nutsuwa a tattare da matan gidan kowacce tana zaune a ƙofar ɗakinta cikin jimami har da masu kuka wiwi da hawaye don a tsawon shekarun da muka yi a gidan Abba ya zauna da kowa lafiya cikin aminci da girmamawa.
Amira ta taso muka rungume juna muna kuka kowa sai da ya tausaya mana, aka ce mu shiga cikin muka shiga É—akin Ummanta don É—akinmu ya cika da mutane babu masaka tsinke. Mun daÉ—e muna kukan har sai da na kasa buÉ—e idanuna saboda yadda suka kumbura ji nake yi tamkar ni ma ba zan kai zuwa yamma a raye ba.
Umman Amira ta shigo ta ce mu zo mu yi wa Abba addu'a za a tafi da shi, ko da na fita na kasa taɓuka komai illa kwantar da kaina da na yi a jikin makaran, bakina ya kasa cewa komai addu'ar ma a cikin zuciyata na dinga yi masa.
Da ƙyar aka ɓaɓɓare ni daga jikin makarar, ina da ilmin cewar mamaci ba a nuna masa ƙauna da hanyar yi masa kuka. Wannan dalilin ya sanya yi ƙarfafa zuciyata na dinga karatun duk wani addu'ar da ya zo bakina a lokacin ina yi. Ban yi aune ba na ji an rufe ni da duka ta ko'ina tun ina kare kaina har na sadadu na baje a ƙasa. Idanuna suka soma gano mini Umma da ta kau saman ruwan cikina tana ta jibga duk da yadda mutane suka yi tururuwa suna janye ta amma ba ta fasa abin da ta yi niyya ba.
"Ku bar ni na kashe matsiyaciya wacce ba ta yi gadon abin azirki ba. Ku bar ni na kashe ta don babu amfani rayuwarta gwara na kawar da ita".
Da ƙyar mutane suka taru suka janye Umma daga kaina, lokacin har na fita daga cikin hayyacina na ji ɗumin wani abu mai ruwa yana bin tsakanin cinyoyina yana sauƙar har izuwa dugadugaina. Aka ɗaga ni na kasa tsayiwa na lu na faɗi.
Tun daga sa'ilin nan ban ƙara sanin inda kaina yake ba sai farkawa na yi na ganni a gadon asibiti da Anty Zulaihatu da Amira a kusa da ni, ina buɗe ido suka soma yi mini sannu wani bin wani kana Amira ta je ta ƙira likita ya zo ya ƙara duba ya kuma tabbatar da cewar babu wani damuwan.