Sashe 36
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zumbur na yi na miƙe har na riga ta fita daga cikin ɗakin, ina sanya ƙafata na fita daga cikin gidan na ji wani sanyin daɗi yana ratsa ruhina. Nauyin da ƙirjina ya yi mini yana warwarewa a hankali-hankali, gidan Ta salla muka nufa wacce take dafawa Amira awara.
Cike muka iske gidan da samari da ƴan mata, gefe guda wasu sun baje hajarsu yayin da Ta salla take zaune akan garduma gabanta da manyan kulolin abincin da take sayarwa a gida, kusa da ita muka zauna ta bi mu da kallo har muka zauna muka gaishe ta ta amsa tana zarcewa da faɗin"Amira wannan fa ina kika samo ta?". Ta kai ƙarshen zancen tana nuna ni da ƴar manuniyar ƴatsarta.
"Au! Wannan É—in ce ba ki gane ta Hajiya? Amatullah ce fa ta gidanmu".
Ta tafa hannu gami da rafza salati ta riƙe haɓa cikin mamaki ta ce"lalle girman ɗan mutum ba shi da wuya yanzu Amatullah ɗin Hafsatu ce ta girma har haka? Lalle muna da ƴan mata a unguwan zankaɗa-zankaɗa sai mu yi fatan Allah ya baku mazaje na gari".
"Amin ya Allah".
Muka haɗe baki wajen amsawa, sai a lokacin na sama damar ƙarewa tsari da zubi gami da irin mutanen da suke cikin gidan, a ƙalla mutane za su kai ashirin muka iske a gidan kowa yana harkan gabansa daga fahimtar da na yi ma wasu a gidan suke kwana.
"Har yanzu muna gidan nan nakun ashe? Ciki da falo ne kaman ai ko?". Tambayar da Ta salla ta jefo mini kenan da ya dawo da ni daga cikin karatun wasiƙan jakin da na faɗa.
Na sadda kaina ƙasa na ce"e ciki da falo ne kawai, ai duk ɗakunan gidan ma haka ne".
"Ai kuwa wannan akwai takura a ciki yanzu haka kuke cakuɗuwa da iyayen nakun duk a ɗaki ɗaya?". Kunya ta hana ni cewa komai yayin da Amira babu abin da take yi face dariya har da ƙyalƙyalewa.
Tashin samun amsa daga gare ni ya ba ta lasisin ci gaba da cewa"ai kuwa gwara tun wuri ku nemawa kanku mafita. Ga ku Æ´an mata da ku amma ace har yanzu kuna raba É—aki da iyayenku. Ai gwara ku É—inga zuwa nan kuna kwana".
"Kwana kuma a nan Hajiya?". Na furta babu shiri ina ware girman idona akan fuskarta da ta gaji da jin man bleaching har ya saduda ya daina amsar man, ta yi jajir da ita tamkar ƙosan da ya ji jawa.
"Ƙwarai kuwa ƴan mata nawa ne akan layin nan suke kwana a cikin gidan nan. Kai wasu ma gabaɗaya rayuwarsu a cikin gidan nan suke gudanar da ita".
Na sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya ina satan kallon Amira na ga hankalinta ba ma a kanmu yake ba. Sai da na haɗo jarumta kafin na iya furta"Hajiya haka dai za mu ci gaba da haƙuri har Allah ya kawo mana mafita, ko kuma mazaje mu yi aure mu tafi gidajenmu".
Ta taɓe baki"to Allah ya kyauta".
"Amin".
Na amsa da shi a taƙaitacce, ba ta ƙara cewa da ni komai illa mayar da idonta kan Amira ta yi ta umarce ta da ta tashi ta ɗauko kwana ta zubo mana abinci na ce na ƙoshi da ƙyar ta tilasta mini akan sai na ci na saka hannu na ɗan caccakala abincin sai da muka yi sallan isha'i kafin muka fito za mu tafi. Cike ƙofar gidan yake da masu jaura babu wani nau'in abincin da ba a sayarwa a wajen, ƴan shaye-shaye sun yi bataliya a wajen sai cin karensu suke yi babu babbaka.
Gabaɗaya jikina ya yi sanyi luƙus haka har muka isa gida jikina babu kuzari ba mu iso gida sai kusa ƙarfe tara da wasu mintuna na dare. Muna shiga gidan tun daga zaure na fahimci Abba ya dawo gaba ya soma faɗuwa har muka ƙarisa ciki. A ƙofar ɗakinmu na hango Abba yana tsaye ya naɗe hannayensa a bayansa idanunsa akan hanyar shigowa take na sha jinin jikina na kasa ɗago kaina. Ko gaisuwar da Amira ta yi wa Abba bai amsa ba ya juyo ya shige ciki ya bar ni cikin tarin fargaba.
"Amira na shiga uku, me ye zan cewa Abba?".
Na yi zancen a rikice muryata har yana shaƙewa tsabar rikicewar da na yi. Ta riƙo hannuna saboda gabaɗaya jikina rawa yake yi tamkar wacce aka jonawa wutar lantarki.
"Ki kwantar da hankalinki mana komai zai zo da sauƙi. Idan ya tambaya ki ce raka yi kika gidan Sa'ade mu kai zubin adashen Ummata".
"Amira ke ma kin san ai dole ne ya tambaya".
"Ki nutsu kawai don in dai kika shiga a wannan yanayin duk abin da za ki faÉ—a ba zai shiga kansa ba".
Kaina kawai na jinjina mata alamar na ji muka yi wa juna sai da safe kafin na shiga cika. Sai na da na aro jarumta da ƙarfin hali na yafawa kaina kafin na sama ƙwarin gwiwan shiga ciki bakina ɗauke da sallamar da sai na yi baki biyu kana a yunƙuri na uku na ji Abba ya amsa mini tare da ba ni iznin shigowa. Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka na shigo cikin falon kaina a ƙasa kamar wacce ta ƙullawa Sarki sharri na zo na zauna ina yi masa sannu da zuwa maimakon ya amsa mini sai ya jefo mini tambaya.
"Daga ina kuke?".
"Na'am".
"Na ce daga ina kuke a cikin daren nan?". Ya kuma maimata mini tambayar a karo na biyu cikin tsawar da ya haifar mini da runtse idanuna.
"Abba ka yi haƙuri".
Na furta hawaye masu É—umi suna gangarowa daga kurmin idaniyata.
"Ba abin da na buƙata ba kenan. Amatullah daga ina kuke kuma waye kika tambaya kafin ki yi?". Sosai jikina ya ɗauki kyarma don duk ranar da Abba ya ƙira sunana kai tsaye to tabbas magana ce mai girma zai yi da ni ko kuma ransa ya kai maƙura wajen tunzura.
"Wai me yake faruwa ne nake jin ka na ta É—aga murya?".
Furucin Umma kenan yayin da take fitowa daga cikin É—aki ta iso cikin falon ta zauna, Abba ya irge mata komai da ya wakana.
"Don ta fita shi ne kake ta tada jijiyoyin wuya haka Manniru? So kake yi mu garƙame ta a cikin gidan mu dafa ta mu cinye kenan?. Ni fa ba zai yiyuwa ka tisa min ƴa a gaba kana ɗaga mata murya ba ba zai yiyuwa. Kai ba ka bar ni ba ƴan uwanka ma ba su bar ni ba, da wanne kuke so na ji ne?".
"Hafsatu ki bar ni da yi iko da ƴarta don ni Allah ya ɗaurawa nauyin kula da tarbiyanta. Ba zai yiyu na zuba ido ina ji ina gani ta lalace ba, wani abu ne zai fitar da ita da dare wanda ba ta yi sa ba tun ido na ganin ido?. Daga yau sai yau idan na ƙara dawowa ban tarar da Amatullah a cikin gidan nan daga ke har ita sai na saɓa muku saɓawa mafi muni".
Tsam Umma ta miƙe tamkar kububuwa jikinta har wani rawa yake yi ta nuna Abba da ƴatsarta haɗe da cewa"Manniru ba ka isa ba wallahi ka yi tsararo".
"Ai kuwa yau zan nuna miki cewa na isa a gidana". Ya yi zancen shi ma yana miƙewa akan ƙafafunsa cikin tsananin ɓacin rai.
Ta matsa kusa da shi tana nuna kanta"ni kake ɗagawa murya? Ni kake kallon tsabar idona kana furta min duk abin ya fito daga bakinka? Tabbas ka kyauta kuma na gode". Tana dasa aya ta juya ta shige cikin ɗaki tare da turo ƙofar ta murza masa makulli. Cikin wani irin sauri kamar mayan ƙarfe haka Abba ya bi bayanta ya soma dukkan ƙofan yana magana.
"Hafsatu ki yi haƙuri ki buɗe ƙofar nan ki fito mu zauna mu fahimci juna. Kar ki kwanta da baƙin cikina a cikin ranki hakan sai ya fi komai ƙona min rai". Har ya yi ya gama jawabinsa Umma ba ta tanka masa ba balle ta buɗe ƙofar, haka ya yi ya gaji ya komo ya zauna ya zabga tagumi.
Na ja jikina na matso na riƙe ƙafafunsa ina kuka don yadda na so na yi masa jawabi na rasa wannan ƙwarin gwiwan, saboda kukan ya gama cin ƙarfina ainun. Da dukkan ƙarfina nake kuka da take jikina ya ɗauki zafi kaina ya yi mini wani irin nauyi tamkar an ɗaura mini dutsen dala na jihar Kano a tsakiyar kaina.
"Ki daina wannan kukan komai ya wuce ki je ki kwanta. Dare ta yi yanzu".
Ya yi zancen yana zare ƙafarsa daga riƙon da na yi masa. Ya miƙe tsaye na yi wuf na ƙara riƙe sa sai a lokacin na sama damar yin magana.
"Abba to ina za ka je?".
"Zan je masallaci na kwana, kar ki manta ki rufe ƙofar".
Yana gama faɗin haka ya fice ba tare da ya jira abin da zan ce ba. Na daɗe zaune a wajen ba tare da na motsa ba ina kuka kafin na tashi na lallaɓa na fito waje na yi alwala na koma ciki na gabatar da salla raka'a biyu. A falon na kwanta bayan na rufe ƙofar na kashe wuta, gabaɗaya na rasa gane mai yake yi mini daɗi idan na tuna Ni ce silar faruwar duk abin da ya faru sai na ji zuciyata ta ƙara karyewa hawaye sun soma ambali a kuncina.
Maganganun Hajiya Ta salla ta soma dawo mini cikin kwanyata tabbas da yanzu ina da wajen kwana da Abba ba zai fita ya kwana a masallaci ba.
[10/6, 3:36 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
_____________________________________
Page 2ï¸âƒ£8ï¸âƒ£
Cike muka iske gidan da samari da ƴan mata, gefe guda wasu sun baje hajarsu yayin da Ta salla take zaune akan garduma gabanta da manyan kulolin abincin da take sayarwa a gida, kusa da ita muka zauna ta bi mu da kallo har muka zauna muka gaishe ta ta amsa tana zarcewa da faɗin"Amira wannan fa ina kika samo ta?". Ta kai ƙarshen zancen tana nuna ni da ƴar manuniyar ƴatsarta.
"Au! Wannan É—in ce ba ki gane ta Hajiya? Amatullah ce fa ta gidanmu".
Ta tafa hannu gami da rafza salati ta riƙe haɓa cikin mamaki ta ce"lalle girman ɗan mutum ba shi da wuya yanzu Amatullah ɗin Hafsatu ce ta girma har haka? Lalle muna da ƴan mata a unguwan zankaɗa-zankaɗa sai mu yi fatan Allah ya baku mazaje na gari".
"Amin ya Allah".
Muka haɗe baki wajen amsawa, sai a lokacin na sama damar ƙarewa tsari da zubi gami da irin mutanen da suke cikin gidan, a ƙalla mutane za su kai ashirin muka iske a gidan kowa yana harkan gabansa daga fahimtar da na yi ma wasu a gidan suke kwana.
"Har yanzu muna gidan nan nakun ashe? Ciki da falo ne kaman ai ko?". Tambayar da Ta salla ta jefo mini kenan da ya dawo da ni daga cikin karatun wasiƙan jakin da na faɗa.
Na sadda kaina ƙasa na ce"e ciki da falo ne kawai, ai duk ɗakunan gidan ma haka ne".
"Ai kuwa wannan akwai takura a ciki yanzu haka kuke cakuɗuwa da iyayen nakun duk a ɗaki ɗaya?". Kunya ta hana ni cewa komai yayin da Amira babu abin da take yi face dariya har da ƙyalƙyalewa.
Tashin samun amsa daga gare ni ya ba ta lasisin ci gaba da cewa"ai kuwa gwara tun wuri ku nemawa kanku mafita. Ga ku Æ´an mata da ku amma ace har yanzu kuna raba É—aki da iyayenku. Ai gwara ku É—inga zuwa nan kuna kwana".
"Kwana kuma a nan Hajiya?". Na furta babu shiri ina ware girman idona akan fuskarta da ta gaji da jin man bleaching har ya saduda ya daina amsar man, ta yi jajir da ita tamkar ƙosan da ya ji jawa.
"Ƙwarai kuwa ƴan mata nawa ne akan layin nan suke kwana a cikin gidan nan. Kai wasu ma gabaɗaya rayuwarsu a cikin gidan nan suke gudanar da ita".
Na sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya ina satan kallon Amira na ga hankalinta ba ma a kanmu yake ba. Sai da na haɗo jarumta kafin na iya furta"Hajiya haka dai za mu ci gaba da haƙuri har Allah ya kawo mana mafita, ko kuma mazaje mu yi aure mu tafi gidajenmu".
Ta taɓe baki"to Allah ya kyauta".
"Amin".
Na amsa da shi a taƙaitacce, ba ta ƙara cewa da ni komai illa mayar da idonta kan Amira ta yi ta umarce ta da ta tashi ta ɗauko kwana ta zubo mana abinci na ce na ƙoshi da ƙyar ta tilasta mini akan sai na ci na saka hannu na ɗan caccakala abincin sai da muka yi sallan isha'i kafin muka fito za mu tafi. Cike ƙofar gidan yake da masu jaura babu wani nau'in abincin da ba a sayarwa a wajen, ƴan shaye-shaye sun yi bataliya a wajen sai cin karensu suke yi babu babbaka.
Gabaɗaya jikina ya yi sanyi luƙus haka har muka isa gida jikina babu kuzari ba mu iso gida sai kusa ƙarfe tara da wasu mintuna na dare. Muna shiga gidan tun daga zaure na fahimci Abba ya dawo gaba ya soma faɗuwa har muka ƙarisa ciki. A ƙofar ɗakinmu na hango Abba yana tsaye ya naɗe hannayensa a bayansa idanunsa akan hanyar shigowa take na sha jinin jikina na kasa ɗago kaina. Ko gaisuwar da Amira ta yi wa Abba bai amsa ba ya juyo ya shige ciki ya bar ni cikin tarin fargaba.
"Amira na shiga uku, me ye zan cewa Abba?".
Na yi zancen a rikice muryata har yana shaƙewa tsabar rikicewar da na yi. Ta riƙo hannuna saboda gabaɗaya jikina rawa yake yi tamkar wacce aka jonawa wutar lantarki.
"Ki kwantar da hankalinki mana komai zai zo da sauƙi. Idan ya tambaya ki ce raka yi kika gidan Sa'ade mu kai zubin adashen Ummata".
"Amira ke ma kin san ai dole ne ya tambaya".
"Ki nutsu kawai don in dai kika shiga a wannan yanayin duk abin da za ki faÉ—a ba zai shiga kansa ba".
Kaina kawai na jinjina mata alamar na ji muka yi wa juna sai da safe kafin na shiga cika. Sai na da na aro jarumta da ƙarfin hali na yafawa kaina kafin na sama ƙwarin gwiwan shiga ciki bakina ɗauke da sallamar da sai na yi baki biyu kana a yunƙuri na uku na ji Abba ya amsa mini tare da ba ni iznin shigowa. Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka na shigo cikin falon kaina a ƙasa kamar wacce ta ƙullawa Sarki sharri na zo na zauna ina yi masa sannu da zuwa maimakon ya amsa mini sai ya jefo mini tambaya.
"Daga ina kuke?".
"Na'am".
"Na ce daga ina kuke a cikin daren nan?". Ya kuma maimata mini tambayar a karo na biyu cikin tsawar da ya haifar mini da runtse idanuna.
"Abba ka yi haƙuri".
Na furta hawaye masu É—umi suna gangarowa daga kurmin idaniyata.
"Ba abin da na buƙata ba kenan. Amatullah daga ina kuke kuma waye kika tambaya kafin ki yi?". Sosai jikina ya ɗauki kyarma don duk ranar da Abba ya ƙira sunana kai tsaye to tabbas magana ce mai girma zai yi da ni ko kuma ransa ya kai maƙura wajen tunzura.
"Wai me yake faruwa ne nake jin ka na ta É—aga murya?".
Furucin Umma kenan yayin da take fitowa daga cikin É—aki ta iso cikin falon ta zauna, Abba ya irge mata komai da ya wakana.
"Don ta fita shi ne kake ta tada jijiyoyin wuya haka Manniru? So kake yi mu garƙame ta a cikin gidan mu dafa ta mu cinye kenan?. Ni fa ba zai yiyuwa ka tisa min ƴa a gaba kana ɗaga mata murya ba ba zai yiyuwa. Kai ba ka bar ni ba ƴan uwanka ma ba su bar ni ba, da wanne kuke so na ji ne?".
"Hafsatu ki bar ni da yi iko da ƴarta don ni Allah ya ɗaurawa nauyin kula da tarbiyanta. Ba zai yiyu na zuba ido ina ji ina gani ta lalace ba, wani abu ne zai fitar da ita da dare wanda ba ta yi sa ba tun ido na ganin ido?. Daga yau sai yau idan na ƙara dawowa ban tarar da Amatullah a cikin gidan nan daga ke har ita sai na saɓa muku saɓawa mafi muni".
Tsam Umma ta miƙe tamkar kububuwa jikinta har wani rawa yake yi ta nuna Abba da ƴatsarta haɗe da cewa"Manniru ba ka isa ba wallahi ka yi tsararo".
"Ai kuwa yau zan nuna miki cewa na isa a gidana". Ya yi zancen shi ma yana miƙewa akan ƙafafunsa cikin tsananin ɓacin rai.
Ta matsa kusa da shi tana nuna kanta"ni kake ɗagawa murya? Ni kake kallon tsabar idona kana furta min duk abin ya fito daga bakinka? Tabbas ka kyauta kuma na gode". Tana dasa aya ta juya ta shige cikin ɗaki tare da turo ƙofar ta murza masa makulli. Cikin wani irin sauri kamar mayan ƙarfe haka Abba ya bi bayanta ya soma dukkan ƙofan yana magana.
"Hafsatu ki yi haƙuri ki buɗe ƙofar nan ki fito mu zauna mu fahimci juna. Kar ki kwanta da baƙin cikina a cikin ranki hakan sai ya fi komai ƙona min rai". Har ya yi ya gama jawabinsa Umma ba ta tanka masa ba balle ta buɗe ƙofar, haka ya yi ya gaji ya komo ya zauna ya zabga tagumi.
Na ja jikina na matso na riƙe ƙafafunsa ina kuka don yadda na so na yi masa jawabi na rasa wannan ƙwarin gwiwan, saboda kukan ya gama cin ƙarfina ainun. Da dukkan ƙarfina nake kuka da take jikina ya ɗauki zafi kaina ya yi mini wani irin nauyi tamkar an ɗaura mini dutsen dala na jihar Kano a tsakiyar kaina.
"Ki daina wannan kukan komai ya wuce ki je ki kwanta. Dare ta yi yanzu".
Ya yi zancen yana zare ƙafarsa daga riƙon da na yi masa. Ya miƙe tsaye na yi wuf na ƙara riƙe sa sai a lokacin na sama damar yin magana.
"Abba to ina za ka je?".
"Zan je masallaci na kwana, kar ki manta ki rufe ƙofar".
Yana gama faɗin haka ya fice ba tare da ya jira abin da zan ce ba. Na daɗe zaune a wajen ba tare da na motsa ba ina kuka kafin na tashi na lallaɓa na fito waje na yi alwala na koma ciki na gabatar da salla raka'a biyu. A falon na kwanta bayan na rufe ƙofar na kashe wuta, gabaɗaya na rasa gane mai yake yi mini daɗi idan na tuna Ni ce silar faruwar duk abin da ya faru sai na ji zuciyata ta ƙara karyewa hawaye sun soma ambali a kuncina.
Maganganun Hajiya Ta salla ta soma dawo mini cikin kwanyata tabbas da yanzu ina da wajen kwana da Abba ba zai fita ya kwana a masallaci ba.
[10/6, 3:36 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
_____________________________________
Page 2ï¸âƒ£8ï¸âƒ£