Sashe 27
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Harara na bi Amira da shi da ta yi furucin tana sheƙewa da dariya gami da tafa hannu.
"Ke Amira ba na son rainin wayo fa, me ye hakan kuma? Yanzu wannan abun ne ya zama abin dariya a wajenki?. In ce dai da ke muka sha wuyar nemo wannan fankasau ɗin na yi tunanin ai za mu haɗu ne mu taya juna jimami da takaici, amma sai ki bige da dariya". Na ƙare zancen a kulefe don ba ƙaramin cusa mini takaici dariyar tatan ta yi ba.
"Ki yi haƙuri ƙawata, me ye laifin maganata fisabillillahi? Ai ni ina ga hakan ma abin alfahari ne gare ki da tunƙaro. Ko a gaban waye za ki tinƙaho ki bigi ƙirji domin mahaifiyarki sarauniya take a cikin a wajen mahaifinki kuma tana iya juya gidan kaman waina a bisa tanda".
Na bi ta d irin kallon da mai hankali yake yi wa zautacce kafin na furta"yanzu ke a irin tunaninki wannan abin wayewa ne?".
Ba tare da shakkan komai ba ta ce"ƙwarai kuwa, ai duk wacce kika ga mahaifiyarta ta isa da gidansu ta huta gaba da baya kuma ta wuce raini". Na jijjiga kaina tsabar takaicin da ya zarge muni wuya ya haifar nuni da wanzuwar ɗaci a cikin maƙoƙarona.
"Wani lokacin idan kina yin magana sai ki jefa ni cikin tunani, na yi ta hashashen anya kina amfani da ilmi da hankalinki kuwa wajen haɗa kalmomin da bakinki zai furta. Amira ina wayewa a cikin wannan lamarin? Yanzu fa in gaya miki gaskiya samari sun waye ko aure za su nema sai sun tabbatar da cewa uban yarinyar ya isa da gidansa, kuma yana da cikakken ikon zartar da ko wani irin hukunci ta yadda ko kara ya ajiye babu bai ƙetare shi".
"Wannan kuma ra'ayinki ne. Kin faɗi naki ni ma na faɗi nawa, don haka kowa sai ya riƙe na shi".
Tana ƙare zancen ta soma cin fankasau ɗin zallarta ba tare da ta haɗa da miyar ba. Ban ƙara cewa da ita komai ba har izuwa lokacin da Umma ta fito daga cikin ɗaki, Amira ta gaishe ta ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa kafin ta juyo gare ni.
"Wai ina mutumin nan ya shiga ne?".
Cikin rashin fahimta na ce"Umma waye fa kenan?".
"Waye kuwa ban da wannan lalatacceb uban nakin. Ina magana kin wani tsare ni da ido shegiya tanbaÉ—aÉ—É—iyar yarinya wacce ba ta yi gadon abin azurki ba".
Kalamanta suka sanya jikina yin sanyi ƙalau har da na rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa, muryata a shaƙe na furta"tun safe da ya fita har yanzu bai shigo ba".
"Haba! Ke kuwa baiwar Allah ki dinga sasauta harshenki mana akan yarinyar nan. Wallahil azim bakin uwa guba ne ga Æ´aÆ´ansa wanda da yawan uwaye ba su san hakan ba".
Furucin ustazun gidan kenan wanda bai daÉ—e da kama hayar É—akin da yake kusa da na Naman Vector ba, daga shi sai matarsa amarya wanda a cewarta aure su wata huÉ—u kenan.
"To fa! Ɗankari manƙari har da su kaza acin ɗanko?. Wanene kake da suna?".
Ya yi hanzarin faÉ—in"Abdulwahab nake".
Umma ta gyara tsayiwarta kafin ta ci gaba da furzar da zantukan dake kan harshenta masu nauyin gaske, wanda kunnuwa ba za su yi mararin ƙara sauraran su ba ko da bisa kuskure ne kuwa.
"Zan ɗaga maka ƙafa ne kawai don kai baƙo ne a cikin gidan nan, amma wallahi bacin haka babu abin da zai dakatar da ni daga yaga maka rigar mutumci a tsakar gidan nan a gaban kowa. Don ni da kake gani na ɗin nan abun kunya gaba na ba shi ba baya ba. Ka jira tukunnan idan ka sama naka ɗiyar sai ka yi yadda kake so da ita amma ba yanzu ba, Amatullah ƴata ce babu wanda ya fi ni ƙarfin iko akan ta".
Cike da takaicin zantukan Umma, Ustaz ya jijjiga kansa tare da sadda kansa ƙasa.
"Allah ya kyauta, Allah ta yi mana mai kyau". Ya furta yayin da yake ficewa daga cikin gidan ba tare da ya É—ago kansa ba.
"To ku kuma munafukai masu kunnuwan son jin gulma da tsegumi, sai ko wacce ta ja jikinta ta bar nan". Umma ta yi zancen tana wurgawa Maman Adnan da Asabe da suke yi cirko-cirko a ƙofar ɗakunansu harara, kafin ta ja dogon tsaki ta shige ɗaki.
Ban san sa'ilin da ƙwalla suka soma tsere a bisa kuncina sai ɗuminsu na ji suna sauƙa a saman haɓarta, daidai lokacin da Amira ta dafo kafaɗuna tana doge mini hawayen da suka ɓata mini fuska. Ta ja hannuna zuwa ɗakin su a nan ta dinga lallashina da kalaman masu kwantar da hankali da haifar da nutsuwa a cikin rai da ruhi.
Wayarta ta soma ruri ta É—aga ta sanya a kunnenta, hankalina baya gare ta hakan ya sa ban ci abin da take faÉ—a ba har sai lokacin da na ji ta duga ihu gami da tashi tsaye ta daka tsalle. Na fita da kallo ba tare da na ce da ita ko kanzil ba har sai da ta gama wayar kafin ta kallo ni, fuskarta kamar gonar auguda bakinta har kunne ta soma cewa"albishirinki Amatullah".
"Goro".
"Fari ko ja?".
Na juya idanuna kafin na ce"fari ƙal kamar haƙwaranki".
"Yau Mansur zai dawo kuma ya yi min alƙawarin yana shigowa garin nan a ƙofar gidan nan zai tsaya. Saboda ya yi wa kansa alƙawarin da ni zai fara tozali da zaran ya dawo".
"Allah ya dawo da shi lafiya, Allah kuma ya bar ƙauna".
Cike da annuri ta furta"Amin na gode". Ta ƙare maganar tare da rungume ni. Mun ɗau lokaci muna tattaunawa har Ummanta ta gama toya waina ta zubo mana muka ci, na baro ta akan za ta shiga wanka. Na iske Umma har ta kammala dama kunnun na yi mata sannu da aiki ta yi banza da ni, sai da na jira Amira ta fita kana ni ma na shiga na yi wanka muka shirya muka fita muka yada zango a inda muke zama a tasha.
Kan ka ce kabo mutane sun yi mana rumfa sanyan waina da kunun ake yi babu ƙauƙautawa, tun daga nisa da na hango Bashir na fara haɗe fuskata ban bar wata ƙofar da zai iya yi mini kowacce iriyar maganar ba. Ya iso ya zauna suka gaisa da Amira suka ɗan taɓa hira ina jin su ban soma baki ba.
"Bari na kai wa Naziru masarsa kafin ta yi sanyi". Na tsikayo muryar Amira. Na bi ta da ido don na san da gayya ta yi maganar, na yi tsam na riga ta miƙewa ta kafe ni da ido alamar son ƙarin bayani.
"E mu je na raka ni, tun da muke tashar nan fa kin san babu inda na taɓa zuwa a cikinta".
"Kin san ke ma ai hakan ba zai yiyu ba. Kayan kuma a waye za mu bar wa". Na saurin tarar numfashinta" ba ga Bashir yana zaune a wajen ba, sai mu bar mi shi".
"Bashir kuma?".
"Ƙwarai kuwa, Bashir ko kana da wani uzurin ne?". Na yi zancen cikin sanyin murya mai cike da taushi gami da jawo hankali mai sauraro.
"Kin san ance ai sayon giwa ya take na raƙumi, ko ina da wani uzurin ai ya sama dole na zauna na jire muku kaya tun da Gimbiya da kanta ne ta buƙaci hakan". Ya yi zancen yana washe baki kamar wanda aka yi wa kyautar kujerar hajji da umra. Ta yi masa fari da ido kafin muka bar wajen tafiya ce mai ɗan nisa muka yi kafin muka iso bakin wasu shagona biyu.
"Ki jira ni anan bari na shiga na kai masa".
Na yi wuf na riƙo hannunta"Amira shiga za ki yi? Kamar ɗaki ne fa?".
"Ba ma kama ba ne É—auki ne, ke dai kawai ki jira ni yanzu zan fito". Ba ta jira abin da zan ce ba ta fizge hannunta ta shige ta bar ni tsaye a wajen ina kallon ikon Allah buwayi gagara misali.
Tun ina tsaye akan ƙafafuna har sai da suka gaji Amira ba ta fito ba, ɗakin da yake kusa da wanda Amira ta shiga aka buɗe ƙofar aka fito, wata mai tallan awara ne ta fito daga ɗaƙin riƙe da roban awaran a hannunta yayin da wani mutum yake bayanta daga shi sai singileti da gajeren wando.
Ya miƙo mata kuɗi yana faɗin"yau fa ba irin farashin kullum zan biya ba, don ba ki yi min yadda nake so ba don haka ga wannan ki je ki rage zafi". Ta yi masa wani mungun kallo kafin ta amsa kuɗin" kawo ai an ce raba arne da makami ibada ne". Ta kai aya tana kwafce kuɗin daga hannunsa.Ya ɗaga hannu zai maka duka ta yi hanzarin kaucewa.
"Matsalan ƴaƴan matsiyata kenan kana son su da azurki kuna ɓokarewa. Da ni kike zance yarinya". Ya yi zance a kufule yana yin ƙwafa.
Daidai sanda zai shige ɗakin muka haɗa ido da shi ya yi mini ɗagowa, da hakan ya sanya ni sauri rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa, kafin kakkauran muryarsa suka dira a ƙofofin kunnuwana.
"Ke dan ubaki me ye kike yi a nan? Kuma me ye kika tsaya kina kallo?".
Na ji maganar ƙarshen a kusa da ni na cira kaina na gan shi tsaye a gabana. Gaba ɗaya na ruɗe hakan ya sani gaza cewa komai. Har Amira ta fito ta same mu a haka.
"Amatullah me ye yake faruwa? Me ye ya haÉ—a ki da shi?".
"Babban yarinya daman kin san ta ne?".
"Ƙwarai kuwa tare muke da ita".
"Ke Amira ba na son rainin wayo fa, me ye hakan kuma? Yanzu wannan abun ne ya zama abin dariya a wajenki?. In ce dai da ke muka sha wuyar nemo wannan fankasau ɗin na yi tunanin ai za mu haɗu ne mu taya juna jimami da takaici, amma sai ki bige da dariya". Na ƙare zancen a kulefe don ba ƙaramin cusa mini takaici dariyar tatan ta yi ba.
"Ki yi haƙuri ƙawata, me ye laifin maganata fisabillillahi? Ai ni ina ga hakan ma abin alfahari ne gare ki da tunƙaro. Ko a gaban waye za ki tinƙaho ki bigi ƙirji domin mahaifiyarki sarauniya take a cikin a wajen mahaifinki kuma tana iya juya gidan kaman waina a bisa tanda".
Na bi ta d irin kallon da mai hankali yake yi wa zautacce kafin na furta"yanzu ke a irin tunaninki wannan abin wayewa ne?".
Ba tare da shakkan komai ba ta ce"ƙwarai kuwa, ai duk wacce kika ga mahaifiyarta ta isa da gidansu ta huta gaba da baya kuma ta wuce raini". Na jijjiga kaina tsabar takaicin da ya zarge muni wuya ya haifar nuni da wanzuwar ɗaci a cikin maƙoƙarona.
"Wani lokacin idan kina yin magana sai ki jefa ni cikin tunani, na yi ta hashashen anya kina amfani da ilmi da hankalinki kuwa wajen haɗa kalmomin da bakinki zai furta. Amira ina wayewa a cikin wannan lamarin? Yanzu fa in gaya miki gaskiya samari sun waye ko aure za su nema sai sun tabbatar da cewa uban yarinyar ya isa da gidansa, kuma yana da cikakken ikon zartar da ko wani irin hukunci ta yadda ko kara ya ajiye babu bai ƙetare shi".
"Wannan kuma ra'ayinki ne. Kin faɗi naki ni ma na faɗi nawa, don haka kowa sai ya riƙe na shi".
Tana ƙare zancen ta soma cin fankasau ɗin zallarta ba tare da ta haɗa da miyar ba. Ban ƙara cewa da ita komai ba har izuwa lokacin da Umma ta fito daga cikin ɗaki, Amira ta gaishe ta ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa kafin ta juyo gare ni.
"Wai ina mutumin nan ya shiga ne?".
Cikin rashin fahimta na ce"Umma waye fa kenan?".
"Waye kuwa ban da wannan lalatacceb uban nakin. Ina magana kin wani tsare ni da ido shegiya tanbaÉ—aÉ—É—iyar yarinya wacce ba ta yi gadon abin azurki ba".
Kalamanta suka sanya jikina yin sanyi ƙalau har da na rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa, muryata a shaƙe na furta"tun safe da ya fita har yanzu bai shigo ba".
"Haba! Ke kuwa baiwar Allah ki dinga sasauta harshenki mana akan yarinyar nan. Wallahil azim bakin uwa guba ne ga Æ´aÆ´ansa wanda da yawan uwaye ba su san hakan ba".
Furucin ustazun gidan kenan wanda bai daÉ—e da kama hayar É—akin da yake kusa da na Naman Vector ba, daga shi sai matarsa amarya wanda a cewarta aure su wata huÉ—u kenan.
"To fa! Ɗankari manƙari har da su kaza acin ɗanko?. Wanene kake da suna?".
Ya yi hanzarin faÉ—in"Abdulwahab nake".
Umma ta gyara tsayiwarta kafin ta ci gaba da furzar da zantukan dake kan harshenta masu nauyin gaske, wanda kunnuwa ba za su yi mararin ƙara sauraran su ba ko da bisa kuskure ne kuwa.
"Zan ɗaga maka ƙafa ne kawai don kai baƙo ne a cikin gidan nan, amma wallahi bacin haka babu abin da zai dakatar da ni daga yaga maka rigar mutumci a tsakar gidan nan a gaban kowa. Don ni da kake gani na ɗin nan abun kunya gaba na ba shi ba baya ba. Ka jira tukunnan idan ka sama naka ɗiyar sai ka yi yadda kake so da ita amma ba yanzu ba, Amatullah ƴata ce babu wanda ya fi ni ƙarfin iko akan ta".
Cike da takaicin zantukan Umma, Ustaz ya jijjiga kansa tare da sadda kansa ƙasa.
"Allah ya kyauta, Allah ta yi mana mai kyau". Ya furta yayin da yake ficewa daga cikin gidan ba tare da ya É—ago kansa ba.
"To ku kuma munafukai masu kunnuwan son jin gulma da tsegumi, sai ko wacce ta ja jikinta ta bar nan". Umma ta yi zancen tana wurgawa Maman Adnan da Asabe da suke yi cirko-cirko a ƙofar ɗakunansu harara, kafin ta ja dogon tsaki ta shige ɗaki.
Ban san sa'ilin da ƙwalla suka soma tsere a bisa kuncina sai ɗuminsu na ji suna sauƙa a saman haɓarta, daidai lokacin da Amira ta dafo kafaɗuna tana doge mini hawayen da suka ɓata mini fuska. Ta ja hannuna zuwa ɗakin su a nan ta dinga lallashina da kalaman masu kwantar da hankali da haifar da nutsuwa a cikin rai da ruhi.
Wayarta ta soma ruri ta É—aga ta sanya a kunnenta, hankalina baya gare ta hakan ya sa ban ci abin da take faÉ—a ba har sai lokacin da na ji ta duga ihu gami da tashi tsaye ta daka tsalle. Na fita da kallo ba tare da na ce da ita ko kanzil ba har sai da ta gama wayar kafin ta kallo ni, fuskarta kamar gonar auguda bakinta har kunne ta soma cewa"albishirinki Amatullah".
"Goro".
"Fari ko ja?".
Na juya idanuna kafin na ce"fari ƙal kamar haƙwaranki".
"Yau Mansur zai dawo kuma ya yi min alƙawarin yana shigowa garin nan a ƙofar gidan nan zai tsaya. Saboda ya yi wa kansa alƙawarin da ni zai fara tozali da zaran ya dawo".
"Allah ya dawo da shi lafiya, Allah kuma ya bar ƙauna".
Cike da annuri ta furta"Amin na gode". Ta ƙare maganar tare da rungume ni. Mun ɗau lokaci muna tattaunawa har Ummanta ta gama toya waina ta zubo mana muka ci, na baro ta akan za ta shiga wanka. Na iske Umma har ta kammala dama kunnun na yi mata sannu da aiki ta yi banza da ni, sai da na jira Amira ta fita kana ni ma na shiga na yi wanka muka shirya muka fita muka yada zango a inda muke zama a tasha.
Kan ka ce kabo mutane sun yi mana rumfa sanyan waina da kunun ake yi babu ƙauƙautawa, tun daga nisa da na hango Bashir na fara haɗe fuskata ban bar wata ƙofar da zai iya yi mini kowacce iriyar maganar ba. Ya iso ya zauna suka gaisa da Amira suka ɗan taɓa hira ina jin su ban soma baki ba.
"Bari na kai wa Naziru masarsa kafin ta yi sanyi". Na tsikayo muryar Amira. Na bi ta da ido don na san da gayya ta yi maganar, na yi tsam na riga ta miƙewa ta kafe ni da ido alamar son ƙarin bayani.
"E mu je na raka ni, tun da muke tashar nan fa kin san babu inda na taɓa zuwa a cikinta".
"Kin san ke ma ai hakan ba zai yiyu ba. Kayan kuma a waye za mu bar wa". Na saurin tarar numfashinta" ba ga Bashir yana zaune a wajen ba, sai mu bar mi shi".
"Bashir kuma?".
"Ƙwarai kuwa, Bashir ko kana da wani uzurin ne?". Na yi zancen cikin sanyin murya mai cike da taushi gami da jawo hankali mai sauraro.
"Kin san ance ai sayon giwa ya take na raƙumi, ko ina da wani uzurin ai ya sama dole na zauna na jire muku kaya tun da Gimbiya da kanta ne ta buƙaci hakan". Ya yi zancen yana washe baki kamar wanda aka yi wa kyautar kujerar hajji da umra. Ta yi masa fari da ido kafin muka bar wajen tafiya ce mai ɗan nisa muka yi kafin muka iso bakin wasu shagona biyu.
"Ki jira ni anan bari na shiga na kai masa".
Na yi wuf na riƙo hannunta"Amira shiga za ki yi? Kamar ɗaki ne fa?".
"Ba ma kama ba ne É—auki ne, ke dai kawai ki jira ni yanzu zan fito". Ba ta jira abin da zan ce ba ta fizge hannunta ta shige ta bar ni tsaye a wajen ina kallon ikon Allah buwayi gagara misali.
Tun ina tsaye akan ƙafafuna har sai da suka gaji Amira ba ta fito ba, ɗakin da yake kusa da wanda Amira ta shiga aka buɗe ƙofar aka fito, wata mai tallan awara ne ta fito daga ɗaƙin riƙe da roban awaran a hannunta yayin da wani mutum yake bayanta daga shi sai singileti da gajeren wando.
Ya miƙo mata kuɗi yana faɗin"yau fa ba irin farashin kullum zan biya ba, don ba ki yi min yadda nake so ba don haka ga wannan ki je ki rage zafi". Ta yi masa wani mungun kallo kafin ta amsa kuɗin" kawo ai an ce raba arne da makami ibada ne". Ta kai aya tana kwafce kuɗin daga hannunsa.Ya ɗaga hannu zai maka duka ta yi hanzarin kaucewa.
"Matsalan ƴaƴan matsiyata kenan kana son su da azurki kuna ɓokarewa. Da ni kike zance yarinya". Ya yi zance a kufule yana yin ƙwafa.
Daidai sanda zai shige ɗakin muka haɗa ido da shi ya yi mini ɗagowa, da hakan ya sanya ni sauri rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa, kafin kakkauran muryarsa suka dira a ƙofofin kunnuwana.
"Ke dan ubaki me ye kike yi a nan? Kuma me ye kika tsaya kina kallo?".
Na ji maganar ƙarshen a kusa da ni na cira kaina na gan shi tsaye a gabana. Gaba ɗaya na ruɗe hakan ya sani gaza cewa komai. Har Amira ta fito ta same mu a haka.
"Amatullah me ye yake faruwa? Me ye ya haÉ—a ki da shi?".
"Babban yarinya daman kin san ta ne?".
"Ƙwarai kuwa tare muke da ita".