← Book details Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 58

Sashe 45

Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dinner tayi kyau da dadi,bayan an tashi duk an watse gida,su Mama sun tafi da Aabid,Alim ya fito ya hango Amana zata shiga Mota shima zai shiga tasa ya murde mata kunne sosai ya,Amana haushi ya isheta ta sai kawai ta shareshi ta shiga Mota ta figa ta hau titi,Alim ma haka,

Gani tayi Alim zai wuce ta tayi masa Over taking tare da sauke glass tana masifeshi dan jagaliya baka iya tuki ba ka koma ka koyi mata,Alim ma ya leko ya kwalla da karfi idan na raina kasuwa ko sautun Cincin bazan yi ba,
Amana tace dan kauyeeeeee,Alim yace daga birni nazo nazo ai,wai yayiwa Amana gori,
Nafi karfinka dai ni na wayar da kai,
Alim yace ai kin iya daurin dankwali yanzu,Amana tace ance maka da can iyawa kayi? ,Alim yayi maganar yan daba yace kya nuna mana Zara,ai mune Zara yar nan,
Ni ba karamin tantirin dan iska bane,Amana ta kwallo itama da karfi tace ai kuwa nima ba karamar tantiriyar yar iska bace kai dukkan mu ba kananan tantirai bane,Maganar ta irin ta nigogi tayi Baaaaba kana yawa,Alim yace motar aroceee,Amana tace dan mafiya me kudin tsafiiiii motar da ka siya da kan dan jariri.

Suna karasowa cikin gidan kowa ya Parker tare da fitowa zata wuce part dinsu,Alim ya kama yatsanta ya lankwasosu baya ta kwalla kara ta kwala masa jakarta,tana haki tace azzalumin mutum ni ba wasa nake da kai ba
Tafiya Alim yayi ya kyaleta yace yarinyar nan da gaske take amma na kyaleta daga yau ya furta cikin fushi.

Amana kuwa ciki ta shiga tayi wanka ta canja kayan bacci ta kwanta gefen Sakina da Badriyya.
Badriyya ce ta Mike ta fara magana Anty Amana ina kika tsaya haka kin San har 2am yanzu fa,banza Amana ta mata,Badriyya tace dama tambayarki zanyi dan Allah first night da Zafi?Allah tsoro nakeji,
Amana tayi dariya tace sanda kika dinga zuga Alim kina hadamu daki ki kulle kin nemi shawarata?
Ki kyaleni naji da abinda ya dameni pls,
Juya baya Amana tayi ta fara tunanin Alim yanda zata daina kulashi ko yayi magana ta daina kulashi,ita zai rainawa hankali ya mata laifi ko yayi tunanin lallashinta saima wani hade mata fuska da yakeyi tare da gwada mata mungunta.

Washe gari bayan Anyi sallar Asuba rana ta fito kadan kowa ya koma baccin safe,12pm Amana ta tashi daga bacci wanka tayi ta shirya cikin doguwar Rigar material Golding color tayi kyau Sosai kamar a sace ta,Amare da kawaye duk sun dau wanka anci ansha,Amana bata ci komai ba ta wuce wajen Maman Huzaifa tare da gaisheta da sauran dangi,Aabid ne yazo tare da makaleta,cike da kunya Amana tace Mama abinci nazo nema,Mama tace ke duk kowa yaci yasha sai yanzu kika fito ana jira a kawo lunch duk an wanke komai tare da gyarawa,shiga kitchen ki hadawa kanki,
Kitchen ta shiga ta dafo indomie da kwanta ta dawo Palo kusa da Mama zata fara ci Alim ya fito cikin 3qtr da Riga T-shirt yana kamshi,Mama tace girman lagos aikinka kenan yawo cikin Mata kaine nan kaine can ga shigar arna, Amana sau daya ta kalleshi ta dauke kanta gefe,
Matsowa yayi tare da gaisar da Mama kana ya kurawa Amana Ido tana cin Indomie Aabid yana gaida Alim ya zura da gudu ya bar wajen ya hango yara na wasa,
Alim kuma ya tsuguna ya dauke plate din Amana yayi tafiyarsa da abincin,Mama ta saki baki tace Alim zan bata maka wlh dawo mata da abincinta,Alim yace Mama yunwa nakeji fa,to ita kuma fa?Sai ta dafa wata Mama tace sai dai ka dawo kuci tare sai ta kara dafa muku wata Ku kara,
Amana tace ni na koshi kyaleshi,a'a baki isa ba cewar Mama spoon biyu kikayi fa, Mama ni bazan ci dashi ba Kazami ne fa Amana ta fada da azababbiyar shagwaba wacce tayi sanadin zukewar numfashin Alim, ajiye Alim kuci cewar Mama, cikin yan uwa duk suna palon,Alim ya jawo sallaya ya zauna yana masifa yacewa Amana sai ki sakko kasa ai kamar wasu yara, Amana gudun kar tayiwa Mama musu ga dangi za a gane basa shiri kawai ta sakko kasa ta zauna Mama harda mika mata pillow ta zauna tana hade rai,
Mama tace Asiya ta je ta dafa musu wata kafin su cinye wannan,
Asiya taso a kyaleta itama taga fadan su Alim amma haka ta wuce kitchen,

Fork spoon dayane Alim ya fisge a hannun Amana ya dinga cin indomie da sauri da sauri wai dan yafi ci da yawa Amana ta rasa ,Amana ta finciko cokalin a bakinsa yasa hakuri ya rike spoon din gam, da kyar ta zaro cokalin itama tai ta ci da yawa ya kwace cokalin tare da tattaro indomie gabansa,yana ta ci,Amana tace Mama kinga zai cinye du,Mama tace wai kai wanne irin mugu ne?bata spoon dinta taci,Amana ta warce itama ta sharba,Alim yace Mama kalli kazantar da takeyi wlh zata lalata abincin,Mama tace to kema baki dai dai ba bashi cokali yaci,Alim ya kwace yaci da yawa Mama tace kaima kayi zari ka bar mata plate din sai an kawo wata Alim yace haba Mama ko romon ni fa ban sha ba,Wata a cikin dangi tace to kai kaci girma mana akan Indomie kamar mayunta ku bari a kawo wata mana wlh Mama ke kike kulasu,ji nake jiya suka gama iskancin ture ture da yakushe yakushe,
Amana tace Allah ni bana kulashi shine yake takalata,cokalin ya dan buga mata a goshi,Mama tace ah...kema da halinki duk halinku daya,ni ban san Alim da haka ba sai yanzu,

Asiya ce ta kawo musu lafiyyar Indomie tare da mikawa Alim cokalinsa daban,
Nan kowa ya fara ci sai gwaren cokali sukeyi a plate,ka daina cimin gabana,cikin rada Alim yace tab wannan maganar tafi karfina kin jin nace ina nema zan....Amana tayi shuru har ya fassara mata magana. Suna ci gaba da ci Sai ta ebo yasa cokali ya kwace,Amana ganin mutane yasa ta kyaleshi,da yaga taki kulashi kuma so yake ya sata bakin ciki sai,ji tayi kawai ya turo plate din jikinta Indomie ta zubo mata a gefenn cinya ta bata mata kaya Amana kwalla tab a idonta tace Mama kin ganshi ko wlh kar na rama aga banyi dai dai ba,na gaji da halinsa sai yana dukana yanzu ma kina kallon can ya mareni kaji Amana da karya, wata dattijuwa tace abin naku iskanci ne kawai ,Mama tace kai ku rabu dani na gaji da halinku,Amana tace Mama shine fa yake ta min abu,jiya ma haka ya dinga dukana,har marina yayi a wajen dinner da zamu dawo,Wata a cikin yan biki tace wai ba mata da miji bane? akace mata da miji ne,matar tace iya shegen banza da ya kuke zama a gidan auren? Wannan ai sai kusa mutum hawan jini,

Mama tace Alim ka kiyayeni na fada maka,Kanwar Abban su Alim ce tazo tace Mama yaranan ina kallon gangancin da sukeyi da Mota a titi zasu je dinner suna ta fada ta windon Mota,mutane suka saki Salati,kunya Amana taji ta mike ta bar palon,Alim ma haka,mutanen wajen suka ce wannan matar tasa yar nema ce naga a tsaye take itama,amma Alim da miskili ne ta koya masa sun zama daya,wasu sukace wannan Yara da kuruciya suke abin dariya,fadan nasu duk ba fada bane.

Amana suna waje a zaune da mata da Maza kawaye da angwaye ana ta hira,Alim shi da wani frnd dinsa suka zo wajen kusa da Amana Alim ya zauna cikin hira Alim yace ai shi yasa akace mata duk sunfi yawa a wuta,Amana tana ji tasan da ita yake zaraf cikin dagewa da masifa tace ai wlh wannan karan sai dai ayi kunnen doki Maza rabi mata rabi,Mazan gasu nan duk azzalumai,

Alim a fusace yace kinji nayi magana dake zancen mu mukeyi zaki sa min baki,Amana ta shareshi,Alim ya kara cewa ai idan mace ta isheka to ka karo aure,Amana tace wace zata zauna da kai da baka san komai yanda duniya take ciki ba,duk mutane wajen shuru sukayi ana jin fadan su Alim,Alim yace dadin abin dai Aljannarku na kasan kafafunmu,Amana tace idan mun zo shiga ku take,ke da ke nake wai? Alim ya mike tare da Barin wajen yana masifa

9pm aka fara shirye shiryen tafiya dinner,Hamza ma duk sunzo kuma sun karbi motar hannun Amana suna kai kawaye,Amana data shirya ta fito cikin shiga ta gaske,ba kowa a tsakar gida duk an gama tafiya sai kakar su Alim kawai ta fito zasu tafi da Alim tana ta tsokanar Amana,Alim ya fito fes cikin rantsatsiyar shiga,kaka taja Amana wai dole su tafi tare,Amana taki yarda Amma kaka ta matsa mata,dole ta bude gidan baya a motar Alim ta shi ga ba walwala,Alim ma fuska ba rahma,ya zauna gefen kaka,Asiya ta fito ta shige gaban Mota,
Bai ce komai ba driver yaja Mota kamar abin arziki sun danyi nisa da tafiya, Alim da Amana sunsa Kaka a gefe karshen mota Amana a tsakiya Alim a gefenta

Alim ya leko da kansa ya kurawa Amana ido,dagowa tayi suka hada ido aí kuwa ya mata gwalo itama ta rama,
Bayan minti daya yace Anjima idan mun dawo zamuyi magana ta fahimta yayi zancen ne ba wasa da gaske,Amana tabe baki tayi tana so tace bata da lokacinsa Amma kuma Kaka na wajen da Asiya,kawai sai tace ba time,
Pls kinji?tayi banza dashi kamar bata ji ba,yace am talking to u fa,tayi banza dashi,
Nan ya zuro hannu tare da latsa cikinta ina abina?

Amana ta kwadawa Alim duka a hannun,Kaka tace yau naga fitsararre,Dariya Alim yayi ya Mika hannu again Kaka ta bige hannun,Amana ya kara rukowa hannu pls ki bani time,Amana ta rike hannun Alim ta garza masa cizo sai suka fara kokawa da hannaye, Kaka na kallonsu suna ta yakushe ya kushe,Alim ya kara tafkawa Amana mintsini,tana haki da Hawaye tare da cewa ka mintsinen?
Chapter 45 · 0% Book details