Sashe 38
Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da gani har yanzu yana sonki sai yanzu muka gane dalilin da yake barka kuka,
Zamu tayaki da addua Allah ya bayyana gaskiya,Haladu yace Insha'allah zai dawo da kansa wajenki ki raini cikinki Allah raba lfy,Umma tace shi yasa kike ta kuka haka,gwaggo tace Allah ya shige gaba,sauran matan sukace Ameen,Amana sai hawayene ke sintiri a fuskarta,ana ta mata Nasiha,Badriyya tace wlh ko Saude ko Mum ne zasu kala miki wannan sharri na sani Allah zai saka miki.
Alim kuwa kwana yakeyi ba barci saboda tunanin Amanarsa tsananin sonta,da abinda kuma ya gani wai kwarto fasiki Amana taci Amanarsa,shima yayi kuka yayi bakin ciki yana wani Hali ya rasa inda zaisa kansa,shike nan cikin zazzabi,baya cin abinci,duk ya rame sosai,kamar yau yana kwance a gidansa domin tunda ya dawo gida bai taba ko kwana a gidansu wajen Mum ba,yauma kwance yake zaman bed zazzabi ya rufeshi a hankali ya furta I missed u me yasa zaki zalunceni,bayan ina sonki zaki ha'inceni?why Amana.haka yayi ta sambatu,
Mum tayi farin cikin ganin Alim dinta gashi ya dawo shi kadai ba tare da tsinanniya Amana ba. cewar Mum
Abba da su Nura sun tambayi Alim ina matarsa sai yace ya dan barta a gidansu ta huta Sabo da rasuwar Babansu zai dinga zuwa can yana da gida a garin nasu a ciki ya sata.
Aabid kuwa yana gidan Nura sunyiwa Mum wayo sun daukeshi.
Amana ta gargadi Badriyya kar ta fadawa Huzaifa komai tsakaninta da mijinta.
Kwana biyu laulayi Amana ta fara sosai zazzabi,kwadayi ga yawan sha'awa da takeji kuma sha'awa r Alim kadai take ji,s ai ciye ciye kullum na kwadayi yan uwanta Maza da mata su suke kula da ita sosai,kafin tace tana son abu sunyi mata,sai abinda take so suke kawo mata,kowa lallabata yakeyi dan hankalinta ya kwanta,ta rame sosai sai fari data kara kwal kwal da ita,
Yanzu bata da matsalar komai sai ta rashin Alim,sha'awarsa,sai nauyin da Abba ya dora mata har yau bata sauke ko daya ba,
Sati Uku da rasuwar Baba sai kuma wata sabuwa Umman Amanace ta bijiro da wata tsiya rigima sabuwa fil ta baro.
AsmaBaffa
Readers a dinga Afwa idan anga mistake,ba lallai Allah ya hada komai abinda kake so ba,idan kunga abinda bai muku ba kuyi hakuri story a haka yazo,kuma ku dinga nutsuwa a ko wanne acting da akayi a wannan novel ko wanne page akwai sakon dayake isarwa a dinga gane abinda ake rubutawa ana masa kyakyawar fahimta ta gaske.na gode kwarai
✳CIRANIN AMANA✳
155-160
Official
By
AsmaBaffa
ANTY SUMEE INA GAISUWA WANNAN PAGE NAKINE.MARAICIN SO FANS INA GODIYA KWARAI.
Umman Amana ta tsiro da wata tsiya Inda kwata kwata take ta jin haushin Amana saboda taga yanzu bata da kudi,bata Auren me kudi komai sai dai su Hamza suyi mata,yan kudin da take dasu duk ta karar dasu a gidan tana yo musu cefane idan mazan basa gida gashi ta biya sauran yara kudin makaranta,gashi mutane da yawa sunzo wai suna bin Sulemanu Harka kudi kafin ya mutu ya ranta,sabo da haka kudin bashin da ake bin Mamaci dubu dari tara akayi lissafi,
Gashi sauran mazan gaba daya sana'arsu batayi karfi ba ga kula da gida,
Gashi wanda sukayi aure ma ko wacce rurowa sukeyi a gidan ake tallafa musu,ga yara masu tasowa cincirundo,shawara suka hadu iya manyan gidan babu kudin da za a biya Bashin mamaci kuma ya zama dole,Amanace ta bada takaddun gidan da suka zauna da Alim aka siyar dashi aka biya bashi,
Sauran canji akayi bukatun gida,bayan kwana biyar wani yazo yace shima yana bin bashin dubu dari biyu Amana ta bada sarkar Gold dinta har guda Hudu da Alim ya siya mata nan ma aka siyar aka biya,bayan sati biyu wasu suka kara zuwa wannan yace dubu hamsin,wani ashirin wani talatin,haka mutane suka dinga zuwa su Hamza suka nemo sukayi karo karo aka gama biyan bashin Baba kaf,kowa na gidan a gida tattalin arzikinsa yayi kasa basu da wani karfi,gwara ma su Hamza ba laifi,dole suka jinginar da maganar aurensu.
Kullum Umman Amana haushin Amana takeji wai ta kwashe kudinta ta biya bashin Baba ita kadai arzikinta duk ya kare ita bata bata ko kwandala ba,kuma Amana yanzu da su Hamza take shawara har meeting sukeyi,
Amana ga halin da take ciki ga kuma Umma kullum cikin hantararta da zaginta takeyi tana jifanta da muggan kalamai,idan readers baku manta ba Umman Amana ko koko safe a da bata bawa Amana sai dai ta siya,ganin Amana Allah ya buda mata ta samu kudi tana auren me kudi shine Umma ta sakko take kula da Amana,yanzu Amana Babu ba mutunci,dama ita Umma me bata shine nata,idan kana bata to a cikin yayanta kiri kiri zata dinga nuna banbanci.
Yauma gaba daya family na mirgayi Sulemanu sun Hallara a babban palo ana shawara,banda iyaye a meeting din,
Amana zaune take a tsakiyar Palo ta darararrashe ta sangale kafafu zaman masu ciki sosai ta rame idan kunga Amana za ku sha mamaki ta rame sosai,kana ganinta sai ka tausaya mata Sabo da Amana kullum sai tayi Kukan rashin Alim tayi addua tayi ba dare ba rana,
Da addua aka bude taro Hamza yace da Amana sayyada a cika mana da addua kinfi kowa Ilmi,ai kuwa akayi addua sannan aka kawo littafin wasiyyar Baba daya bari na gadon kowa gwara a bawa kowa hakkinsa dama Umman Amanace tace wlh sai an dakko an raba gado domin duk anyi tunanin Sulemanu ya tara dukiya ne a boye shi yasa har yayi littafi guda ya raba gardamar gado,
Page din farko na littafin aka bude ga abinda aka gani da Babban baki ya sa wani abokinsa ya rubuta masa domin Harka baiyi boko ba Badriyya ce me karantawa.ga abinda ke rubuce.
AMANATA INA KAUNARKI,Amana na jin an karanta haka ta fashe da Kukan tuna Baba,NI SULEMANU HARKA BABAN AMANA NA BAWA A CIKIN DUKIYATA DA ALLAH YA MALLAKA MIN NA BAWA AMANA SANIYATA WACCE NAKE KIWATAWA A GIDAN ABOKINA ME GARI,SANIYAR BATA HAIHUWA ITA KADAI CE ABINDA NAFI SO A CIKIN DUKIYATA,SABO DA HAKA SANIYA TA AMANACE KAR TA SIYAR DA ITA TA YANKA TA IDAN ALLAH YA BATA HAIHUWA TA DAGARGAJI DADINTA.dariya kowa yayi harda Amana me kuka,
Page 2. HAMZA NA BAKA TINKIYATA DA RAGO KA YANKAWA AMARYARKA RANAR BABBAR SALLAH ASHA DABGE,hhhhhh nan ma aka dau shewa da tafi tare da cewa Allah yaji kan Baba.
Page 3. KABIRU KB DAMIN GERO SHIDDA KA SIYAR KA KASHE KUDIN,
ISA KUMA WAYATA TA CELLULA DA AMANA TA SAI MIN,
HALADU KUWA BUHUM MASARA BIYAR,
BADRIYYA TOLO TOLO GUDA UKU,
SAKINA BARGONSA NA BACCI DA RADIO DA YAKE JIN LABARAI,DUK SUNA GIDAN ABOKINA ME GARI IDAN BAI BAKU BA KU SHIGAR DA KARA.
MATAN AURE KUWA KO WACCE A BATA RIGARSA DA WANDONSA DAYA DAYA,
SAURAN YARAN GIDAN KUWA KAI KUNCI UWAKU GABA DAYA GA SU AMANA NAN DUK ZASU KULA DAKU KAR KUCE BAN BAKU KOMAI BA CIKIN KAYAN SAWATA KUMA A RABA MUKU DAYA DAYA KOMA ME ZAKUYI DASU KUYI.
second to the last page kuwa na matansa ne,
KO WACCE CIKIN MATANA NA BATA KYAUTAR IYA DAKIN DA TAKE CIKI TA ZAUNA HAR IYA RAYUWARTA,SAURAN GIDAN KUMA KAR WANDA YA SIYAR GABA DAYA NA YAYA NANE,WACCE TAGA ZATAYI AURE TO BA BATUN SIYAR DA DAKI DOLE SAI DAI CIKIN YAYAN WATA KO WANI YA SIYA
LAST PAGE KUWA FATAN ALKHAIRI DA ADDUA YA ZAZZAGAWA IYALINSA,
Gaba dayansu sai da sukayi hawaye na tunowa da Baba,Umman Amana kuwa wani uban tsaki taja tare da cewa aikin banza akan wannan ya bata lokacin to wlh ni yola state zan koma cikin city wajen yan uwana su rikeni mahaifina,duk kun hanani ci gaba a garin nan.
Dan haka wanda yaga yana da kudin siyen dakina ya siya ya bani ko na kira wani a waje bare ya siya,
Amana hawaye da takaici ya isheta,tace Umma zan siya,Umma saida tayiwa Amana kallon banza sannan taja tsaki tace naji dumus,Kb Amana ta kira gefe tace kb ku samu a siyi dakin nan banda kudi hanuna kun san komai dai,kb yace akwai ragowar kudin gidan ki a hannuna ina ga zai siyi gidan,
Amana ta dawo cike da Ladabi tace Umma nawa kudin dakin? Umma tace sannu azagwai uwar Iya, wa ya sani ko da gaskene abinda kika aikata nasan ubanki kika gada shi kwarto ke kuma fa
?ai dole ayi gadon tsiya,wannan mijin naki yaron kirki Amana amma sai da kika nuna hali ya sako ki gaki ga gidan nan ai ki zauna,
Muna zaman lfy yaro na mana kyauta kika watsa kanki ya sakoki ga ciki dan Allah baki ji kunya ba?
To ko kin sayi dakina dan ubanki dole ki bini mu tafi yola na dinga dora miki talla,mene amfaninki wai ku masu Uba ko?
Amana dai bala'in da take ciki kadai ya isheta ta saba da hali Ummansu tunda yanzu bata da kudi,
Shi yasa Amana kamar ba ita ba duk tayi laushi tubus ta gama karaya da lamarin duniya,cike da ladabi tace to Umma amma Baba yace in ba aure ba kar mu rabu da yan Uwa, da karfi Umma tace iyyeeeeeee to wlh sai kin bini,sana'a za muyi mene amfaninki,
Nan Umma tayi kudin daki Amana ta siya sannan Umma tace dauko kaya mu tafi,kowa dake gidan yaji ba Dadi,nan Mutuwar Baba ta dawo musu sabuwa kowa kuka,
Musamman Badriyya da suka shaku da Amana ga bikin Badriyya da Huzaifa ya kusa,domin Huzaifa ma har tallafi yake kawo musu idan yazo sai Badriyya tace suna tare da Alim a lagos ita kuma Amana ta boye kanta,Sakina da Badriyya rana daya za ayi bikinsu saboda mazajensu masu hali ne sunce sun dauki nauyin komai na biki.
Amana bata so bin Uwarta ba amma gudun bijirewa iyaye dan kar ta maimaita yanda ta bijirewa Baba ta bar gidan da ita da Alim duk da cewa iyayen sune masu laifin amma duk da haka saida masifa ta afka musu shi yasa taji tsoron bijirewa Ummanta
Duk yan gidan ne suka taushi Amana suna ta kwantar mata da hankali,Badriyya da Haladu harda kuka yanda Amana ta fita daga hayyacinta gaba daya,
Zamu tayaki da addua Allah ya bayyana gaskiya,Haladu yace Insha'allah zai dawo da kansa wajenki ki raini cikinki Allah raba lfy,Umma tace shi yasa kike ta kuka haka,gwaggo tace Allah ya shige gaba,sauran matan sukace Ameen,Amana sai hawayene ke sintiri a fuskarta,ana ta mata Nasiha,Badriyya tace wlh ko Saude ko Mum ne zasu kala miki wannan sharri na sani Allah zai saka miki.
Alim kuwa kwana yakeyi ba barci saboda tunanin Amanarsa tsananin sonta,da abinda kuma ya gani wai kwarto fasiki Amana taci Amanarsa,shima yayi kuka yayi bakin ciki yana wani Hali ya rasa inda zaisa kansa,shike nan cikin zazzabi,baya cin abinci,duk ya rame sosai,kamar yau yana kwance a gidansa domin tunda ya dawo gida bai taba ko kwana a gidansu wajen Mum ba,yauma kwance yake zaman bed zazzabi ya rufeshi a hankali ya furta I missed u me yasa zaki zalunceni,bayan ina sonki zaki ha'inceni?why Amana.haka yayi ta sambatu,
Mum tayi farin cikin ganin Alim dinta gashi ya dawo shi kadai ba tare da tsinanniya Amana ba. cewar Mum
Abba da su Nura sun tambayi Alim ina matarsa sai yace ya dan barta a gidansu ta huta Sabo da rasuwar Babansu zai dinga zuwa can yana da gida a garin nasu a ciki ya sata.
Aabid kuwa yana gidan Nura sunyiwa Mum wayo sun daukeshi.
Amana ta gargadi Badriyya kar ta fadawa Huzaifa komai tsakaninta da mijinta.
Kwana biyu laulayi Amana ta fara sosai zazzabi,kwadayi ga yawan sha'awa da takeji kuma sha'awa r Alim kadai take ji,s ai ciye ciye kullum na kwadayi yan uwanta Maza da mata su suke kula da ita sosai,kafin tace tana son abu sunyi mata,sai abinda take so suke kawo mata,kowa lallabata yakeyi dan hankalinta ya kwanta,ta rame sosai sai fari data kara kwal kwal da ita,
Yanzu bata da matsalar komai sai ta rashin Alim,sha'awarsa,sai nauyin da Abba ya dora mata har yau bata sauke ko daya ba,
Sati Uku da rasuwar Baba sai kuma wata sabuwa Umman Amanace ta bijiro da wata tsiya rigima sabuwa fil ta baro.
AsmaBaffa
Readers a dinga Afwa idan anga mistake,ba lallai Allah ya hada komai abinda kake so ba,idan kunga abinda bai muku ba kuyi hakuri story a haka yazo,kuma ku dinga nutsuwa a ko wanne acting da akayi a wannan novel ko wanne page akwai sakon dayake isarwa a dinga gane abinda ake rubutawa ana masa kyakyawar fahimta ta gaske.na gode kwarai
✳CIRANIN AMANA✳
155-160
Official
By
AsmaBaffa
ANTY SUMEE INA GAISUWA WANNAN PAGE NAKINE.MARAICIN SO FANS INA GODIYA KWARAI.
Umman Amana ta tsiro da wata tsiya Inda kwata kwata take ta jin haushin Amana saboda taga yanzu bata da kudi,bata Auren me kudi komai sai dai su Hamza suyi mata,yan kudin da take dasu duk ta karar dasu a gidan tana yo musu cefane idan mazan basa gida gashi ta biya sauran yara kudin makaranta,gashi mutane da yawa sunzo wai suna bin Sulemanu Harka kudi kafin ya mutu ya ranta,sabo da haka kudin bashin da ake bin Mamaci dubu dari tara akayi lissafi,
Gashi sauran mazan gaba daya sana'arsu batayi karfi ba ga kula da gida,
Gashi wanda sukayi aure ma ko wacce rurowa sukeyi a gidan ake tallafa musu,ga yara masu tasowa cincirundo,shawara suka hadu iya manyan gidan babu kudin da za a biya Bashin mamaci kuma ya zama dole,Amanace ta bada takaddun gidan da suka zauna da Alim aka siyar dashi aka biya bashi,
Sauran canji akayi bukatun gida,bayan kwana biyar wani yazo yace shima yana bin bashin dubu dari biyu Amana ta bada sarkar Gold dinta har guda Hudu da Alim ya siya mata nan ma aka siyar aka biya,bayan sati biyu wasu suka kara zuwa wannan yace dubu hamsin,wani ashirin wani talatin,haka mutane suka dinga zuwa su Hamza suka nemo sukayi karo karo aka gama biyan bashin Baba kaf,kowa na gidan a gida tattalin arzikinsa yayi kasa basu da wani karfi,gwara ma su Hamza ba laifi,dole suka jinginar da maganar aurensu.
Kullum Umman Amana haushin Amana takeji wai ta kwashe kudinta ta biya bashin Baba ita kadai arzikinta duk ya kare ita bata bata ko kwandala ba,kuma Amana yanzu da su Hamza take shawara har meeting sukeyi,
Amana ga halin da take ciki ga kuma Umma kullum cikin hantararta da zaginta takeyi tana jifanta da muggan kalamai,idan readers baku manta ba Umman Amana ko koko safe a da bata bawa Amana sai dai ta siya,ganin Amana Allah ya buda mata ta samu kudi tana auren me kudi shine Umma ta sakko take kula da Amana,yanzu Amana Babu ba mutunci,dama ita Umma me bata shine nata,idan kana bata to a cikin yayanta kiri kiri zata dinga nuna banbanci.
Yauma gaba daya family na mirgayi Sulemanu sun Hallara a babban palo ana shawara,banda iyaye a meeting din,
Amana zaune take a tsakiyar Palo ta darararrashe ta sangale kafafu zaman masu ciki sosai ta rame idan kunga Amana za ku sha mamaki ta rame sosai,kana ganinta sai ka tausaya mata Sabo da Amana kullum sai tayi Kukan rashin Alim tayi addua tayi ba dare ba rana,
Da addua aka bude taro Hamza yace da Amana sayyada a cika mana da addua kinfi kowa Ilmi,ai kuwa akayi addua sannan aka kawo littafin wasiyyar Baba daya bari na gadon kowa gwara a bawa kowa hakkinsa dama Umman Amanace tace wlh sai an dakko an raba gado domin duk anyi tunanin Sulemanu ya tara dukiya ne a boye shi yasa har yayi littafi guda ya raba gardamar gado,
Page din farko na littafin aka bude ga abinda aka gani da Babban baki ya sa wani abokinsa ya rubuta masa domin Harka baiyi boko ba Badriyya ce me karantawa.ga abinda ke rubuce.
AMANATA INA KAUNARKI,Amana na jin an karanta haka ta fashe da Kukan tuna Baba,NI SULEMANU HARKA BABAN AMANA NA BAWA A CIKIN DUKIYATA DA ALLAH YA MALLAKA MIN NA BAWA AMANA SANIYATA WACCE NAKE KIWATAWA A GIDAN ABOKINA ME GARI,SANIYAR BATA HAIHUWA ITA KADAI CE ABINDA NAFI SO A CIKIN DUKIYATA,SABO DA HAKA SANIYA TA AMANACE KAR TA SIYAR DA ITA TA YANKA TA IDAN ALLAH YA BATA HAIHUWA TA DAGARGAJI DADINTA.dariya kowa yayi harda Amana me kuka,
Page 2. HAMZA NA BAKA TINKIYATA DA RAGO KA YANKAWA AMARYARKA RANAR BABBAR SALLAH ASHA DABGE,hhhhhh nan ma aka dau shewa da tafi tare da cewa Allah yaji kan Baba.
Page 3. KABIRU KB DAMIN GERO SHIDDA KA SIYAR KA KASHE KUDIN,
ISA KUMA WAYATA TA CELLULA DA AMANA TA SAI MIN,
HALADU KUWA BUHUM MASARA BIYAR,
BADRIYYA TOLO TOLO GUDA UKU,
SAKINA BARGONSA NA BACCI DA RADIO DA YAKE JIN LABARAI,DUK SUNA GIDAN ABOKINA ME GARI IDAN BAI BAKU BA KU SHIGAR DA KARA.
MATAN AURE KUWA KO WACCE A BATA RIGARSA DA WANDONSA DAYA DAYA,
SAURAN YARAN GIDAN KUWA KAI KUNCI UWAKU GABA DAYA GA SU AMANA NAN DUK ZASU KULA DAKU KAR KUCE BAN BAKU KOMAI BA CIKIN KAYAN SAWATA KUMA A RABA MUKU DAYA DAYA KOMA ME ZAKUYI DASU KUYI.
second to the last page kuwa na matansa ne,
KO WACCE CIKIN MATANA NA BATA KYAUTAR IYA DAKIN DA TAKE CIKI TA ZAUNA HAR IYA RAYUWARTA,SAURAN GIDAN KUMA KAR WANDA YA SIYAR GABA DAYA NA YAYA NANE,WACCE TAGA ZATAYI AURE TO BA BATUN SIYAR DA DAKI DOLE SAI DAI CIKIN YAYAN WATA KO WANI YA SIYA
LAST PAGE KUWA FATAN ALKHAIRI DA ADDUA YA ZAZZAGAWA IYALINSA,
Gaba dayansu sai da sukayi hawaye na tunowa da Baba,Umman Amana kuwa wani uban tsaki taja tare da cewa aikin banza akan wannan ya bata lokacin to wlh ni yola state zan koma cikin city wajen yan uwana su rikeni mahaifina,duk kun hanani ci gaba a garin nan.
Dan haka wanda yaga yana da kudin siyen dakina ya siya ya bani ko na kira wani a waje bare ya siya,
Amana hawaye da takaici ya isheta,tace Umma zan siya,Umma saida tayiwa Amana kallon banza sannan taja tsaki tace naji dumus,Kb Amana ta kira gefe tace kb ku samu a siyi dakin nan banda kudi hanuna kun san komai dai,kb yace akwai ragowar kudin gidan ki a hannuna ina ga zai siyi gidan,
Amana ta dawo cike da Ladabi tace Umma nawa kudin dakin? Umma tace sannu azagwai uwar Iya, wa ya sani ko da gaskene abinda kika aikata nasan ubanki kika gada shi kwarto ke kuma fa
?ai dole ayi gadon tsiya,wannan mijin naki yaron kirki Amana amma sai da kika nuna hali ya sako ki gaki ga gidan nan ai ki zauna,
Muna zaman lfy yaro na mana kyauta kika watsa kanki ya sakoki ga ciki dan Allah baki ji kunya ba?
To ko kin sayi dakina dan ubanki dole ki bini mu tafi yola na dinga dora miki talla,mene amfaninki wai ku masu Uba ko?
Amana dai bala'in da take ciki kadai ya isheta ta saba da hali Ummansu tunda yanzu bata da kudi,
Shi yasa Amana kamar ba ita ba duk tayi laushi tubus ta gama karaya da lamarin duniya,cike da ladabi tace to Umma amma Baba yace in ba aure ba kar mu rabu da yan Uwa, da karfi Umma tace iyyeeeeeee to wlh sai kin bini,sana'a za muyi mene amfaninki,
Nan Umma tayi kudin daki Amana ta siya sannan Umma tace dauko kaya mu tafi,kowa dake gidan yaji ba Dadi,nan Mutuwar Baba ta dawo musu sabuwa kowa kuka,
Musamman Badriyya da suka shaku da Amana ga bikin Badriyya da Huzaifa ya kusa,domin Huzaifa ma har tallafi yake kawo musu idan yazo sai Badriyya tace suna tare da Alim a lagos ita kuma Amana ta boye kanta,Sakina da Badriyya rana daya za ayi bikinsu saboda mazajensu masu hali ne sunce sun dauki nauyin komai na biki.
Amana bata so bin Uwarta ba amma gudun bijirewa iyaye dan kar ta maimaita yanda ta bijirewa Baba ta bar gidan da ita da Alim duk da cewa iyayen sune masu laifin amma duk da haka saida masifa ta afka musu shi yasa taji tsoron bijirewa Ummanta
Duk yan gidan ne suka taushi Amana suna ta kwantar mata da hankali,Badriyya da Haladu harda kuka yanda Amana ta fita daga hayyacinta gaba daya,