Sashe 39
Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka tana ji tana gani tare da sharbar kuka ta hada kayanta tas tabi Ummanta,amma abin mamaki Umma ta bar kannen Amana wajen su gwaggo wai su rikesu Amana tallafa mata za tayi da talla.
Tun a tasha,Amana kuka kawai take shike nan an kara nesantata da Alim,kuka kamar ta kashe kanta,Umma tace kiyi kukan jini ma ke kika jawa kanki,
A mota ma kuka takeyi ana ta kallonsu,to Amana ko wa zai taimaka miki oho.yanzu ba kudi basu Hamza ba Alim baki da kowa sai Allah.
Yanda Amana take wannan halin haka Alim ya shiga sanadiyyar rashin Amana kusa dashi ya yarda itace rayuwarsa,shima ya rame sosai da kyar yake fita ma,yan uwansa da iyayensa sun rasa gane kansa,yayin da Mum ta Nemo masa wata yar kawarta Zainab wai Abba yayi masa aure ko zai samu nutsuwa,Abba kuwa ganin halin da Alim ke ciki sai ya yarda,
Har zance Mum tace sai yaje wlh,Alim yana zuwa yaga Zainab wata tambadaddiya marar tarbiyya nan take yaci mutuncinta tun daga sama har kasa yayi tafiyarsa,wannan dalilin yasa aka dage biki sai nan da 6mnths,
Saude kuwa ana can Ana Wainar siyarwa tare da ci gaba da kulle kullen tsiya.
Ranar da Amana tabi Umma suka tafi ranar da yamma Alim yazo gidan shi da Huzaifa,dalili kuwa ranar kawai yaji ba abinda yake so ya gani a duniya irin Amana,
Waya yayiwa Huzaifa wai yana so ya gaisar da iyayen Amana mata yayi musu alherin saboda yanzu basu da miji,ai kuwa Umma bata da rabo Alim Mota guda yasa aka kawo gidan ta kayan abinci,sai kallon yan gidan yakeyi,sai ya faki ido ya share Hawaye,gaba daya suma sunga ya rame,inda
Su Hamza suka birgeni ba wanda yayiwa Alim maganar Amana ko kadan,sai Baza ido yakeyi yaga Inda Amanansa zata bullo yayi tozali da ita ko bai mata magana ba zaiji sanyi kuma zai rage radadin sonta da yake daminsa,
Amma duk da haka yana cike da bakin cikin Amana taci Amanarsa ta zalinceshi gashi yana sonta Amma dole ya hakura da ita,maybe ma ta manta dashi tana ta rayuwarta cikin Jin dadi,a hankali ya furta Allah sarki ni..a fili .
To Alim dai yana ta baza idanu Ba Amana ba labarinta,tunowa yayi da Badriyya mutuniyarsa me handling case dinsa,
Komawa yayi wajensu ita da Huzaifa yace sorry frnd zanyi magana da kanwata for some few minutes,
Sun kebe waje daya shi da Badriyya Alim yace Sis wannan yarinyar fa? Badriyya tace wa kenan a hankali yace Aman...kasa karasawa yayi saboda yanda zuciyarsa ta kare,takaici yake son taso masa haka ya daure,
Badriyya ta lura da hakan sai tace oh...Amana ai sun bar gidan na....kafin ta karasa Alim yace Badai aure tayi kan aure na ba?Badriyya tayi dariya kamar bata San komai ba tace haba aure ba aure ba kawai Ummanta ce ta takura mata sai sun tafi Yola garinsu tayi mata talla.
Talla?Alim ya kwala da karfi yace to wlh bazai yiwu ba Sam,nan ya fara fada ni nake da iko da abata,
Badriyya batace komai ba sai tace ai na tausaya mata in ka ganta baza ka ganeta ba ta rame sosai kullum cikin kuka take tace wai sharri akayi mata aka rabaku gashi tana da ciki har ya fara girma,kasan me Baka ga bakar wahalar da take Sha da cikin nan ba,yanzu Amana ko maganar kirki ta daina sai da dalili,
Fiya fiya fiya Alim ya kama fyalla sauri kamar zai tashi sama,mota ya bude tare da fadawa ciki ya dinga bakin ciki da share kwalla na tausayin Amana har ya gaji yace ko mene ke kika jawo,ke kika jefa mu cikin masifa...nan take zazzabi ya rufeshi da ciwon kai mai tsanani cikin motar ya kudundune saida Huzaifa ya kaishi asibiti sannan suka koma gidansu Kano kenan.
Amana sun sauka lfy,wani gida suka shiga da Alama nan ne gidan su Umma,gidan Bulo ne ko siminti babu,daki biyu ne rak,ba mace a gidan iya Baban Umma ne kawai wato kakan Amana kenan,shi kadai yake rayuwa saboda tsabar masifar tsohon,masifaffe ne number daya,sabo da haka mata basa Zama da shi,haka Umma ta masa bayanin Amana da ita,zasuyi Sana'a,
Malam Nuhu yace to gwara da kukace zakuyi Sana'a ni dai kwandalata bazan kashe muku ba,gida dai gashi nan Ku zauna a waccen dakin baya Ga wannan ba zan yi muku abun sisi ba,
Amana dai tunda ta gaisheshi kala batace ba,tana rakube a bango kamar marainiya,tana tunanin Umma Babanta ta gado, Umma ce ta dan sai musu abinci har Malam Nuhu sukaci dan kadan dashi baifi mutum daya ba,
Amana kuwa bata cin shinkafa da miya amai takeyi da tashin zuciya amma Umma tace iskancine wlh baza ta sai mata komai ba,ga yunwa tana ji gashi bata da ko sisi,haka taci abincin tana ci ta fara Amai sosai Ai kuwa Malam Nuhu ya fara sauke Bala'i wannan iskanci ne wannan?yanzu haka ma cikin shege ne kuka gudo min nan za a cuceni, Umman Amana tace Haba Baffa da kai fa aka daura mata aure.
Amana ta ebu ruwa zata kuskure baki ta wanke hannu datt
ijon yace karki bata min gida kimin asarar ruwa ubanki ne ya sai min?kai gaskiya ubanku ya Sha wahala daku to wlh baza a zo a hanani walawa ba a gidana,
Amana kwalla ta share tare da tsugunawa tace kayi hakuri,kallonta yayi tsab yace iyye ke baiwar Allah yaushe kika daina harkar niganci da jagaliyar ne?Allah da iko yaushe haka ta faru?amma wanda ya aureki kamata yayi a bashi kyautar sarkin hakuri,yo ni da nine yausheeeeee tabbb,badan halin ki ba ebi ruwan kadan amma ki shiga bayi ki wanke hannu da baki ba a tsakar gidana ba bar ganin gidan ba siminti ba a lalata min gida,hakan Amana tayi ba tare da tacewa Malam kala ba,saboda tasan ma idan tayi magana to bakar magana zatayi domin ta kai wuya saboda halin da take ciki ga duniya ta bata darasi shi yasa bata cewa komai,kun San shi karatun duniya dole sai ka jishi,kuma ba iya kunne ne ke ji ba duk gangar jiki ce ke karba sosai.Amana sarkin zuciya ji take kamar tayi ta dukan Malam har ya suma,dan darajar Umma ta kyaleshi amma da sai ta nuna masa ita wace
Washe gari Umman Amana ta siyo gero ta fara kunun siyarwa ba na markade ba na daka su surfa ita da Amana su daka ayi Amana ta dauki katon botikin paint a kanta ta fita can wata majalisa,bata so gudun fushin Umma ta hakura, Amana kar A manta fa,dama can ta Saba da sana'a talla ne kawai bata taba yi ba amma duk aikin wahala tayishi kuma gata da zafin nama ba bata lokaci tunda tasan dole tayi ko dan abinda zasu sa a bakin salati bare ma ta San Umma ba kyaleta za tayi ba kuma bata son yi mata musu heeeee su Amana anji jiki fa da dane na tabbata Umma baza ta iya juya Amana ba,sai gashi yau Amana har mamakin wai ita Amana akewa abinda aka ga dama,da ace da dane har Baban Umma Malam Nuhu zata ci Ubansa. duniya kenan.
Amana kam yau satinsu Biyu da zuwa Yola,suna zuwa har gidajen sauran yan Uwan su Umma suna zumunci,
Amana tana zaune da waya a hannunta zata kira Hamza Umma ta kwace wayar kawo siyarta zanyi na kara jari,Amana shuru tayi ta zare sim dinta ta mikawa Umma dalleliyar wayarta sannan ta fashe da kuka sabo da wayar taka rage zafi da ita wajen kallon hotunansu tare da Alim sai taji sanyi a ranta ta samu nishadi to yau Umma ta kwace wayar ma amma duk da haka ba iya sim ta cire ba komai na wayar ta mayar kan Memory ta zare Memorynta ta hade ta daure a Leda tasa a bag dinta,
A banza Umma ta siyar da wayar Amana duk tsadarta,yayi dai dai da Alim wanda ya kasa hakura da Amana,ya shiga matsanancin Hali kullum sai ya Sha maganin bacci yake iya bacci kawai ya yanke shawarar kiran Amana ko muryarta zaiji ya rage zafi,canja new Sim yayi tare da dan nawa Amana kira amma ya makara wayar bata shiga,Badriyya ya kira itama ta gwada bata zuwa,yace Badriyya pls bani Address din inda suke a Adamawa,Badriyya tace wlh duk gidan basu sani ba amma dai gwaggo tasan sunan local government da suke a can da unguwar amma bata San wanne gida bane,tsaki Alim yaja yace kinga Illar rashin Zumunci wannan ba zumunci bane yanzu idan wani abu ya sameta kuma baza Ku sani ba، ya kamata ace ko kishiyoyi a dinga zumunci ana sanin asalin inda kowanne ke zaune Sabo da irin wannan. yanzu wannan me yake nufi kenan kuna Uba daya baku san inda yar uwarku take ba ku bakwa shiga harkar kowa gashi abin har yan Uwa na jini ma wannan ba dai dai bane,
Haka Alim ya dage ya dinga bala'in da masifa ya dinga saukewa Badriyya kwando kwando yana ta nuna mata illar rashin zumunci wasu kuma zumuncinsu ma sai suna Uwa daya Uba daya da iya su suke zumunci.Sai da ya gama yana huci kana yace hadani da gwaggo ta fada min Unguwar da lg din,
Bayan an fadawa Alim komai sai kuma ya fara jin dadi da nishadi kamar wanda akace masa ga Amana a gabansa,
Amana ce suke ta daka geron kunu,sanye take cikin kayan da ta saba dasu wata falkekiyar riga tshirt saboda cikinta ya dan fito sai jean trouser fari tayi kyau ba laifi Sabo da yanzu yawan addua yasa ta dan rage damuwa duk da cewar kullum sai tayi Kukan rashin Alim,amma yanzu ta danyi kiba kadan Sabo da cikin ya sata yar kiba da kyau yanzu,
Tun a tasha,Amana kuka kawai take shike nan an kara nesantata da Alim,kuka kamar ta kashe kanta,Umma tace kiyi kukan jini ma ke kika jawa kanki,
A mota ma kuka takeyi ana ta kallonsu,to Amana ko wa zai taimaka miki oho.yanzu ba kudi basu Hamza ba Alim baki da kowa sai Allah.
Yanda Amana take wannan halin haka Alim ya shiga sanadiyyar rashin Amana kusa dashi ya yarda itace rayuwarsa,shima ya rame sosai da kyar yake fita ma,yan uwansa da iyayensa sun rasa gane kansa,yayin da Mum ta Nemo masa wata yar kawarta Zainab wai Abba yayi masa aure ko zai samu nutsuwa,Abba kuwa ganin halin da Alim ke ciki sai ya yarda,
Har zance Mum tace sai yaje wlh,Alim yana zuwa yaga Zainab wata tambadaddiya marar tarbiyya nan take yaci mutuncinta tun daga sama har kasa yayi tafiyarsa,wannan dalilin yasa aka dage biki sai nan da 6mnths,
Saude kuwa ana can Ana Wainar siyarwa tare da ci gaba da kulle kullen tsiya.
Ranar da Amana tabi Umma suka tafi ranar da yamma Alim yazo gidan shi da Huzaifa,dalili kuwa ranar kawai yaji ba abinda yake so ya gani a duniya irin Amana,
Waya yayiwa Huzaifa wai yana so ya gaisar da iyayen Amana mata yayi musu alherin saboda yanzu basu da miji,ai kuwa Umma bata da rabo Alim Mota guda yasa aka kawo gidan ta kayan abinci,sai kallon yan gidan yakeyi,sai ya faki ido ya share Hawaye,gaba daya suma sunga ya rame,inda
Su Hamza suka birgeni ba wanda yayiwa Alim maganar Amana ko kadan,sai Baza ido yakeyi yaga Inda Amanansa zata bullo yayi tozali da ita ko bai mata magana ba zaiji sanyi kuma zai rage radadin sonta da yake daminsa,
Amma duk da haka yana cike da bakin cikin Amana taci Amanarsa ta zalinceshi gashi yana sonta Amma dole ya hakura da ita,maybe ma ta manta dashi tana ta rayuwarta cikin Jin dadi,a hankali ya furta Allah sarki ni..a fili .
To Alim dai yana ta baza idanu Ba Amana ba labarinta,tunowa yayi da Badriyya mutuniyarsa me handling case dinsa,
Komawa yayi wajensu ita da Huzaifa yace sorry frnd zanyi magana da kanwata for some few minutes,
Sun kebe waje daya shi da Badriyya Alim yace Sis wannan yarinyar fa? Badriyya tace wa kenan a hankali yace Aman...kasa karasawa yayi saboda yanda zuciyarsa ta kare,takaici yake son taso masa haka ya daure,
Badriyya ta lura da hakan sai tace oh...Amana ai sun bar gidan na....kafin ta karasa Alim yace Badai aure tayi kan aure na ba?Badriyya tayi dariya kamar bata San komai ba tace haba aure ba aure ba kawai Ummanta ce ta takura mata sai sun tafi Yola garinsu tayi mata talla.
Talla?Alim ya kwala da karfi yace to wlh bazai yiwu ba Sam,nan ya fara fada ni nake da iko da abata,
Badriyya batace komai ba sai tace ai na tausaya mata in ka ganta baza ka ganeta ba ta rame sosai kullum cikin kuka take tace wai sharri akayi mata aka rabaku gashi tana da ciki har ya fara girma,kasan me Baka ga bakar wahalar da take Sha da cikin nan ba,yanzu Amana ko maganar kirki ta daina sai da dalili,
Fiya fiya fiya Alim ya kama fyalla sauri kamar zai tashi sama,mota ya bude tare da fadawa ciki ya dinga bakin ciki da share kwalla na tausayin Amana har ya gaji yace ko mene ke kika jawo,ke kika jefa mu cikin masifa...nan take zazzabi ya rufeshi da ciwon kai mai tsanani cikin motar ya kudundune saida Huzaifa ya kaishi asibiti sannan suka koma gidansu Kano kenan.
Amana sun sauka lfy,wani gida suka shiga da Alama nan ne gidan su Umma,gidan Bulo ne ko siminti babu,daki biyu ne rak,ba mace a gidan iya Baban Umma ne kawai wato kakan Amana kenan,shi kadai yake rayuwa saboda tsabar masifar tsohon,masifaffe ne number daya,sabo da haka mata basa Zama da shi,haka Umma ta masa bayanin Amana da ita,zasuyi Sana'a,
Malam Nuhu yace to gwara da kukace zakuyi Sana'a ni dai kwandalata bazan kashe muku ba,gida dai gashi nan Ku zauna a waccen dakin baya Ga wannan ba zan yi muku abun sisi ba,
Amana dai tunda ta gaisheshi kala batace ba,tana rakube a bango kamar marainiya,tana tunanin Umma Babanta ta gado, Umma ce ta dan sai musu abinci har Malam Nuhu sukaci dan kadan dashi baifi mutum daya ba,
Amana kuwa bata cin shinkafa da miya amai takeyi da tashin zuciya amma Umma tace iskancine wlh baza ta sai mata komai ba,ga yunwa tana ji gashi bata da ko sisi,haka taci abincin tana ci ta fara Amai sosai Ai kuwa Malam Nuhu ya fara sauke Bala'i wannan iskanci ne wannan?yanzu haka ma cikin shege ne kuka gudo min nan za a cuceni, Umman Amana tace Haba Baffa da kai fa aka daura mata aure.
Amana ta ebu ruwa zata kuskure baki ta wanke hannu datt
ijon yace karki bata min gida kimin asarar ruwa ubanki ne ya sai min?kai gaskiya ubanku ya Sha wahala daku to wlh baza a zo a hanani walawa ba a gidana,
Amana kwalla ta share tare da tsugunawa tace kayi hakuri,kallonta yayi tsab yace iyye ke baiwar Allah yaushe kika daina harkar niganci da jagaliyar ne?Allah da iko yaushe haka ta faru?amma wanda ya aureki kamata yayi a bashi kyautar sarkin hakuri,yo ni da nine yausheeeeee tabbb,badan halin ki ba ebi ruwan kadan amma ki shiga bayi ki wanke hannu da baki ba a tsakar gidana ba bar ganin gidan ba siminti ba a lalata min gida,hakan Amana tayi ba tare da tacewa Malam kala ba,saboda tasan ma idan tayi magana to bakar magana zatayi domin ta kai wuya saboda halin da take ciki ga duniya ta bata darasi shi yasa bata cewa komai,kun San shi karatun duniya dole sai ka jishi,kuma ba iya kunne ne ke ji ba duk gangar jiki ce ke karba sosai.Amana sarkin zuciya ji take kamar tayi ta dukan Malam har ya suma,dan darajar Umma ta kyaleshi amma da sai ta nuna masa ita wace
Washe gari Umman Amana ta siyo gero ta fara kunun siyarwa ba na markade ba na daka su surfa ita da Amana su daka ayi Amana ta dauki katon botikin paint a kanta ta fita can wata majalisa,bata so gudun fushin Umma ta hakura, Amana kar A manta fa,dama can ta Saba da sana'a talla ne kawai bata taba yi ba amma duk aikin wahala tayishi kuma gata da zafin nama ba bata lokaci tunda tasan dole tayi ko dan abinda zasu sa a bakin salati bare ma ta San Umma ba kyaleta za tayi ba kuma bata son yi mata musu heeeee su Amana anji jiki fa da dane na tabbata Umma baza ta iya juya Amana ba,sai gashi yau Amana har mamakin wai ita Amana akewa abinda aka ga dama,da ace da dane har Baban Umma Malam Nuhu zata ci Ubansa. duniya kenan.
Amana kam yau satinsu Biyu da zuwa Yola,suna zuwa har gidajen sauran yan Uwan su Umma suna zumunci,
Amana tana zaune da waya a hannunta zata kira Hamza Umma ta kwace wayar kawo siyarta zanyi na kara jari,Amana shuru tayi ta zare sim dinta ta mikawa Umma dalleliyar wayarta sannan ta fashe da kuka sabo da wayar taka rage zafi da ita wajen kallon hotunansu tare da Alim sai taji sanyi a ranta ta samu nishadi to yau Umma ta kwace wayar ma amma duk da haka ba iya sim ta cire ba komai na wayar ta mayar kan Memory ta zare Memorynta ta hade ta daure a Leda tasa a bag dinta,
A banza Umma ta siyar da wayar Amana duk tsadarta,yayi dai dai da Alim wanda ya kasa hakura da Amana,ya shiga matsanancin Hali kullum sai ya Sha maganin bacci yake iya bacci kawai ya yanke shawarar kiran Amana ko muryarta zaiji ya rage zafi,canja new Sim yayi tare da dan nawa Amana kira amma ya makara wayar bata shiga,Badriyya ya kira itama ta gwada bata zuwa,yace Badriyya pls bani Address din inda suke a Adamawa,Badriyya tace wlh duk gidan basu sani ba amma dai gwaggo tasan sunan local government da suke a can da unguwar amma bata San wanne gida bane,tsaki Alim yaja yace kinga Illar rashin Zumunci wannan ba zumunci bane yanzu idan wani abu ya sameta kuma baza Ku sani ba، ya kamata ace ko kishiyoyi a dinga zumunci ana sanin asalin inda kowanne ke zaune Sabo da irin wannan. yanzu wannan me yake nufi kenan kuna Uba daya baku san inda yar uwarku take ba ku bakwa shiga harkar kowa gashi abin har yan Uwa na jini ma wannan ba dai dai bane,
Haka Alim ya dage ya dinga bala'in da masifa ya dinga saukewa Badriyya kwando kwando yana ta nuna mata illar rashin zumunci wasu kuma zumuncinsu ma sai suna Uwa daya Uba daya da iya su suke zumunci.Sai da ya gama yana huci kana yace hadani da gwaggo ta fada min Unguwar da lg din,
Bayan an fadawa Alim komai sai kuma ya fara jin dadi da nishadi kamar wanda akace masa ga Amana a gabansa,
Amana ce suke ta daka geron kunu,sanye take cikin kayan da ta saba dasu wata falkekiyar riga tshirt saboda cikinta ya dan fito sai jean trouser fari tayi kyau ba laifi Sabo da yanzu yawan addua yasa ta dan rage damuwa duk da cewar kullum sai tayi Kukan rashin Alim,amma yanzu ta danyi kiba kadan Sabo da cikin ya sata yar kiba da kyau yanzu,