← Book details Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 58

Sashe 42

Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ana gobe Amare zasu dawo Kano a fara biki angwaye tuni ma sun fara zuwa domin wasu duk daga kasar waje suka sauka,sai na wasu state duk sunzo,Alim yana cikinsu sun cika a Palo yana kwance a 3seater baya magana duk hirar da sukeyi,bacci kuwa ya daukeshi Bai Dade da bacci ba ya fara mafarkin Amana,Yana ta dariya a mafarki yana washsh....Amana zaki kasheni,sai yayi dariya yace my wife I love u,do u know what? Can yayi shuru sai sukaji yace I missed u,
Mika ya karayi ya ci gaba da mafarkinsa yana ta furta I love u.......I missed u......sai hawaye zirrrr zirrrr ta idonsa suna ta gangarowa yana I missed u kuka na kara yawa,sai yi yake ta yi,yayan Huzaifa Ahmad ne ya danawa Alim duka tashi banza na mamajo,zumbur Alim ya tashi yana taba fuska alamar Bai San ma yayi mafarkin ba,sai da ya nutsu ya tuno mafarkin Amana ya kara yi dama kullum aikinsa kenan,da masifa yace mene haka zaka tashe ni,Ahmad yace to dan iska kaje can wajen Amana ka sauke gajiyarka da kwadayinka zaka zo nan kana mana kukan banza da wofi,mayen mata kawai manniru,kwana dayan ma baza ka hakura ba,me yasa Baka taho da ita ba kasan Baka iya Zama saida ita,Alim ya cika tam amma ganin mutane sai ya share zance sai tsaki da yaja kawai yana turo bakin shagwaba kamar mace,Ahmad yace Allah....sannu Ayu....mu zaka kawowa iskancin shagwabarka nan to bada mu ba kaje can gaban Amanan ka mata, Huzaifa yace pls Babban yaya a kyaleshi haka.

Gobe dai za a fara party daya dan haka Amare da kawaye yan makaranta hadaddu Sabo da Badriyya duk kawayenta yan cikin birni ne bata kula na kauye,Sakina kuwa nata duk yan makarantar boarding schl dinsu ne,sai da suka zabo gogaggun yan wanka da masu kyau hadaddu su suka gayyata dinner saboda kar a lalata musu party,tuni Ishaq ya turo abokansa aka ebi Amare da kawayensu da wasu manyan ma da zasu dinna,Hamza ma yana da Mota yanzu zai tafi da kb,Isa da Haladu, Alim ne yace dole sai sunje dinner har dinkin dinner ya musu.

To fa Badriyya da kawayenta da sauran yan Uwa yan mata suna cikin kano gidan su ango Huzaifa,suna part dinsu maman Su Huzaifa rakanas ta dauko musu me lalle da kwalliya,dama Amare sun kashewa jikinsu kudi sunyi gyara sosai,Amana ta rasa me zata siyawa Amare gudun mawa kawai ta je gidan Me gari aka bata Saniyarta ta gado ta sa aka girba saniya da wuka,aka gyarata ta karbi motar Hamza aka zuba nama a buhun huna,ta figi motar Hamza sai cikin birnin kano,wani waje da akeyin kwangilar hada take away takai tace ayi dambun nama lafiyye a zuba a abin take away unique color na alfarma,
Zoben Gold na Alim da ya taba bata ta cire ta ba dashi jingina hhhh jinginar zobe huuu Amana aka bata kudin da niyar idan ta samu kudi zata basu su bata zobenta zoben Alim ne baza ta iya siyarwa ba,baza ta iya rabuwa dashi ba,haka ta karbe kudi ta biya masu dambun nama,computer Laptop dinta ta Nemo ta siyar da ita nan ta kara figar kyakyawar motar Hamza ta tafi Saloon da lalle cikin city,
Sai dare aka gama mata,a daren sabo da rashin tsoron Amana ta koma garinsu Wudil,
Amana fa ta fara daukan haske shining kawai takeyi,ga lalle ga gashi yasha gyara,washe gari Badriyya sai waya take radowa Amana tayi sauri tazo a fara kwalliya da ita,Amana kuwa kwalliya ta cancada kai kace yaune party, Hamzane yace kiyi amfani da matata Amana kije da ita kawai ni zamu yi Amfani da ta friend dina tafi tawa girma sosai kinga muna da yawa kuma zan kai su little Zaliha ma.
Tnx Bro cewar Amana.

Akwatinta guda tasa a bayan Mota,t a cokala takalmi me shegen tsini cikin kayan da akace na Huzaifa ne a cikinsu tasa wata arniyar atamfa baka da green,dinkin riga da skert yayi mugun da Meta fam,da kyar take mitsi a ciki,ga takalmi da gyale siriri na daukan magana malam,ta sha kyau kamar a sace ta kamar wata yar shugaban kasa,
Dama ga tafiyar Amana tun asalin ta takama da gadara ce,

Sai zuba kamshi takeyi gashin ta glass a fuskarta brown yayi mugun mata kyau gashi sake a gadon baya.
Wajen masu take away ta nufa tuni an gama mata komai nata na take away yayi kyau shi kanshi plastic da marfinsa da aka zuba dambun naman a ciki abin kallo ne,Bare ledar da aka sa plastic din a ciki wai wai,buhunan take away ta zuba a Mota,sannan ta sa kati a wayarta,sai canjin kudi sababbi dal dal yan dari dari da ta canja rapa biyu,ta zuba a pose din dake hannunta
Direct gidan su Huzaifa ta nufa da motarta,

Yan mata da samari sai sintiri sukeyi a gidan,wasu tsakanin mata da mazan ma har sun saba da juna sai shagali akeyi tare,musamman aka dauki dj aka sa a tsakar gida zai dinga kida kwana da yini har a gama biki,Alim duk wacce ta shige sai ya kalleta ko Amana ce ,amma Amana shuru,ko yaushe yana tsakar gida ko zai ga tazo amma shuru,Shine ya kutsa wajen Badriyya wai lallai sai ta kira Amana tayi sauri tazo ayi mata kwalliya,Badriyya shine fa take ta faman kiran Amana,
A waya.

Dama in baku manta ba Amana tasan gidan su Huzaifa,Alim yana zaune a farar kujera a tsakar gida gindin bishiya ga dj na tashi wasu na rawa wasu na hira,wasu matam gulmar Alim sukeyi ga wani me kyau ga haduwa kamar bature,wasu suce dan india ne,musamman kawayen su Asiya da kannen su Huzaifa yan iyayin tsiya yan kwalliya da daukan wanka,har fada sukeyi wai ina marar mutunci matar yaya Alim ne,gwarzuwa me tuko Mota from lagos to kano,sun ga Alim ba fara"a yanzu shi yasa basa tambayarsa Amana,wasu yan matan kuwa cewa suke mutum baya kula kowa sai ya dinga fitowa yana wayon kallon yan mata,
Wasu sukace munafukin banza ba fara'a baya kallon ko wacce da mutunci kamar yaga kashi to uban waye ya sa ya fito waje.

Amana ce ta danna uban Horn a kofar gidan,me gadi ya wangale kofa,ta shararo motar cikin gidan da Alim tayi tozali.

Sorry masu karatu bakuwa nayi yau shi yasa ban gama typing da wuri ba,n asan kun jirani,gashi ku karba na wullo muku.........

AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳

165-170

Official

By
AsmaBaffa

INA GAISHE KU MAKARANTA CIRANIN AMANA.

Da Alim tayi tozali ya harde a kujera ya tsirawa gate ido,tuni gaban Amana yayi mummunan faduwa,da kyar ta iya parking din motar sannan tasa hannu a saitin kirjinta ta dafe tana maida numfashi ga mugun sabon Son Alim da ya taso mata,tunani ta shiga na abinda ya faru a baya, Hawaye ke neman kwace mata a hankali ta maida kukanta tare da furta ah...Oh God ....bazanyi kuka ba...karki yi kuka Amana ke me dauriyace,amma duk da haka saida hawaye kadan ya fito tasa yatsa tare da dauke hawayen,sai da ta daidaita kanta sannan ta bude kofa tare da zuro kafarta daya waje,bata ma son ta kalli bangaren da Alim yake bare ya mata wani wulakancin tunda yace duk hanyar da zata hadasu kar ta sake ta bi ta wajen,sannan yace mata ya tsaneta,amma kuma dole sai ta wuce ta gaban su Alim sannan ta shiga cikin gidan part din Amare,
Alim kuwa kalle kalle yakeyi yanda Amana zata bullo bai kawo itace a Mota ba domin bata da Mota amma sai kallon motar yakeyi yana tuna inda ya san motar,

Alim a ransa yace wannan kamar motar Hamza,gashi wata kyakyawar kafar mace ya hango kamar ta yar India,takalmin kawai ya gani ya gane takalmin da yasiyo ne a London ya kaiwa Badriyya ta bawa Amana,wannan kenan Amana ce tazo da motar Hamza tunda dama yasan Amana ta iya driving,yes itace Alhmdllh cewar Alim.

Amana kuwa kasa fitowa tayi saboda da gudun kar tayi kuka,amma haka tayi shahada ta fito gaba daya da kyar saboda yanda dinkin ya tamke mata ko ina cip cip,tuwon mazaunan nan gasu sunyi dam sosai,
Ko mayafi bata yafa ba yana hannunta saboda taga cikin gidane kuma tayi ne Sabo da Alim yaga fa ba ta tashi takeyi ba wai irin ta manta dashi ma wanka take dauka shiga takeyi yanda taga dama,bayan kwalliyar duk dan shi akayi,shi kuwa Alim yaga duk kayan da ya siya matane a matsayin na Huzaifa,sai farin ciki ya lullubeshi,ga wani kyau na ban mamaki da Amana ta karo,da gogewa tare da zama hamshakiyar wata yar budurwa,
Ka rantse bata taba aure ba,

Nan take kishi ya tasowa Alim za a kalli Amana ga maza,to wai ma ina cikin dake jikinta tambayar Alim,ko ta zubar dashi lallai ma yarinyar nan zanyi maganinta,
Yana ta magana a zuci ji yake kamar yaje da gudu ya rungumeta,yama rasa inda zaisa kansa,Amana kuwa juyawa tayi tana fito da buhun hunan take away,da akwatinta,mayafinta na rike a hannunta tana ta tunanin Alim,ji take kamar taje itama ta rungumeshi yanda taga ya kara kyau da haduwa yar ramace kadan jikinsa ita ma sai kayi masa farin sani za kace ya dan ragu kadan,Amana a ranta tace uhmm dan gayu wannan uban daukan wanka da yayi haka kamar zaije dinner,
Ya wani zo ya zauna cikin mata sai kallonsa akeyi,awai dan a kalleshi an fada masa kowa ce zata soshi dan yana da kudi da kyau ya wani zo sai tallar kansa yakeyi,salon wai ace ana sonsa tsaki taja a hankali,kaji fa Amana to ina ruwanki.

Buhu buyu ta dauka tana tafiya das das kowa mata da Maza sai kallonta akeyi,Alim kuwa dafe kai yayi yana hadiyar yawu,yace lallai yarinyarnan kalli yanda take wani bawa mutane show kalli Maza sai kallonta akeyi lallai zan gyara mata zama wannan ai tangal tangal ne da aure kaji Alim to ina ruwanka da ita kaida ka tsaneta,
Chapter 42 · 0% Book details