Sashe 37
Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kb ne yace baku da hankali Ku ta abin duniya kukeyi ko,Baba ne ya fara tari ba ji ba gani sannan ya lafa,Amana ya damko yace ga Amana nan na daura mata nauyinku gaba daya saboda nayi Imani duk abinda zan muku Amana zatayi muku shi domin tafi kowa hankali,kyauta,da son zumunci,Amana ke ce wakiliyata ki rike min Iyalina ki maye gurbina,ga yayyenki Maza da sauran Ku hadu kuyi zumunci Ku tallafi juna,ku Manyan maza abinda Allah ya hore muku Ku tallafi yan uwanku Ku hade kanku babu yan Ubanci duk da nasan dama bakwa nuna yan Ubanci Ku kara akan Nada,
Ku Zama masu hakuri,juriya,hankali da nutsuwa duk fitinar da kukeyi da kuyi kokari Ku daina saboda nasan kun daina Amma a kara jajircewa duniya ba matabbata bace,hakuri da yafiya shine komai Ku rike wannan komai akayi muku banda daukan fansa Ku Zama masu yafiya da kawaici,a tsare mutunci, amma kar Ku bari a rainaku ko ubanye Ku taka masa birki.
Baba ya kara Suma ya farfado ya Dora da nasan Amana da saurin zuciya kike dan Allah ki dinga salalawa ga maza nan zasu tayaki Ku Kula da kanku,ga takaddun dukiyata nan nayi rubutu na fitarwa da kowa gadonsa yana nan rubuce a cikin littafin nan,Amana nafi yarda da ke me adalci ce dauki ki rike a hannunki,Amana dai sai kuka kawai Baba sai nauyi yake Dora mata Bai San ma Alim ya gujeta ba a lokacin da take bukatarsa.
Baba yace Ku kuma matana wacce taga zatayi aure to tayi aurenta amma ta barwa yayana a cikin yan uwansu ban yarda a rabamin kan yayana ba su zauna tare su so junansu zumincinsu yayi karfi,
Kuci gaba da min addua ko Allah zai karbi tubana ya yafe min,na barku da alheri.
Nan Baba tari ya turnukeshi yana ta murkususu Bai kara minti biyu ba yace Amana ki tallafi zuri'ata tayi kyau,ta gyara,abinda banyi ba kiyi musu kiyi iya kokarinki ki bar sauran ga Allah,
Gaba dayanku Maza da mata Manyan Ku tallafawa Amanata Ku Kula da kan....k...luf Baba ya cika Allah ya karbi rayuwarsa cikin wannan dare,
Sunyi kuka sunyi Addua mutane sun girgiza da wannan mutuwa,
A daren aka hada gawa akayi komai,washe gari Aka fito da gawa akayi mata sallah aka dauka akayi hanyar Makabarta a hankali akaji kamar makara na motsi, a tsaya a tsaya a kace Makarafa na motsi dubban jama'a suka fara guduwa sun firgita,
Liman da wasu tsirarine suka karasa kan makara tare da yayan Sulemanu suka duba Gawa sai akaga Baba ne yake motsi yana magana Badai asibiti zaku kaini ba a mai Dani gida ko na tsine muku,yana makyarkyata yace ina Amanata iceko tana Kula da Iyalina,ina su Hamza kai ...kuna tallafa mata kuwa,matana fa sunyi aure?karfa su auri kowa ina son matana ina kishinsu, idan sukayi aure to nima za a bani Hurulein
Ina littafin da dukiyata take ciki ne Ku raba kuwa?na bawa Haladu buhun masarata Biyar,Amana a bata sabon injin murzar taliya dana siyo rannan hhh
Ai su Hamza murna da gudu suka suri Baba suka koma gida ana Bai mutu ba Bai mutu ba,gawa taki rami gawa taki rami Allah wlh sai Baba.
Suna dawowa karfe Biyun rana Baba ya kara margayawa wannan mutuwar gaske ce domin Har doctor suka dauko ya auna ya tabbatar musu ya rasu, haka suka kara sabon kuka da komai aka kai gawar Sulemu Harka aka binne.
Amana kuka kamar ranta zai fita sauran kuwa har sun fara Hakura,Amma Amana itakam ba iya kukan mutuwa take ba,kukan rabuwa da masoyinta takeyi,ga nauyin da Baba ya daura mata,ga kuma ko secondary bata gama ba,bare ace tayi karatu tunda ba miji ta nemi aiki ta cikawa Baba Burinsa,
Ga cikin dake jikinta gashi Alim baima yarda nasa bane,ga bakin cikin sharrin da aka mata ga mutuwar uba duk ita kadai,shi yasa gaba daya ta kusa zarewa,yan uwa duk sun hadu da aluma masu zaman makoki ana ta yiwa Amana nasiha an zata kukan mutuce kawai,mutane sai ace Allah sarki Amana duk tafi shiga damuwa ai sun shaku da Babanta duk yafi sonta dole tayi kuka mutuwar tafi taba ta,
Tun Amana na kuka ita kadai a daki har ta fito waje ta kalli bishiyar da Baba ke Zama sanda tana Budurwa tazo ta wuce tana bouncing tace ai sai Baba Allah bar mana tsoho,yanda Baba ke ji da ita komai Amanansa,
Alim dinta ta tuno ta tabbatar da suna tare da tuni ya lallasheta ya sata nishadi da tuni ya zame mata gurbin uba,amma yanzu Babu me lallashinta,ya tarairayeta ya bata farin ciki ya tallafi danginta da iyayenta,shine gatanta,iyaye kuma duk lalacewarsu katanga ne,nan take Amana ta kurma ihu a kofar gidan ga maza masu zaman makoki su Hamza suna ciki,Amana ta fadi a kasa ta fara burbuwa tare da cewa wayyo Allah Bango ya fadi katanga ta rushe,gatana ya kare,gatana wayyo gatana,duniya kin juyamin Baya,kin juya min up side down,wayyo uwata wayyo Ubana...mijina...mijina shikenan nima.
Su Hamzane cikin hawaye suka riketa tare da danne kirjinta saitin zuciyarta domin wani numfashi yakeyi zuciyarta zata buga,
Da kyar aka samu numfashinta ya dawo normal,magana ta fara Ya Hamza a haka rami nima a binneni,nima dan girman Allah ku harbeni,zuciyarta ta nuna tace ku fasa min nan da Bullet,
Haladu dauko wuka a samu wani ya yankani dan Allah masifar danake ciki tafi karfina,
Kb da Isa ta kamo tace dan Allah ku farke min ciki mene Amfanina,kuka ta kara fashewa dashi,haka suka shigar da ita gida Amana ta fita daga hayyacinta,
Zazzabi tayi sosai sai hakuri ake bata,yau Kwana hudu da rasuwar Baba,Amana ta dan gana ta daina Kukan rashin Baba sai na Kukan rashin Alim,amma duk da haka idan taga abokan Baba da wani abu daya shafi Baba sai kuka mutuwar ta dawo mata sabuwa.
Kamar yau Huzaifa Badriyya ta fada masa rasuwar babansu dole ya taso Abbansa da kanwarsa Saddiqa suka taho ta'aziya,bayan sunyiwa su Hamza sai suka jera Baban su Huzaifa a gaba,Huzaifa da kanwarsa Saddiqa suna baya haka suka shiga har cikin gida domin Yiwa mata ta'aziyya,Amana tana ganinsu haka mutuwar Baba ta dawo mata sabuwa ta dora hannu aka tare da kwallawa da karfi wayyo wasu suna da Uba mu bamu dashi wayyo Ubanmu...ga wasu yan gata da Ubansu nan ma da kyar aka lallasheta,sai kuma tashin Alim ya fado shima,ganin Huzaifa suna yanayi da Alim sai ta fara Hawaye,
Tana ta kallon su Huzaifa kamar bata sansu ba,
Huzaifa bai sai me ya faru ba,yace Madam sai hakuri na sanarwa mutuminki yace min yaji kin yayanki ya fada masa dashi Akayi ta'aziyya zuwansa ukku ma,
Cak Amana ta tsaya da Kukan wato har ta'aziyya yazo ko nemanta baiyi ba da gaske ya hakura da ita,nan hawaye masu zafi suka zubo mata,
Ta kara wajen Haladu tace wai Alim yazo ta'aziyya?
Haladu yace dashi aka raka Baba har makabarta a mutuwarsa ta karshe, dashi akayi sadakar Uku,cewa yayi kar mu fada miki bai son ganin kukanki,
Amana a ranta tasan dan kar ya ganta ne ya tsaneta,
Amma kuma taji wani irin dadi da farin ciki tare da da ran Allah sa ya dawo gareta watarana,nan kuma tayi dariya hadi da hawaye,Amana bamu sanki da kuka ba ko ya kukace readers?
Huzaifa ne ya fito zasu tafi Su Abbansu na Mota da kanwarsa shi kuma Huzaifa sun tsaya a soro suna ta hira da Badriyya cike da so yana lallashin Badriyya,Amana ta hangosu a cikin mutane a fili ta furta ni bani da masoyi babu me lallashina sai kuka tare da tuna yanda Alim ke ji da ita.Ummanta ne suka fara mata fada sosai,kamar akanki aka fara mutuwa Allah ya hana Yiwa mamaci kuka haka,idan ma ganinki wani abu to ki sani Baba ba dawowa zaiyi ba kukanki ba gata bane a wajensa,masifa kike kara masa,daki Amana ta fada taita Kukanta.
Kwanan Baba Bakwai da rasuwa yau Alim yasa Abbansa,da Nura tare da dan autansu suka je sukayiwa yan gidan su Amana ta'aziyya,
Lokacin Amana ta kule a daki tana ta zazzabi da kuka,sai jin labari tayi Alim ne ya hana a tasota,wai zai dawo.
Ga abinci sun kawo musu Mota guda da kudi masu yawa sannan suka tafi,
Haladu ya ce Amana kai mijinki na sonki kinga yanda yake barka kuka kamar mace ke kyace babansa ne ya mutu,kb yace ai wannan Kukan Uba bai cancanci ayi masa ba sai dai Uwa,Isa yace kutmar Uba guy nan mace ne,kb yace a macen ma ta gaske,Hamza yace mamakin danayi mutum kai ba ubanka ba amma kafi yayan cikinsa kuka,
Haladu yace kai Burauba naga kuka wajen yaron nan kasan yaran masu kudi yayan Hutu ne inda kaga mace haka suke basu saba da gwagwamarya ba,wai guy nan daga cewa Amana ta suma tana kuka ta rame tayi duhu kawai ya barke da kuka shima yo ko uwatace ai bazanyi kuka ba bare mata,akan wata mace ka kama kuka,
Hamza yayi dariya yace ai kabewa ne,Isa yace ai mugun tumatir ne wlh.ammafa yana son Amana da ka ambaci sunanta za kaga ya kafe ka da ido ya shiga wani hali sai kwalla kuma kwal kwal,
Kb yace ai da ace ban san Amana ba da cewa zanyi asiri tayiwa guy nan,Hamza yace gaskiya Uwarsa ta haifawa Amana da Allah ya tsare ta haifawa Wata da,
Suna tsaye suka ga Amana yif tayi kasa ta sume saboda tsananin tunanin Alim,surarta sukayi Sai asibiti.
Kwananta uku aka sallameta tare da garga din Likita cewar a kiyaye damuwa zata mata illa kwanan nan,
Suna dawowa gida aka rufarwa Amana da nasiha cikin kuka tana share ido tace ku nutsu na baku labarin mece damuwata,
Kaf Amana ta kwashe ta fada musu tun farkon Haduwarta da Alim da irin zaman auren da sukeyi da soyayyarsu,da Mum Alim abinda take mata,da kuma gidan da ta zauna tare da Alim a garin,da sharrin da aka mata,sai rasuwar Baba,mata har Amana suka taya kuka,sun san Baza ta aikata haka ba,Hamzane yayi magana Lallai ko waye aka masa haka dole ya yarda kar kuga laifin Alim,
Ku Zama masu hakuri,juriya,hankali da nutsuwa duk fitinar da kukeyi da kuyi kokari Ku daina saboda nasan kun daina Amma a kara jajircewa duniya ba matabbata bace,hakuri da yafiya shine komai Ku rike wannan komai akayi muku banda daukan fansa Ku Zama masu yafiya da kawaici,a tsare mutunci, amma kar Ku bari a rainaku ko ubanye Ku taka masa birki.
Baba ya kara Suma ya farfado ya Dora da nasan Amana da saurin zuciya kike dan Allah ki dinga salalawa ga maza nan zasu tayaki Ku Kula da kanku,ga takaddun dukiyata nan nayi rubutu na fitarwa da kowa gadonsa yana nan rubuce a cikin littafin nan,Amana nafi yarda da ke me adalci ce dauki ki rike a hannunki,Amana dai sai kuka kawai Baba sai nauyi yake Dora mata Bai San ma Alim ya gujeta ba a lokacin da take bukatarsa.
Baba yace Ku kuma matana wacce taga zatayi aure to tayi aurenta amma ta barwa yayana a cikin yan uwansu ban yarda a rabamin kan yayana ba su zauna tare su so junansu zumincinsu yayi karfi,
Kuci gaba da min addua ko Allah zai karbi tubana ya yafe min,na barku da alheri.
Nan Baba tari ya turnukeshi yana ta murkususu Bai kara minti biyu ba yace Amana ki tallafi zuri'ata tayi kyau,ta gyara,abinda banyi ba kiyi musu kiyi iya kokarinki ki bar sauran ga Allah,
Gaba dayanku Maza da mata Manyan Ku tallafawa Amanata Ku Kula da kan....k...luf Baba ya cika Allah ya karbi rayuwarsa cikin wannan dare,
Sunyi kuka sunyi Addua mutane sun girgiza da wannan mutuwa,
A daren aka hada gawa akayi komai,washe gari Aka fito da gawa akayi mata sallah aka dauka akayi hanyar Makabarta a hankali akaji kamar makara na motsi, a tsaya a tsaya a kace Makarafa na motsi dubban jama'a suka fara guduwa sun firgita,
Liman da wasu tsirarine suka karasa kan makara tare da yayan Sulemanu suka duba Gawa sai akaga Baba ne yake motsi yana magana Badai asibiti zaku kaini ba a mai Dani gida ko na tsine muku,yana makyarkyata yace ina Amanata iceko tana Kula da Iyalina,ina su Hamza kai ...kuna tallafa mata kuwa,matana fa sunyi aure?karfa su auri kowa ina son matana ina kishinsu, idan sukayi aure to nima za a bani Hurulein
Ina littafin da dukiyata take ciki ne Ku raba kuwa?na bawa Haladu buhun masarata Biyar,Amana a bata sabon injin murzar taliya dana siyo rannan hhh
Ai su Hamza murna da gudu suka suri Baba suka koma gida ana Bai mutu ba Bai mutu ba,gawa taki rami gawa taki rami Allah wlh sai Baba.
Suna dawowa karfe Biyun rana Baba ya kara margayawa wannan mutuwar gaske ce domin Har doctor suka dauko ya auna ya tabbatar musu ya rasu, haka suka kara sabon kuka da komai aka kai gawar Sulemu Harka aka binne.
Amana kuka kamar ranta zai fita sauran kuwa har sun fara Hakura,Amma Amana itakam ba iya kukan mutuwa take ba,kukan rabuwa da masoyinta takeyi,ga nauyin da Baba ya daura mata,ga kuma ko secondary bata gama ba,bare ace tayi karatu tunda ba miji ta nemi aiki ta cikawa Baba Burinsa,
Ga cikin dake jikinta gashi Alim baima yarda nasa bane,ga bakin cikin sharrin da aka mata ga mutuwar uba duk ita kadai,shi yasa gaba daya ta kusa zarewa,yan uwa duk sun hadu da aluma masu zaman makoki ana ta yiwa Amana nasiha an zata kukan mutuce kawai,mutane sai ace Allah sarki Amana duk tafi shiga damuwa ai sun shaku da Babanta duk yafi sonta dole tayi kuka mutuwar tafi taba ta,
Tun Amana na kuka ita kadai a daki har ta fito waje ta kalli bishiyar da Baba ke Zama sanda tana Budurwa tazo ta wuce tana bouncing tace ai sai Baba Allah bar mana tsoho,yanda Baba ke ji da ita komai Amanansa,
Alim dinta ta tuno ta tabbatar da suna tare da tuni ya lallasheta ya sata nishadi da tuni ya zame mata gurbin uba,amma yanzu Babu me lallashinta,ya tarairayeta ya bata farin ciki ya tallafi danginta da iyayenta,shine gatanta,iyaye kuma duk lalacewarsu katanga ne,nan take Amana ta kurma ihu a kofar gidan ga maza masu zaman makoki su Hamza suna ciki,Amana ta fadi a kasa ta fara burbuwa tare da cewa wayyo Allah Bango ya fadi katanga ta rushe,gatana ya kare,gatana wayyo gatana,duniya kin juyamin Baya,kin juya min up side down,wayyo uwata wayyo Ubana...mijina...mijina shikenan nima.
Su Hamzane cikin hawaye suka riketa tare da danne kirjinta saitin zuciyarta domin wani numfashi yakeyi zuciyarta zata buga,
Da kyar aka samu numfashinta ya dawo normal,magana ta fara Ya Hamza a haka rami nima a binneni,nima dan girman Allah ku harbeni,zuciyarta ta nuna tace ku fasa min nan da Bullet,
Haladu dauko wuka a samu wani ya yankani dan Allah masifar danake ciki tafi karfina,
Kb da Isa ta kamo tace dan Allah ku farke min ciki mene Amfanina,kuka ta kara fashewa dashi,haka suka shigar da ita gida Amana ta fita daga hayyacinta,
Zazzabi tayi sosai sai hakuri ake bata,yau Kwana hudu da rasuwar Baba,Amana ta dan gana ta daina Kukan rashin Baba sai na Kukan rashin Alim,amma duk da haka idan taga abokan Baba da wani abu daya shafi Baba sai kuka mutuwar ta dawo mata sabuwa.
Kamar yau Huzaifa Badriyya ta fada masa rasuwar babansu dole ya taso Abbansa da kanwarsa Saddiqa suka taho ta'aziya,bayan sunyiwa su Hamza sai suka jera Baban su Huzaifa a gaba,Huzaifa da kanwarsa Saddiqa suna baya haka suka shiga har cikin gida domin Yiwa mata ta'aziyya,Amana tana ganinsu haka mutuwar Baba ta dawo mata sabuwa ta dora hannu aka tare da kwallawa da karfi wayyo wasu suna da Uba mu bamu dashi wayyo Ubanmu...ga wasu yan gata da Ubansu nan ma da kyar aka lallasheta,sai kuma tashin Alim ya fado shima,ganin Huzaifa suna yanayi da Alim sai ta fara Hawaye,
Tana ta kallon su Huzaifa kamar bata sansu ba,
Huzaifa bai sai me ya faru ba,yace Madam sai hakuri na sanarwa mutuminki yace min yaji kin yayanki ya fada masa dashi Akayi ta'aziyya zuwansa ukku ma,
Cak Amana ta tsaya da Kukan wato har ta'aziyya yazo ko nemanta baiyi ba da gaske ya hakura da ita,nan hawaye masu zafi suka zubo mata,
Ta kara wajen Haladu tace wai Alim yazo ta'aziyya?
Haladu yace dashi aka raka Baba har makabarta a mutuwarsa ta karshe, dashi akayi sadakar Uku,cewa yayi kar mu fada miki bai son ganin kukanki,
Amana a ranta tasan dan kar ya ganta ne ya tsaneta,
Amma kuma taji wani irin dadi da farin ciki tare da da ran Allah sa ya dawo gareta watarana,nan kuma tayi dariya hadi da hawaye,Amana bamu sanki da kuka ba ko ya kukace readers?
Huzaifa ne ya fito zasu tafi Su Abbansu na Mota da kanwarsa shi kuma Huzaifa sun tsaya a soro suna ta hira da Badriyya cike da so yana lallashin Badriyya,Amana ta hangosu a cikin mutane a fili ta furta ni bani da masoyi babu me lallashina sai kuka tare da tuna yanda Alim ke ji da ita.Ummanta ne suka fara mata fada sosai,kamar akanki aka fara mutuwa Allah ya hana Yiwa mamaci kuka haka,idan ma ganinki wani abu to ki sani Baba ba dawowa zaiyi ba kukanki ba gata bane a wajensa,masifa kike kara masa,daki Amana ta fada taita Kukanta.
Kwanan Baba Bakwai da rasuwa yau Alim yasa Abbansa,da Nura tare da dan autansu suka je sukayiwa yan gidan su Amana ta'aziyya,
Lokacin Amana ta kule a daki tana ta zazzabi da kuka,sai jin labari tayi Alim ne ya hana a tasota,wai zai dawo.
Ga abinci sun kawo musu Mota guda da kudi masu yawa sannan suka tafi,
Haladu ya ce Amana kai mijinki na sonki kinga yanda yake barka kuka kamar mace ke kyace babansa ne ya mutu,kb yace ai wannan Kukan Uba bai cancanci ayi masa ba sai dai Uwa,Isa yace kutmar Uba guy nan mace ne,kb yace a macen ma ta gaske,Hamza yace mamakin danayi mutum kai ba ubanka ba amma kafi yayan cikinsa kuka,
Haladu yace kai Burauba naga kuka wajen yaron nan kasan yaran masu kudi yayan Hutu ne inda kaga mace haka suke basu saba da gwagwamarya ba,wai guy nan daga cewa Amana ta suma tana kuka ta rame tayi duhu kawai ya barke da kuka shima yo ko uwatace ai bazanyi kuka ba bare mata,akan wata mace ka kama kuka,
Hamza yayi dariya yace ai kabewa ne,Isa yace ai mugun tumatir ne wlh.ammafa yana son Amana da ka ambaci sunanta za kaga ya kafe ka da ido ya shiga wani hali sai kwalla kuma kwal kwal,
Kb yace ai da ace ban san Amana ba da cewa zanyi asiri tayiwa guy nan,Hamza yace gaskiya Uwarsa ta haifawa Amana da Allah ya tsare ta haifawa Wata da,
Suna tsaye suka ga Amana yif tayi kasa ta sume saboda tsananin tunanin Alim,surarta sukayi Sai asibiti.
Kwananta uku aka sallameta tare da garga din Likita cewar a kiyaye damuwa zata mata illa kwanan nan,
Suna dawowa gida aka rufarwa Amana da nasiha cikin kuka tana share ido tace ku nutsu na baku labarin mece damuwata,
Kaf Amana ta kwashe ta fada musu tun farkon Haduwarta da Alim da irin zaman auren da sukeyi da soyayyarsu,da Mum Alim abinda take mata,da kuma gidan da ta zauna tare da Alim a garin,da sharrin da aka mata,sai rasuwar Baba,mata har Amana suka taya kuka,sun san Baza ta aikata haka ba,Hamzane yayi magana Lallai ko waye aka masa haka dole ya yarda kar kuga laifin Alim,