← Book details Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 58

Sashe 35

Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Magana tayi tace to..to..to naga Alama tana ta zaune taki kwanciya sai satar kallonsa takeyi,
Kashe computer yayi Amana na ganin haka tayi Hamdala a ranta,bai kwanta ba sai ya zauna cure a bed din,Hannunta ta mika a hankali ta kama wasa da kafarsa,
Dauriya kawai yakeyi,gajiya Amana tayi matsa jikinsa cikin sigar shagwaba tace am in...in....the...mood kaji kayi wani abu sweet mana,ta kare zancen tana shafa hannunsa,matsawa yayi gefe yace dazu da nace I need u me kika ce min?sai yanzu zaki neman da yake bukatarkice I hope zan iya miki yanzu amma na gaji kin makara
Jiki a sanyaye ta Mike zata bar dakin tare da cewa ahhhh.....ok.....never mind ta fara tafiya ya fisgota ta fado kansa flat ya mata ya fara kissing dinta dama Amana jiran kadan takeyi ba bata lokaci suka gigita Kansu kamar mayunwata,Sosai Amana ke enjoying din abinda Alim ke mata ta bada hadin kai ta dage tayi iya yinta,ta gama baje basirarta a kan Alim,ta mishi abubuwa masu rikita hankali wanda ya Sha mamakinta yanda ta tafiyar dashi,gata gwarzuwa ce akwai juriya da jajircewa na ganin ta bawa Alim abinda yake so ,shima hakan take
Yau su Alim harda kwallar dadi da farin ciki,bai taba Jin makamancinsa ba,Amanansa ta dabance sai da yayi round 3 ya kyaleta hakanma kawai kyaleta yayi dan kar ya shiga hakkinta Bai sani ba domin Amana Idan zaiyi sau 100 baza ta nuna masa alamar ta gaji ba sai ta daure,duk da cewa itama tana da karfin sha'awa kuma uwa uba tana Jin dadin harkar kasancewar mijinta ya hadu ta ko ina,style iri iri sunyi shi,tasha sambatu wajen Alim itama haka,saida suka nutsu ya shiga sa mata jerin Albarka,wanka sukayi tare da tsarkake jikinsu sai nafeela da sukayi da adduoi suka fada Bed hade da manne juna sai bacci.

Sulemanu Harka jiki yaki dadi duk yanda za ayi anyi masa ana ta kashe kudi amma kafunsa sunki doruwa,sai ma kara lalacewa sukayi yanzu kullum sai an fitar dashi an Shanyashi a rana a kofar gidansa,
Yauma yana kwance a tsakar gida sai numfarfashi yakeyi ya tambayi Badriyya ke ina Amana ta ke zaune a garin nan?Badriyya tace Baba nima ban sani ba tana dai zuwa dubaka kuma ta ebi kayan sawa ta tafi,duk kusan ta kwashe kayanta na sawa,
Baba yaga bashi da kudi kudinsa ya kare gashi ba fita yake ba ba lfy,ga ba Amana ba mijinta babu me bashi domin ko sanda Amana na lagos har kudi take tura masa.
Baba ya kwalla kara yace Wannan kwai gantalalliyar yarinya akan wannan shegen yaron ta bar gidana saboda nace baza ta koma ba,
Indai Namiji ne gata gashi na yafe mata taje tabi mijinta akan haka harda barin gidana,to ni dai na yafe mata ta koma dakinta yarinyar kirki ta gari bani da kamarta ga biyayya tafi kowa Jin tausayi na da bin umarnina,matansa da yaransa ya Tara ya fada musu dalilin barin gidansa da Amana tayi,babu wanda ya kulashi sai Umman Amana tace Baka kyauta ba kayi butulci,nan dukka gidan Akayi caaaaa akan Baba,yace to kuzo Ku dakeni Ku huta

Isa yace Baba matar da kake zargi itace Umman Alim wlh ba ita bace Baka ganeta ba,ni naga matar ganin idona,Babar Alim fara ce waccen kuma Baka ce,
Ka bari ayi bincike tukun amma mijin Amana mutumin kirki kalli yanda ya mai damu mutane,

Nan Sulemanu Harka yace to latso min waya ka kira min Amanata,Hamza ya fara kira amma bata shiga har Number Alim duk basa shiga,

Da dare Alim Zaune a saman kujera Amana na kasa magana ya mata honey yau mu dan fita mu zaga gari mana,
To bari mu shirya ko,wanka sukayi fes dasu suka hade cikin shiga me matukar kyau sannan suka kulle wajensu suka fito,da yake akwai wuta ko Ina da haske ba laifi,
Sunzo tsakar gida su shiga Wajen Sa'adatu suka gaisa sai ga Yarta budurwa Iklima ta fito sai kallon Alim takeyi taga baiwar cikar zati

Mum gaba daya ta rasa sukuni sabo da rashin Alim,gashi Abba yaki saurarar zancenta yace karyane dansa yana nan lafiya,
Su Nura ma shareta sukayi kowa ya kama harkar gabansa,matar Nura shanawa sukeyi da mijinta saboda Mum tana cikin damuwa bata kulasu,Matar Nura ke Kula da Aabid sosai.Mum kuwa kullum kuka takeyi harda Jin haushin Abbansu Alim shi ya cuceta ya tura mata da yaro aiki wani state.

Amana na kallon yanda Iklima yar Sa'adatu take kallonsa ta faki idon kowa ta dallawa Iklima harara,radawa Alim tayi tashi mu tafi tare da tamke fuska wai haushi,a hankali yace mu dan zauna ayi hira ko ma Saba dasu,Amana tace pls kaga ni Bana son wani sabo,mu kadai zamu dinga rayuwarmu.
Me za
Muyi a wajensu dama mutuncin makwaftaka yasa muka shiga,
Sa'adatu ce ta fito dauke da lemo da ruwa amma Amana tace sun koshi tafiya zasuyi,Sa'adatu tace da kun zauna munsha hira?Amana tace zamu dawo watarana ai,Alim yace to Mene mu zauna mana Amana cikin Jin haushinsa tace ko second Biyar bazan kara ba tashi mu tafi kawai ai yawo zamuje.muje to ya Mike sukawa matar sallama Amana tasa Alim a gaba kamar danta,suna fita Iklima tace Mama wlh wannan matar tasa masifaffiyace kuma kamar itace mijin yanda take abu ta gama mallake bawan Allah, wa ya sani ko asiri ta masa da ganin Alama,Sa'adatu cikin fada tace ina ruwanki dasu ki iya bakinki,Iklima tace ai naga ta gama mallakeshi wlh har ya bani tausayi.

Alim suna fita Amana tace Allah ya taimaki yarinya watarana ta gwada min hauka kamar yau ta gane shayi ruwane da kanta kamar kwallon kwakwa,Alim yayi murmushi ke ki kwantar da hankalin ki ke kadai ce ba Kari don ta kalleni sai me ni kinga na kalleta ne?to me yasa zaka ce mu zauna?nufina mu dinga zumunci,to bazamuyi dasu ba karma ka jawo na koresu daga gidan nan.
Sorry sarkin zuciya ni dai ki huce kar mu koma gidan ki hanani Harka,da wasa Amana ta dalla masa harara sunan Babane fa Harka,sorry na manta I swear
Dariya Amana tayi tare da rungumeshi tsam haba dai ai kome zaka min bazan hanaka komai ba,ba wannan shirmen ai sai kace yarinya marar tunani,idan ana Jan fada haka ai aure baya lasting duk fadan da zakuyi da mutum matukar baza Ku raba makwanci ba to dole a shirya da wuri bare har ya kai ga saki,kiss ya manna mata tare da shafa wuyanta a rungume da juna suke
Suna tsaye sai ga Baba tsoho yana takawa da kyar ya dawo daga masallaci ya kara biyowa ta wannan lungun me duhu,wannan karan tsohon masifa yakeyi a hanya sosai,Alim yace laaa ga tsohon nan na ranar nan mun ga ta kanmu

Tsoho Ashe yaji me Alim yace yace bakuga ta kanku ba sai Allah ya damkeku da kansa,
Yau ba ta Ku nakeyi ba domin kun Zama Bala'i sai sadaka,
Amana tace Malam me aka maka yau kake fada?yace kedai bari karuwai wlh wasu yarane suka bata min tsoho ya fara basu Labari wai wasu Samari ne a masallaci kullum sai sun dagashi bayan an idar da sallah saboda bashi da karfi da kyar yake tashi ma,
Kawai sai rannan matarsa ta haihu gobe suna shine ya bada Sanarwa a masallaci gobe za a rada suna matarsa ta haihu samarin nan suna jin haka suka saki dariya tare da cewa ah....tsoho Ashe kana da karfi yanzu har matarka ta samu ciki ta haihu ta wlh baza su kara dagashi ba sai dai idan ya kasa tashi ya kwana cikin masallaci tunda har yasan zai iya wata ciki,ai kuwa su Alim suka dinga dariya,Amana tace Baba dai dai sukayi wlh gwara haka,
Tsoho yace ai gwarani ba dan iska bane irinku,karuwai shedanu,Amana tace wlh Tsoho muna da aurenmu fa,yace ban yarda ba ko sama da kasa zata hade bazan yarda ba kuna da auren zaku dinga bin lungun masu shegen duhu ba kunya ba komai,
Da Allah kar Ku kara min takaici wai yanzu ace yaronka Bai jawo ma magana ba wasu a titi na kwararo su dinga sawa zuciyarka na tafasa.
Dariya suka karayi tsoho yace kwayi da wani marasa mutunci.
Alim ne ya zaro kudi masu yawa ya mikawa tsohon Baba ga wannan ka siyi rago ko
tsoho yace wuuu...rufani ka sayani dannan niiiiii na karba kudinku na haramci inma cin hanci ka bani wato dan na dinga rufa muku asiri kuna shekewa to ni Bana karbar cin hanci,bazan rufa muku asiri ba,zan karba na gode kuma amma kar kusa rai zaku zauna lafiya a unguwar nan sai na sa me gidan ya koreku,tsoho ya karbe kudinsa yana godiya,wata mata tazo wucewa Ashe tasan Amana nan suka gaisa sosai,tsohon nan har ya fara tafiya ya dawo yace Delu wato ke kike daure musu gindi ko har gaisawa kukeyi?Delu tace kaji tsoho da sa Ido to har duwaiwai na hada na daure musu karewarta,tsoho yace Bana ja'in ja da matar wani yayi tafiyarsa yana masifa wlh sai ya tonawa su Amana Asirinsu.

Delu tace tsohon nan sai hakuri ta wuce,su Alim suka tafi yawonsu sosai suke Jin dadin yanayin.
Chapter 35 · 0% Book details