Sashe 44
Ciranin Amana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har wajen kaka tsohuwa taje har an shirya Aabid,kowa yaba irin kyan da Amana tayi akeyi da wanda ya Santa da wanda Bai Santa ba,Aabid na Jin muryarta ya dago kansa da sauri tare da rugowa da gudu ya daka tsalle ya dane ta,dagashi sama tayi suna ta dariya,Momy ina kika tafi bana ganinki? Amana tace unguwa naje nan suka dinga surutu tare,sai ji tayi gaba daya har an tafi tana nan,Aabid ta dauka tayiwa tsohuwa sallama,tana fita Alim ma ya fito cikin shiga ta alfarma kamar wani dan sarki,yasha kyau sai kallon juna sukeyi kowa na yaba shigar dan uwansa,Alim cikin shadda Fara kal yake komai fari yayi kyau na gaske,suma taci kudi,kamshi da kyalline kawai ke tashi,
Tunawa Alim yayi ai sunyi fada da Amana basa shiri da sauri ya dauke kai ya juya,Itama Amana a hankali tace au jaka ni kamar muna shiri na wani kalleshi,to wanne ma kyau yayi shi din me, me ya hadani dashi tsaki taja ta wuce motarta ta bude tare da sa Aabid a gaba,Aabid ya fito fit yace Momy ga Daddy can motarsa tafi kyau muje a tasa,Aabid ya kwalawa Alim kira Daddy ka jiramu muje a taka,Amana tace to bazan shiga motarsa ba dalla wuce muje,Alim ma yaji me Amana ta fada shima magana yayi da dan daga murya yanda zata jishi ko kinzo ba daukanki zanyi a motata ba,ko kinji nace zan daukeki dama,da masifa Amana tace oho ko kace ma ba shiga zanyi ba ehe,kuma a daina kallona za a cinye min kurwa to tawa daci gareta kurwata kurrrr ta karasa tana huci,.
Alim shi dariya ma ta bashi da birgeshi,kinga na kallekine?baki kyau ba dai,ga masu kyau can sun tafi party,Da masifa Amana ta hayayyako me zasuci da kai ragowar mata,woooo ragowar mata an gama da kai sai ragowa zasu samu,mata nawa ka aura me auri saki,ina fada ma watarana wata sai ta harbeka kowa ya huta,
Dariya ta kusa kwacewa Alim sai ya kara mazewa ya tamke fuska yace haka na gani shi yasa kike bin abokaina kina fada musu su bani hakuri na dawo dake,
Kugu Amana ta rike tace kalleni tsaf na wuce ajinka Malam ai kai na gama da shafinka na jefa a shara masu kwashe shara sunzo sun kwashe ka an zubaka a katon rami.sai yanzu ma nakejin haushi kaina na auri Kazami yan... yan... yan.....tana yatsina fuska ta kara da cewa ko kyau babu,yanzu ma da kasan munin da kayi da baka je dinner ba ta tsaya tare da murguda baki,
Alim dariya fa yake tayi a zuciya ya samu abinda yakeso,da sauri yace wannan kuma karya kikeyi yarinya,kuka ne ya tahowa Amana tayi sauri ta maida shi tare da jan kwafa ta shige mota,Aabid Bai San me sukeyi ba har ya gaji da jira,kowanne ya figi mota ya hau titi suna tafiya idan Alim ya figi mota ya wuce Amana sai Amana ta cisga ta wuceshi itama,
Idan masifa ta ciyosu sai kowa ya danna mugun horn,yanzu Alim zai wuce Amana ya sauke glass kasa ya zo saitinta da mota ya fara mata gwalo,itama kuwa ta tako da karfi ta masa gwalo wullo wai dan ta tura masa haushi da yawa ta dallaro harshenta ta barshi a haka,tana kaga kaga suna hada Ido ta glass tace nafi karfinka baza ka iya Dani ba,na Riga na maka nisa na wuce ajinka,ta ce woooo wulluuuuuu, ta zuge glass tana haki cike da masifa tace nayi maganinsa ai Bai isa na kyaleshi ba,bazai ja Dani ba,
Alim kuwa yana rufe glass ya dinga dariya kamar me har suka karasa wajen dinner.tare suka tsaya Amana da Bala'i ta fito wai irin kar Alim ya rainata.
Alim kuwa ya shirya me zai taokaneta dashi.
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
170-175
Official
By
AsmaBaffa
MARCYCOOL JINJINA GAREKI,
DUK MASU SHARHI WANNAN PAGE NAKUNE,SANNUNKU DA KOKARI INA MATUKAR JIN DADI,KUNA KARA MIN KARFIN GWIWA.
Amana rike da hannun Aabid sauri tayi ta shige wurin da ake event din,wow wuri ya hadu sosai Dinner Baban Ishaq angon Sakina ce yau nasa da ya hada musu aka fara yi,Amare zaune da angwaye sunsha kyau,wurin ya cika da mata da samari dangin Amare da Angwaye,ga kawaye da abokai,wanka iya wanka,mata iya mata maza iya maza a wajen nan ba a magana.
Aabid kuwa da gudu ya tafi wajen Nura da matarsa da yarsu,Amana ana tafiya kwas kwas sai kallonta ake ta faman yi musamman maza,
Ta wuce zata zauna Ashe Alim yana bayanta duk inda tasa kafa sai yasa,sabo da kida bata ji tafiyarsa ba,Amare harda dagowa Amana Hanu suna zaune,Badriyya ta dagawa Alim babban yatsa shima ya daga mata tare da murmushi,Sakina ta masa inkiya da Ido,nan take Alim ya bar kusa da Amana wajen Asiya yaje tana zaune ita da Ahmad yayan Huzaifa ,Alim fuska ba wani walwala ya furta Asiya tashi ki janye min wancen Ku zauna tare,
Dariya Asiya tayi tace yaya Da Alama Allah laifi kayi mata shi yasa kabi ka nacewa mata ka kyaleta ta huta pls,
Zan mareki kije kiyi abinda nace,Ahmad yace kai masifaffe mufa ka ishe mu da wannan matartaka tunda tazo yanzu duk gidan biki gulmarku akeyi iskancinka gaban kowa yi kakeyi Ayu kawai.
Kana surikin nawa? ai an kusa bikinka idan naga dama sai na hanaka kanwata ka rufawa kanka asiri cewar Alim, Asiya kuwa tuni ta cika Umarnin Alim zaune ita da Amana dan auta ma wajensu ya dawo yana fadawa Amana wai ga wata can dan Allah taje ta hadasu ko zata soshi,Amana tace dan yaro dakai to ba Dani ba,dariya sukayi,Alim yana kallonsu yana ta Jin dadi.
Amarya Badriyya da Huzaifa MC ya kira su fito fili ana bukatarsu,Amana ce ta fara mikewa ta shiga fili, Amana bata rawa bata taba yin rawa ba saboda kar a rainata wai hee baya ga haka ma bata iya ba.
Yan Dari Dari ta fara lika musu, cikin takun isa da birgewa sai ga Alim yazo ya fara likawa Amarya da Ango yan Dubu Dubu shima yana liki
Kallon Amana yake yi idonsa na kanta suna hada Ido sai ya maka mata harara itama kafin kace me ta rama harda murguda baki,
mutane ne suka zo yuuuu mata da maza suka lullube wajen kowa liki yakeyi,wani Namiji ya fara likawa Amana kudi sosai,Alim takaici ya kama shi,Amana juyawa tayi ta dinga likawa Saurayin nan kudinta,Alim kamar ya hadiyi zuciya ya sheka lahira,
Kafin kace me ransa yayi bakinkirin,har idonsa ya canja color tsabar bala'in da yakeji,
Yana ta likinsa Bai fasa ba cikin zafin nama ya samu ya shige tsakiyar Amana da saurayi ya musu kerere a tsakiya tare da ci gaba da yiwa Amare likin Naira.
Amana Jin kamshin turaren Alim yasata lumshe Ido nan take ta fada tunanin rayuwarsu sanda suna tare yana nannadeta cikin kirjinsa ta shaki kamshinsa da dumin jikinsa son ranta
Matsowa yayi yanda zata ji shi cikin bacin rai muryarsa har rawa takeyi nace ki fita bana so me kikeyi haka kinawa kato liki for God sake, ko kallonsa Amana batayi ba,cikin karajin da Amana ce kadai zata ji ya furta zan yi maganinki ki bar ganin Ina wasa dake akan wannan bazan miki da sauki ba.
Amana ba walwala ta furta sannu Ubana Sulemanu kai awa?mene hadina da kai ta fada tana Balla masa uwar harara,haka kikace?cewar Alim,Amana ta kalleshi up and down tana fari da Ido tace wacce grass ce kai ko nace wanne weed ne? Wanne ruwan kwatar ne?wacce shara ce?
Me likawa Amana kudi tuni kudinsa suka kare yayi waje kuma yana jin fadan da sukeyi da Alim a ransa yace saurayi kayi asarar budurwa sai dai ka koma wajen Bazawara Amma wannan Budurwar yar dagwas gwas ni zan kwaceta.
Alim da ya tuno me yayi sai ya tuna fada sukeyi ba kishinta yakeyi ba ina ruwansa,
Sai ya canja magana da cewa taimaka miki nakeyi saboda bakiyi kyau ba abin kunyane aga ana miki liki ke baki ga dariya ake miki ba,Amana taci gaba da masifa Alim kake ko wa?ka sakar min mara nayi fitsari pls nace bana yinka kaje ka nemi irinka yanzu nafi karfinka ehe yawwa asakar min mara nayi fitsari,, murmushi Alim ya saki wanda ke kara masa kyau, Amana a ranta tace mijina me kyau, Alim ne ya katse mata tunani da cewa idan naki fa?
Itama ta fara magana kasan ni ai kasan Halina ko na gwada ma? ni da kake gani na ba mutuncine dani ba,ni abin kunya idan ya ganni to guduwa yakeyi saboda uwar gidansa tazo Amana ta furta cikin fushi kamar bata taba dariya ba,Alim yace hmm wanda kikewa ne suke kyaleki yarinya,Amana ta maida martani gaka nan Babban yaro brolas kajin gidan gona girman dare daya.
Gadan gadan ya nufi wajenta da niyyar damkota amma Amana da sauri ta sauka kasa tace idan yau za a kwashi wani zuwa hospital yazo ya biyoni ya gani, masu rawa da liki suka ci gaba da yi,
Amana tsakaninta Da Allah fada akeyi gagarimi, yanda take jin haushin Alim sosai ba mutunci,shima Alim haushin Amana yakeji baiga ciki jikinta ba,sannan ta wani manta dashi ta kara kibarta da kyau,da aurensa a kanta tana ta yawo inda taga dama.
Alim yaga Amana da gaske takeyi karta kunya tashi a mutane sai ya fasa ya koma ya zauna Amana taci gaba da shagalin bikinta,har aka zo cin abinci inda kowa zai tashi yawa kansa serving abinda yakeso,ana ta karbowa,Amana ta ebowa Aabid,little Zaliha,da Ikkram din Nura,
Komawa tayi zatayi serving kanta fara Eba tayi Alim yazo ya wani faffake wajen,Amana bata kulashi ba ta samu ta matsa, kara faffakewa yayi, lekawa tayi tana dogon wuya zata ebo ta wani cokalo bakin masifa,duk inda ta nufa da niyyar ebowa sai Alim yaje yayi blocking wajen,
Alim haushinta yakeji yanda ake kallonta ana yaba surarta, cokali me yatsu tasa tare da yakuso hannun Alim ai kuwa fatar hanun ta kwarzabe kamar yakushin damusa, ta eba tayi gaba.
Tunawa Alim yayi ai sunyi fada da Amana basa shiri da sauri ya dauke kai ya juya,Itama Amana a hankali tace au jaka ni kamar muna shiri na wani kalleshi,to wanne ma kyau yayi shi din me, me ya hadani dashi tsaki taja ta wuce motarta ta bude tare da sa Aabid a gaba,Aabid ya fito fit yace Momy ga Daddy can motarsa tafi kyau muje a tasa,Aabid ya kwalawa Alim kira Daddy ka jiramu muje a taka,Amana tace to bazan shiga motarsa ba dalla wuce muje,Alim ma yaji me Amana ta fada shima magana yayi da dan daga murya yanda zata jishi ko kinzo ba daukanki zanyi a motata ba,ko kinji nace zan daukeki dama,da masifa Amana tace oho ko kace ma ba shiga zanyi ba ehe,kuma a daina kallona za a cinye min kurwa to tawa daci gareta kurwata kurrrr ta karasa tana huci,.
Alim shi dariya ma ta bashi da birgeshi,kinga na kallekine?baki kyau ba dai,ga masu kyau can sun tafi party,Da masifa Amana ta hayayyako me zasuci da kai ragowar mata,woooo ragowar mata an gama da kai sai ragowa zasu samu,mata nawa ka aura me auri saki,ina fada ma watarana wata sai ta harbeka kowa ya huta,
Dariya ta kusa kwacewa Alim sai ya kara mazewa ya tamke fuska yace haka na gani shi yasa kike bin abokaina kina fada musu su bani hakuri na dawo dake,
Kugu Amana ta rike tace kalleni tsaf na wuce ajinka Malam ai kai na gama da shafinka na jefa a shara masu kwashe shara sunzo sun kwashe ka an zubaka a katon rami.sai yanzu ma nakejin haushi kaina na auri Kazami yan... yan... yan.....tana yatsina fuska ta kara da cewa ko kyau babu,yanzu ma da kasan munin da kayi da baka je dinner ba ta tsaya tare da murguda baki,
Alim dariya fa yake tayi a zuciya ya samu abinda yakeso,da sauri yace wannan kuma karya kikeyi yarinya,kuka ne ya tahowa Amana tayi sauri ta maida shi tare da jan kwafa ta shige mota,Aabid Bai San me sukeyi ba har ya gaji da jira,kowanne ya figi mota ya hau titi suna tafiya idan Alim ya figi mota ya wuce Amana sai Amana ta cisga ta wuceshi itama,
Idan masifa ta ciyosu sai kowa ya danna mugun horn,yanzu Alim zai wuce Amana ya sauke glass kasa ya zo saitinta da mota ya fara mata gwalo,itama kuwa ta tako da karfi ta masa gwalo wullo wai dan ta tura masa haushi da yawa ta dallaro harshenta ta barshi a haka,tana kaga kaga suna hada Ido ta glass tace nafi karfinka baza ka iya Dani ba,na Riga na maka nisa na wuce ajinka,ta ce woooo wulluuuuuu, ta zuge glass tana haki cike da masifa tace nayi maganinsa ai Bai isa na kyaleshi ba,bazai ja Dani ba,
Alim kuwa yana rufe glass ya dinga dariya kamar me har suka karasa wajen dinner.tare suka tsaya Amana da Bala'i ta fito wai irin kar Alim ya rainata.
Alim kuwa ya shirya me zai taokaneta dashi.
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
170-175
Official
By
AsmaBaffa
MARCYCOOL JINJINA GAREKI,
DUK MASU SHARHI WANNAN PAGE NAKUNE,SANNUNKU DA KOKARI INA MATUKAR JIN DADI,KUNA KARA MIN KARFIN GWIWA.
Amana rike da hannun Aabid sauri tayi ta shige wurin da ake event din,wow wuri ya hadu sosai Dinner Baban Ishaq angon Sakina ce yau nasa da ya hada musu aka fara yi,Amare zaune da angwaye sunsha kyau,wurin ya cika da mata da samari dangin Amare da Angwaye,ga kawaye da abokai,wanka iya wanka,mata iya mata maza iya maza a wajen nan ba a magana.
Aabid kuwa da gudu ya tafi wajen Nura da matarsa da yarsu,Amana ana tafiya kwas kwas sai kallonta ake ta faman yi musamman maza,
Ta wuce zata zauna Ashe Alim yana bayanta duk inda tasa kafa sai yasa,sabo da kida bata ji tafiyarsa ba,Amare harda dagowa Amana Hanu suna zaune,Badriyya ta dagawa Alim babban yatsa shima ya daga mata tare da murmushi,Sakina ta masa inkiya da Ido,nan take Alim ya bar kusa da Amana wajen Asiya yaje tana zaune ita da Ahmad yayan Huzaifa ,Alim fuska ba wani walwala ya furta Asiya tashi ki janye min wancen Ku zauna tare,
Dariya Asiya tayi tace yaya Da Alama Allah laifi kayi mata shi yasa kabi ka nacewa mata ka kyaleta ta huta pls,
Zan mareki kije kiyi abinda nace,Ahmad yace kai masifaffe mufa ka ishe mu da wannan matartaka tunda tazo yanzu duk gidan biki gulmarku akeyi iskancinka gaban kowa yi kakeyi Ayu kawai.
Kana surikin nawa? ai an kusa bikinka idan naga dama sai na hanaka kanwata ka rufawa kanka asiri cewar Alim, Asiya kuwa tuni ta cika Umarnin Alim zaune ita da Amana dan auta ma wajensu ya dawo yana fadawa Amana wai ga wata can dan Allah taje ta hadasu ko zata soshi,Amana tace dan yaro dakai to ba Dani ba,dariya sukayi,Alim yana kallonsu yana ta Jin dadi.
Amarya Badriyya da Huzaifa MC ya kira su fito fili ana bukatarsu,Amana ce ta fara mikewa ta shiga fili, Amana bata rawa bata taba yin rawa ba saboda kar a rainata wai hee baya ga haka ma bata iya ba.
Yan Dari Dari ta fara lika musu, cikin takun isa da birgewa sai ga Alim yazo ya fara likawa Amarya da Ango yan Dubu Dubu shima yana liki
Kallon Amana yake yi idonsa na kanta suna hada Ido sai ya maka mata harara itama kafin kace me ta rama harda murguda baki,
mutane ne suka zo yuuuu mata da maza suka lullube wajen kowa liki yakeyi,wani Namiji ya fara likawa Amana kudi sosai,Alim takaici ya kama shi,Amana juyawa tayi ta dinga likawa Saurayin nan kudinta,Alim kamar ya hadiyi zuciya ya sheka lahira,
Kafin kace me ransa yayi bakinkirin,har idonsa ya canja color tsabar bala'in da yakeji,
Yana ta likinsa Bai fasa ba cikin zafin nama ya samu ya shige tsakiyar Amana da saurayi ya musu kerere a tsakiya tare da ci gaba da yiwa Amare likin Naira.
Amana Jin kamshin turaren Alim yasata lumshe Ido nan take ta fada tunanin rayuwarsu sanda suna tare yana nannadeta cikin kirjinsa ta shaki kamshinsa da dumin jikinsa son ranta
Matsowa yayi yanda zata ji shi cikin bacin rai muryarsa har rawa takeyi nace ki fita bana so me kikeyi haka kinawa kato liki for God sake, ko kallonsa Amana batayi ba,cikin karajin da Amana ce kadai zata ji ya furta zan yi maganinki ki bar ganin Ina wasa dake akan wannan bazan miki da sauki ba.
Amana ba walwala ta furta sannu Ubana Sulemanu kai awa?mene hadina da kai ta fada tana Balla masa uwar harara,haka kikace?cewar Alim,Amana ta kalleshi up and down tana fari da Ido tace wacce grass ce kai ko nace wanne weed ne? Wanne ruwan kwatar ne?wacce shara ce?
Me likawa Amana kudi tuni kudinsa suka kare yayi waje kuma yana jin fadan da sukeyi da Alim a ransa yace saurayi kayi asarar budurwa sai dai ka koma wajen Bazawara Amma wannan Budurwar yar dagwas gwas ni zan kwaceta.
Alim da ya tuno me yayi sai ya tuna fada sukeyi ba kishinta yakeyi ba ina ruwansa,
Sai ya canja magana da cewa taimaka miki nakeyi saboda bakiyi kyau ba abin kunyane aga ana miki liki ke baki ga dariya ake miki ba,Amana taci gaba da masifa Alim kake ko wa?ka sakar min mara nayi fitsari pls nace bana yinka kaje ka nemi irinka yanzu nafi karfinka ehe yawwa asakar min mara nayi fitsari,, murmushi Alim ya saki wanda ke kara masa kyau, Amana a ranta tace mijina me kyau, Alim ne ya katse mata tunani da cewa idan naki fa?
Itama ta fara magana kasan ni ai kasan Halina ko na gwada ma? ni da kake gani na ba mutuncine dani ba,ni abin kunya idan ya ganni to guduwa yakeyi saboda uwar gidansa tazo Amana ta furta cikin fushi kamar bata taba dariya ba,Alim yace hmm wanda kikewa ne suke kyaleki yarinya,Amana ta maida martani gaka nan Babban yaro brolas kajin gidan gona girman dare daya.
Gadan gadan ya nufi wajenta da niyyar damkota amma Amana da sauri ta sauka kasa tace idan yau za a kwashi wani zuwa hospital yazo ya biyoni ya gani, masu rawa da liki suka ci gaba da yi,
Amana tsakaninta Da Allah fada akeyi gagarimi, yanda take jin haushin Alim sosai ba mutunci,shima Alim haushin Amana yakeji baiga ciki jikinta ba,sannan ta wani manta dashi ta kara kibarta da kyau,da aurensa a kanta tana ta yawo inda taga dama.
Alim yaga Amana da gaske takeyi karta kunya tashi a mutane sai ya fasa ya koma ya zauna Amana taci gaba da shagalin bikinta,har aka zo cin abinci inda kowa zai tashi yawa kansa serving abinda yakeso,ana ta karbowa,Amana ta ebowa Aabid,little Zaliha,da Ikkram din Nura,
Komawa tayi zatayi serving kanta fara Eba tayi Alim yazo ya wani faffake wajen,Amana bata kulashi ba ta samu ta matsa, kara faffakewa yayi, lekawa tayi tana dogon wuya zata ebo ta wani cokalo bakin masifa,duk inda ta nufa da niyyar ebowa sai Alim yaje yayi blocking wajen,
Alim haushinta yakeji yanda ake kallonta ana yaba surarta, cokali me yatsu tasa tare da yakuso hannun Alim ai kuwa fatar hanun ta kwarzabe kamar yakushin damusa, ta eba tayi gaba.