← Book details Ahalinmu Daya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 90

Sashe 7

Ahalinmu Daya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Lokacin da muka taho a mota kina bacci har muka zo nan ɗin amma da Tunda ga bakin babban gate ɗin shigowa zaki ga sunan a rubuce don ko makaho yashafa zai iya karantawa, yanzu inaso kamar yadda hankalin ki yake a kwance kafin na sanar dake, yanzun ma ki kwantar da hankalin ki, saboda nasamu karɓuwa sosai a gurin mamallakin wannan Estate ɗin sannan da alama shi ɗin mutumin kirki ne duk da baza mu'iya gane hakan ba a yanzu, nidai ina roƙon ki da kibani haɗin kai sosai muyi abunda yakawomu mubar garin nan, sannan nidake ba guri ɗaya zamu zauna ba kowa da inda za'akaishe, naji daɗin hakan saboda zamu rinƙa samun bayanai ta kowane ɓangare, sannan zan samu mana waya wadda zamu rinƙa sanar da mother komai kinga Tunda muka baro Bichi mu bamuyi waya da ita ba, Suhaima takai ƙarshan maganar Indon ta tab da kwalla saboda ta tuna da mother,

Sosai khaltum ke kuka saboda jin maganganun Suhaima, a hankali ta rungume Suhaiman tare da FaÉ—in dan Allah Æ´ar uwata ki yafemin, nayi miki mummunar fahimta har nafaÉ—a miki maganganu marasa daÉ—i abisa rashin sani dan Allah kiyi hak'uri,

Da sauri Suhaima ta goge kwallar dake idon saboda bata son zuciyar ta takaryi, tare da sakin murmushi mai sauti, saitin kunnan khaltum ta furta,
" Laaaa laaa wai kuka kikeye lallai waya gaya miki jarumai suna kuka, bai kamata ba, nafiso ki adana hawayanki har zuwa lokacin da zamuyi nasarar É—aukar fansar mu, kinga lokacin hawaye zasu yi amfani, saboda zamuyi kukan farin ciki babu mai hana mu,

Dariya khaltum tayi tare da Faɗin inason ki sosai Allah yarayamu tare da juna cikin aminci da ƙauna, Suhaima na daɗe ina faɗa miki ke ɗin ta musamman ce a cikin mutane samun kamar ke sai antona duk wanda yake da ƴar uwa irinki to tabbas bazai taɓa kukan rashi a rayuwa ba, insha Allah zamuyi nasara ɗari bisa ɗari,
Sai dai abu É—aya ina jin tsoro"

Hannun Suhaima tasa tare da share hawayen da suka wankewa khaltum fuska, cikin tausasawa Suhaima tace, kada kiji tsoron komai, Allah yana tare da mai gaskiya, nasara tana tare da jajirtattun mutane, idan kikaji tsoro to tabbas zamuyi rashin nasara, wanda bazan bari hakan ya faruba, da yaddar Allah, sannan duk ɓangaran da aka kai ki acikin estate ɗin nan ina tare dake koda yaushe, kikasan ce cikin farin ciki da nutsuwa, idan kika zama mai gaskiya to komai naki zaizo cikin nasara yadda kike so,
Tana kaiwa nan tazare jikin ta daga na khaltum, ta nufi inda kayan abincin nan suke,

Kallon ta khaltum tayi tama kasa magana saboda jikin ta duk yayi sanyi,

Duk da fuskar Suhaima a rufe take amma alamu sun nuna murmushi take yiwa khaltum tare da FaÉ—in malama sakko ki cigaba dacin abincin ki saboda ni rabona da abinci irin haka tun muna asibitin nan tsawan kwana 3,

Maƙale kafaɗa khaltum tayi tamkar ƙaramar Yarin Ya tare da Faɗin A'a nibazan ƙara cin abinci gidan nan ba har mutafi, gidan azzalumai kuma sheɗanu,

Dariya Suhaima tayi sosai saida tayi mai isar ta kafin tace to yanzu idan biki ci abinci na ba ya za ayi kenan haka zaki zauna da yunwa, kuma kin taɓa ganin anyi aiki babu abinci, ainasan halinki khaltum baza ki iya yiniba tare da abinci ba azumi ma dayaya kike yinsa bare kina ganin abincin kiƙi ci ai wannan labari ne,

Itama dariya tayi saboda tasan tafaɗa ne kawai amma bawai don zata iyaba saboda khaltum tana ƙaunar abinci, koda babu daɗi bare ma irin wannan mai rai da lafiya,

____________________
______________
_________

Mai girma Hasheem ne tsaye cikin ɗakin duhu, ɗakin dayake surkullan sa aciki, cikin shigar sa, wadda ya haɗu da Suhaima da ita, hannun sa ruƙe da wannan kwaryar, yana kallon mudubin tsafin sa, wanda wani ke magana ta cikin sa amma ba a iya ganin sa saidai sautin kakkausar muryar sa,

"Hasheem tabbas kana son kawo mana gagarumar matsala acikin aikin mu, wanda baza mu bar hakan ya faru ba, akwai babbar matsala acikin gidan ku, ita wannan Yarin yar da kagani, itace ƙaddarar mu idan har baka kawar da itaba,
To ƙarshan ka yazo domin sai ta tarwatsa komai, gashi tun yanzu kafara Bamu matsala, saboda a yau baka kai sadaukar warka ga Dodo ba, Dole acikin kwanakin nan kakawo HATIMIN MALLAKA, ahalin yanzu Sarauniyar tsafi tana fushi dakai,
"mutumin dake maganar ta cikin mudubin yana kai wa nan wani irin baƙin hayaƙi mai duhu ya mamaye fuskar mudubin, batare dajiran abunda Mai girma Hasheem zai ce ba,

Wani irin nannauyar ajiyar zuciya mai girma Hasheem ya sauke, idanuwan sa sunkaɗa sunyi jawur, kwaryar dake hannun sa ya buɗe, take wani irin mugun ƙarnin jini ya mamaye gurin, jini ne aciki kusan cikin kwaryar, haka ya ɗaga tare da juye jin asaman mudubin tsafin nashi, kamar wanda ake jira haka jinin yafara shiga cikin mudubin sannu ahankali, take yazama kamar ba'a taɓa zuba wani abu asaman shiba, wani abun mamaki ko ɗigo ɗaya bai zuba ƙasa ba,
Saida ya tabbata jinin ya gama shiga ciki sannan ya É—akko wani jan kyalle ya rufe gaba É—aya fuskar mudubin, tare da karantu wasu É—alatsuman tsafi, bai daina karan tasu a har saida ya shige, wannan É—akin dayake janza kayan sa aciki,
Cikin ƙan ƙanin lokaci yafito cikin shigar manyan kaya shadda da hula hadda babbar riga, kamar bashi ba hatta kwalliyar dake fuskar sa babu, haka yafita gaba ɗaya daga cikin gurin wanda ya kasan gidan ƙasa ne, wato ginin cikin ƙasa akayi, wanda baza ka taɓa cewa akwai wani, abu acikin ƙasar ba, abun mamaki yana fitowa gurin ya shafe gaba ɗaya,

Wayar sa ya ciro yakira Mahaifiya su, mama bilki, bugu É—aya ta É—auka babu ko sallama yace mata,
Mama inaso mu zauna yanzu yanzu,

Abunka da shashashar uwa batare da musu ba tace to ina ɓangaran mahaifin ku amma ganinan zuwa ka sameni a babban parlour na,

Batare daya ce komai ba ya katse wayar, sannan ya dannawa He Excellency Sambo Call, saida ta tsinke ya sake kira akaro na uku aka É—aga, kana inane?

Amsawa He Excellency Sambo yayi da, lafiya dai ko,

Eh lafiya ba lafiya ba inaso mu haÉ—u a babban parlourn Mama zaman gaggawa ne kakira, Mansur yazo shima, nimakuma zankira, Sulaiman,

Oky abunda He Excellency Sambo yace kenan, saboda kar ayi bashi da bazai jeba haka ya tashi cikin sauri ya zura jallabiya tare da kiran uncle Mansur, ya sanar masa kamar yadda, Mai girma Hasheem ɗin ya buƙata,

Uncle Mansur kamar me jira yariga kowa halartar parlourn Mahaifiyar tasu.!!!

*_F Pen's_*
[01/04, 3:10 pm] Zarah Tymre's Henna: _Typing📲_

What's app channel👇

https://whatsapp.com/channel/0029Van1Keq59Pwb6CDnwe0V

WhatsApp group👇

https://chat.whatsapp.com/C9sZ6UCsGEHKSALn3SYSqs

*_AHALIN MU ÆŠAYA_*

💗💗💗

_CREATED AND WRITTEN_
_BY_

*_Fatima Y zakariyya👌_*
_Tymer's henna_💅

*Nazari writer's ass......📚*

_Sarauniyar👸 Nazari writer's✍️_
*_(THE QUEEN👑)_*

________Dedicated to anty salma💎

*_Part 2_*
(Littafi na biyu📘)

_Godiya ta musamman gareku ɗaukacin masoya na ina matuƙar yaba muku, alkhaerin Allah yakaimu ku a duk inda kuke.🤗😘😘_

*Da sunan Allah mai rahma mai jin kai*

*_in the name of Allah, the Entirely Merciful, the Especially Merciful_*

➡️🅿�1�1⃣➖1�2⃣�

Uncle Mansur kamar me jira ya riga kowa zuwa parlourn mahaifiyar tasu saboda kada yayi asarar kalma É—aya daza a faÉ—a ta wuceshi,

Cikin minti nan daba zasu haura biyu ba, saiga, mai girma Hasheem, atare suka shiga, shida He Excellency Sambo, ko zama basu yi ba saiga mama bilki cikin sauri,

Barrister Sulaiman ne ƙarshan halarta a parlon,

Gaba É—aya suka tattara hankalin su gurin Mai girma Hasheem ganin bashida niyar yin magana ne,

Hakan yasa mama bilki Faɗin, "Hasheem kaifa muke sauraro katara mu anan sannan kayi shiru ga dare yana ƙara yi,

Saida ya numfasa kafin ya kalle su É—aya bayan É—aya, yafara magana,
" Akwai Gagarumar matsala, duka kunyi shiru kwana biyu babu wani bayani ta kowa ne ɓangare, ina so kusani akwai Yarin yar da take cikin estate ɗin nan, kusanar dani idan ɗaya daga cikin ku yasan zuwan ta sannan kuma a wane ɓangare take zaune,

Cike da mamaki suka kai duban su gaba É—aya kan Mai girma Hasheem, kafin kowa yace komai mama Bilki tace, wacece ita sannan kai waya faÉ—a maka? Ta jefa masa tambayar idon ta akan shi,

Ba faɗa min akayi ba gani nayi zahiri da idona a daran nan, acikin ƙarshan estate ɗin nan, wani abun mamaki ma, A inda babu house ko ɗaya cikin gurin nan mai kama da daji, gashi fuskar ta a rufe, dagani annuba ce ita a gurin mu,

Gaskiya ni banji labarin zuwan wata Yarin yaba ina tunanin idon kane kawai yake maka gizo, ko kuma aljanu sun buɗe maka ido, don da ace ankawo wata baƙuwar fuska to dole zansani koda ba a ɓangaran ɗaya daga cikin ku zatayi aiki ba,

Amma mama bakya ganin mu fara bincika wa kafin mu yanke hukunci, kada muzu lokaci ya ƙure mana fa, cewar He Excellency Sambo,

A ɗan harzuƙe Uncle Mansur yace Gaskiya kunɓatamin lokaci ninayi zaton wata kwakkwarar magana ce ashe shirme ne, ta yaya za a kawo Yarin Ya cikin gidan nan batare da sanin mu ba, kawai kafita cikin dare ba dole kayi gamo ba,

Ya isa kowa ya tashi Yabani gurin zuwa gobe zan bincika don samun tabbacin maganar, cewar mama Bilki,

Ina da magana barrister Sulaiman ne yayi maganar hankalin sa na akan wayar hannun sa,
Gaba É—aya hankalin su ya koma zuwa gare shi, alamar shi suke saurare,

Kashe wayar yayi tare da gyara zaman sa, Dama Magana ne Akan HATIMIN Mallaka, ina da cikakkyan bayani akan tabbas yana hannun Sulaim Arab, sannan bai ajiye shi acikin gidan nan ba, saboda mun bincika, abu na gaba da nagano shine tabbas idan har baya cikin gidan nan to, yana Hospital É—in sa, don babu inda ya É—auka da mahimmanci kamar can kuma yana da babban gurin ajiyar sirri acikin office É—in nasa,
Hhmm, wata doguwar ajiyar zuciya ya sauke sannan yaÉ—ora da FaÉ—in, saidai abu É—aya shine bamu san inane ma ajin sirrin nasa ba,
Yakai ƙarshan maganar idon sa akan iyayen nasa,
Chapter 7 · 0% Book details