← Book details Ahalinmu Daya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 90

Sashe 48

Ahalinmu Daya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wani irin doguwar ajiyar zuciya gimbiya shaheedah tayi kafin tace,
" mom kina son taso da abunda ya kwanta acikin zuciya ta pls kibar ni haka inason zan huta yanzu sannan zanyi tunani kan maganar auran Yarima safwan, kome kenan zamuyi magana amma pls kiyi takatsantsan saboda haryanzu aƙarƙashin kulawar, mai martaba sarki kuke,
Ina meƙa gaisuwa zuwa ga ɗan uwa na ina fatan zaki sanar masa idan na tashi zanne me shi awaya
Batare da jiran Cewar Mom ba Takashe Kiran "Ɗiff" tare da miƙewa ta nufi Bedroom ɗin ta,

_TAƘAI TACCAN TARIHIN MASARAUTAR GABAS_👌

*_Waye sarkin Yusuf shareef???_*

Masarauta ce mai tsohon tarihi sarautar Zaki, mutanan yankin, shuwa Arab asalin su ƴan yankin ƙasar Larabawan Africa ta kudu, wanda suke, kasuwanci, da auratayya tsakanin mutanan arewa hakan yajawo yawan su cikin garuruwan Nigeria bama kamar garin Maiduguri yankin barno State,

Mai martaba sarki shareef zaki, shine sarki a wancan lokacin kafin zamanin, sarki adam shareef zaki, wanda asalin sunan sa ba shareef bane,
Kasan cewar su gadon shareefai shiyasa suke amfani da shareef asalin kakan su kenan, ZAKI kuma shine tambarin MASARAUTAR saboda ƙarfin mulkin da take dashi ga arziƙi da izza, bayan rasuwar sarki shareef zaki, mulki ake gudanar wa mai cike da adalci da tsafta duk wani wanda ke ƙarƙashin sarki adam shareef zaki baƙar ramin daɗi yake jiba saboda adalcin sa da son al'ummar dake rayuwa aƙarƙashin mulkin sa,
Allah ya azurta shi da Æ´aÆ´a guda biyar 5 huÉ—u maza mace É—aya , Yusuf, Murtala, Mahaifiyar su É—aya, Abdullahi, Kabir, Mahaifiyar su suma É—aya, Sai Aziza wadda ita kaÉ—ai ce a gurin Mahaifiyar ta kuma tarasu, itace matar sarki Adam ta biyu 2

Ƴaƴan sun tashi cikin rashin jituwa tsakanin su babu wata kwakkwarar shaƙuwa tsakanin su Aziza sai ta tashi a ɗakin Hajiya Baitu, saboda matsalar iyayen su mata basu da haɗin kai ga kishin jaraba, ko wacce tana nuna tafin ɗaya saboda duka auran gida ne Ƴaƴan sarauta ne,
Mahaifiyar su Yusuf, Murtala, itace uwar gida, wadda suke kira da Hajiya Baitu, bata ɗaukar raini akwai son mulki ga isa da nuna iko, tana matuƙar ƙaunar Ƴaƴan ta sosai, ita ta aurar da aziza saboda hannun ta tayi rayuwa tun tana ƙarama maman ta tarasu, tasamu gata sosai daga gurin Hajiya baitu,

Kowa cikin mazan burin sa yaga yazama shine magajin karagar, sarki Adam, banda mutum É—aya Yusuf babu ruwan sa da mulki hasalima shi ba mazauni bane kuma shine É—an fari a gurin sarki adam, Æ´an uwansa ne kaÉ—ai suke bidirin su,

Mahaifiyar, Abdullahi, Kabir, itace matarshi ta uku ta ƙarshe kuma wadda suke kira da Giwar sarki, tunkafin a haifi aziza sarki adam ya aure ta, saida ta yi haihuwar fari wanda ɗan ta na farko Abdullahi, kafin Mahaifiyar aziza itama ta haihu bayan haihuwar tata ba jimawa Allah yayi mata rasuwa,

Sosai sarki yaji mutuwar ta saboda yana so ta sakamakon tana da hak'uri ga kyau da kai baruwan ta da kowa bata da wani abokin faɗa, hakan yaja mata soyayyar mutanen gidan dayawa, wanda hakan baƙaramin ciwo yake yiwa, Hajiya baitu ba, amma da ta mutu saida jikin ta yayi sanyi sosai itama taji babu daɗi duk da ada bata sonta,
Hakan ne ma yasa ta ɗauki ƴar ta aziza tamkar ita tahaife ta cike da so da ƙauna da bata kulawa tamkar yadda Mahaifiyar ta zata yi mata bata bari aziza tayi kukan maraici ba, saboda ita tamayi zaton Hajiya baitu ce Mahaifiyar ta, saida Giwar sarki ta taɓa goran ta mata sannan tasan ba ita tahaife taba, ahaka babu abunda ya canza,

Rayuwar su na tafi cike da rikice-rikice, kowa da abunda ke zuciyar sa burin kowa acikin su yaga shine asama É—aya,

Wata rana kwatsam Yusuf ya dawo daga ƙasar Mali, bayan ya hallaci ɗaurin auran abokin sa da sukai karatu tare, kai tsaye ya wuce fada gurin mai martaba sarki, ya sanar masa da magana yazo kuma mai girma,
Mai martaba yabada umarnin ya shiga har tura kar sa domin suyi maganar, hakan kuwa akayi, cike da girmamawa Yusuf ya gaida mai martaba sarki adam,
Gani Yusuf É—in yayi shiru hakan yasa sarki faÉ—in inajin ka, zaka iya gabatar da komeye a zuciyar ka,

Ranka ya daɗe ina neman gafara da kuma afuwa tuba nake bisa babban laifin dana aikata a gare ku batare da shawarar ku ba Allah yasanya nutsuwa da haƙuri a zuciyar mahaifi na,

Sosai sarki ya kalli É—an nasa Yusuf, Allah yagafar ta mana baki É—aya, inajin ka yusufa jeka kai tsaye kan maganar ka, Allah shine mafi sannin dai dai, sannan shine sarkin dabaya kuskure mai yafiya a koda yaushe ga wanda yayi laifi kuma ya tuba tsarki ya tabbata a gareshi,

Cike dajin daɗin furicin mahaifin nasu Yusuf yace, Allah ya ƙara maka yawan nasara, Yusuf yana tare da Iyali, ya furta hakan tare da ƙara yin ƙasa da kansa sosai cikin jin nauyi da kunya da kuma tsoron abunda zai biyo baya,

Ɗan muskutawa mai martaba yayi cikin son jin ƙarin bayani abunda ɗan nasa yazo dashi, ganin alamar hakan ne yasa Yusuf ƙara gyara zama sosai ya cigaba da Faɗin,
Ranka ya daɗe, anɗaura min aure safiyar jiya, a ƙasar Mali,
Allah ya sanya hak'uri acikin zuciyar mahaifi na, ni mai laifi ne, na shirya ko ban shirya ba dole na karɓi hukunci, amma ina neman afuwa da kuma yafiya a gurin sarki mai adalci tuba nake, yana kaiwa nan yayi shiru,

Sosai sarki Adam shareef ya girgiza dajin lamarin auran da Yusuf ɗin yace yayi, yasan ɗan nasa ko maganar aure baya so ayi masa bari har ace ga mata, mahaifiyar sa Hajiya baitu tasha nuna masa ƴan mata kala kala ƴaƴan manya da sarakuna wasu matan ma suke kawo kansu, amma bai taɓa kulawa ba saidai ma ransa yaɓaci,

Saida sarki ya gama nazarin Yusuf É—in kafin yace,
Yusufa ai duk abunda kaga ya faru to dole Allah ya riga ya tsarawa bawa tunkafin wanzuwar ransa a duniya, bazai ce naji daÉ—in auran da kayi batare da sanin muba ba, sannan bazance banji daÉ—i ba saboda ai dama abunda nadaÉ—e inaso kayi kenan, kaine babba amma Æ´an uwanka biyu, sunyi aure, to Alhamdulillah,
Allah yasa albarka Allah yasa kubiyun alkhairan juna ne,

Da mamaki Yusuf yaɗago kaɗan ya kalli mahaifin nasa abunda bai yiba tunza mansa, sosai yayi mamakin jin furucin, da sarki yayi take zuciyar sa ta mamaye da wani irin farin ciki, dama babbar damuwar da shine mai martaba idan ya amince to duk wani abayansa yake hatta ita Hajiya Baitu wadda itama yana fargabar abunda zai fito daga ɓangaran ta gashi matar da ya auro ɗin ba ƴar kowa bace hasalima ƴan gudun Hijira ne to tabbas akwai matsala idan Hajiya Baitu taji haka don bata son talaka ta tsani hada inuwa da wanda ba kowa bane,

Cigaba da magana mai martaba yayi, "zamu zauna da Mahaifiyar ka insha Allah, sannan akwai hukunci akan ka na karya dokar masarauta wanda sanin kankane bane zanyanke wannan hukuncin ba, Alƙalan Fada suke da wannan alhaƙin,
Yanzu ina ka ajiye ita iyalin naka sannan Æ´ar waye?? Sarki yayi masa tambayar a jere,

Ranka ya daɗe tana sa shen kilishi Aziza, sunan ta Bahijjah, sannan ba ƴar kowa bace, Mahaifin ta Allah yayi masa rasuwa, sakamakon faɗan ƙabilanci da akayi a nahiyar su, Yanzu ita da Mahaifiyar tane suna aiki, a gidan su abokina wanda naje ɗaurin auran sa Mali,
Da fari nayi niyar tahowa da su daga bayan idan kun amince sun ƴan tu daga wahala, sai a ɗaura mana aure, to bisa al'adar garin mutum ɓako baya tafiya da ɗan garin kowa wanda ke zaune a garin, sai dai idan auran ta mutum zaiyi shine zai iya tafiya da ita, ganin irin halin da suke ciki ne na tausaya musu sosai shiyasa na amince a ɗaura auran sai mu taho tare, yakai ƙarshen maganar cike girmama da nutsuwa,

Zaka iya tafiya, sarki ya faɗa a taƙaice,

Russuna wa yayi sosai tare da Faɗin Allah yasa mai martaba bazai yi fushi dani ba domin hakan zai cutar da ni matuƙar cutarwa nabar ku lafiya, ya tashi jiki a saɓule babu kwari, saboda baya son ganin fushin iyayan nasa Sam, Faransa yana ayyana yashirya karɓar duk wani hukunci daga Alƙalan fada, hakan baidameshi ba, amma dai kome za ayi bazai iya ra buwa da matar saba wadda ganin farko yakamu da tsananin son ta, daga shekaran jiya zuwa Yau amma ji yake idan akarabasu tabbas ƙarshan rayuwar sa yazo,

Mai martaba yabi bayan ɗan nasa da kallon sannan yayi wani irin murmushin girma, harcikin ransa yana ƙaunar Yusuf sosai, kaf cikin ƴaƴan sa idan aka cire Aziza itama saboda ba Mahaifiyar tane,
Yasan Yusuf akwai gaskiya gashi da amana bashida son zuciya kamar ƴan uwan sa shiyasa afi shiga ransa sama da kowa acikin su, dole yasan Alƙalan Fada zasu yi hukunci amma dole zai nema wa ɗan nasa sassauci kan a rangwan tamasa.!!!

*_F pen's_*✍️
[01/04, 3:10 pm] Zarah Tymre's Henna: _Typing📲_

What's app channel👇

https://whatsapp.com/channel/0029Van1Keq59Pwb6CDnwe0V

WhatsApp group👇

https://chat.whatsapp.com/C9sZ6UCsGEHKSALn3SYSqs

*_AHALIN MU ÆŠAYA_*

💗💗💗

_CREATED AND WRITTEN_
_BY_

*_Fatima Y zakariyya👌_*
_😍Oum Ameerah_😍

*Nazari writer's ass......📚*

_Sarauniyar👸 Nazari writer's✍️_
*_(THE QUEEN👑)_*

________Dedicated to anty salma💎

*_Part 2_*
(Littafi na biyu📘)

*_Ina mai farin cikin sake haɗuwa daku a cikin Littafin AHALIN MU ƊAYA. Kashi na biyu, ina roƙon Allah ya amfanar da mu abin da ke cikin sa, akasin haka kuma da kuskure na ku watsar dashi gefe, saboda nima mutum ce kamar kowa zanyi dai dai zanyi kuskure, domin ɗan Adam ajizi ne, Allah ya shiga dukkan lamuran mu yayi mana jagoran ci_*

_Godiya ta musamman gareku ɗaukacin masoya na ina matuƙar yaba muku🤗😘😘_

*Da sunan Allah mai rahma mai jin kai*

*_in the name of Allah, the Entirely Merciful, the Especially Merciful_*

➡️🅿� 5️⃣�6️⃣📖

Kamar yadda Yusuf yayi tsammani hakan ne ya faru saboda Hajiya Baitu, ta buga ƙasa tayi tsalle tace ita sam sam bazata yadda da wannan auran ba, sai Yusuf yasaki matar sa Bahijjah,
Sosai mai martaba ya fahimtar da ita kan ta kwantar da hankalin ta amma tace ina ita fa bazata yadda da wannan ba, sai dai Yusuf yazaɓa ko ita ko matar shi,
Chapter 48 · 0% Book details