← Book details Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 61

Sashe 59

Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wasannin su suke ta yi a palourn su kamar wasu ƙananan yara, irin wannan rayuwar Umar da Saudat ke buri a rayuwar su sai gashi sun samu abokan cika burin nasu,qafar saudat ce ta tafi gaba sai ta yi kamar za ta faɗi, da sauri Farouq ya isa gaban ta ya riqe ta ya na tambayar ta lafiya take dai bata ji ciwo ba ko ? Ganin yanda ya rikice ne ya sanya saudat murmusa wa ta kama fuskar shi a tafukan hannayen ta ta na kallon k'waryar idanun shi daga baya ta lumshe Idon ta a hankali ta sumbace shi.

Lumshe nashi idanun ya yi kafin daga baya ta janye cikin murya mai taushi ta ce,

"Me ma ka ke tambaya ta d'azu?"

Murmushi ya yi ya sauke idanun sa qasa sannan ya sake kallon ta cikin sarqewar magana ya ce,

"Amm...nace...ammm.."

Dariya suka sanya baki ɗayan su kafin Umar ya ce,

"Ina son ki mata ta"

"Ni ma ina son ka miji na fiye da yanda ka ke so na"

Nan da nan ya shagwab'e mata ya na buga ƙafa irin yanda take yi masa ya ce,

"Ah ahhhh ni dai na fi son ki"

Itama ta shagwab'e fuska ta ce,

"Ban yarda ba ni ce na fi son ka"

Dariya suka saka sosai har tana riqe ciki, d'aga ta ya yi ta bayan ta suka samu wajen zama a kujerun nasu, bayan ya kwantar da ita a kujerar ne ya kwanta ta bayan ta Shima ya rungumo ta ta ciki ta,suna ci gaba da hirar su, a hankali suka yi shiru yana mata wasa da gashin ta ta ce,

" Babe me yasa baka damuwa da batun rashin haihuwar da kasan ba zan yi ba, bayan kasan babu mahaifa a jiki na? Kuma kai baka taɓa yin aure ba, ko dai ka na da qudirin qara aure ne a nan gaba?"

Murmushi ya yi mai sauti ya sake rungume ta a jikin shi cikin kulawa da tausayawa ya ce,

" My dear ina so ki san cewa da auren da haihuwar duk nufin Allah ne, tayu a baki da mahaifan mu haihu saboda Allah shi ya san yanda yake yi ya azurta bawan sa mu namu hasashe ne da k'ayyade sai muna da kaza sannan kaza zai iya faruwa,sannan ta yu ba za mu haihun ba, to ina son ki sani, haihuwa is a blessing that everyone will love to have, amma ni bana daga cikin waɗanda suke ganin in mace bata haihuwa bata da amfani a wajen su,to ina soyayyar da ake yi mata? Dama dan Yara kawai aka aure ta? Ita ce take bawa kan ta? Idan zan maki kishiya saboda baki haihuwa tabbas na zama daga cikin azzalumai, na kuma zama daga cikin masu butulci ga Allah, domin ya min kyaututtuka mara iyaka da ba zan iya qirga su ba, to me zai sa dan akan abu ɗaya dana ke so ban samu ba na yi mai butulci? Ba zai yu ba, daga ranar da kika ji na qara aure ki tabbata na qara ne kawai dan ra'ayin kai na ko kuma ina son matar ne ya sa na aure ta Saudat, ba zan qara aure wai dan baki haihuwa,dan haka ki kwantar da hankalin ki ni ba mai ra'ayin tara mata bane bama, bana son hayaniya, ban son takura, mata da yawa na saka ni damuwa dan bana son raba fada kullum,"

Maganganun shi ba k'aramin kwanciyar hankali suka saukar wa da Saudat ba,har sai da hawayen farin ciki suka dinga fita daga idanun ta, tabbas Allah ya azurta ta da namiji ɗan gaske, Allah ya qara masa hakuri da juriya akan hakan ta ayyana a ranta.

Ci gaba da shafa wuyan ta zuwa bayan ta ya yi da sigar lallashi,a haka bacci mai daɗi ya ɗauke su.

*****************************

"Ki taho da fidar yaran nan da tissue love"

Salma amsawa ta yi shi kuma Ibraheem ya zauna yana masu wasa, bayan ta iso ne ta zauna kusa da su ta miqa masa abinda ya ce ta kai, cikin tura baki irin na shagwab'ar nan Salma ta ce,

" Ni dai gaskiya ban yarda ba nima sai an min wajen zama a nan, dan wayo kullum ni a qasa ko gefe zan zauna su kuma a cinyar ka?"

Driya ce ta kama Ibraheem, sai ya dauki Hassana ya ɗora a wuya, sannan ya d'ago Salman ya saka a cinyar shi ta na facing ɗin Hussaina,murna ta hau yi tare da sumbatar kuncin shi ta ce,

" Na goooode na zaci ai ce min za a yi na yi hakuri yaran su zauna na yi girma kamar yanda ka saba,da kuwa yau ba zan yarda ba sai dai a maida su d'aki ni na hau"

Ta ƙarasa maganar ta tana sauka daga cinyar tashi, dariya yake sosai dan ya kula da Salma ta na kishi da yanda yake share ta idan ya na tare da yaran, gani take yi gaba ɗaya ya kwashe soyayyar ta ya basu dika, lokacin shi gaba ɗaya nasu ne in yana gida, amma a qasan ranta ba qaramin daɗi take ji ba saboda yanda yake son yaran kamar nashi, hankalin ta a kwance yake dan bata tsammaci hakan a wajen saurayi da bai taɓa aure ba kuma gidan su babu qananan yara balle ta ce ya iya reno.

A cikin kujerar basu abinci ya saka su,ya ɗorawa kowa nata abincin a gaban ta, sannan ya damqa masu cokulan su a hannun su na dama,da kyar suke riqewa saboda rashin iya hakan, yana tsaye a kan su in ya ga zasu karkace ya gyra masu, ta baya ta ziro hannun ta ta tsugunna itama ta kwantar da kanta a bayan shi ta furta,

"I love u"

Shima waiwayar da kan shi ya yi suka hada ido yace mata,

" I love u more my wife"

Tare da sumbatar goshin ta ya juya ga yaran su suma ya yi musu,Salma ta tura baki ta ce,

"Na hakura ni dai na saddaqar an fi son su akai na, ba za a taɓa yi min abu ba sai an yi musu suma"

Dariya ya yi kawai dan ya san idan zai biye mata haka za su kwana ta na masa qorafi.

Jama'a ina so mu gane cewa shi d'a na kowa ne, baka san wa zai more shi ba,shi yasa bahaushe ke cewa da d'a da dukiya ba a yi masu mugunta, in ka lalata su wataqila kai ka lalata wa goben ka da al'umma, idan kuma ka kyautata musu wataqila su amfane ka a gaba ko su amfani al'umma, wani sai ya gama tarbiyyar yaron ya girma saura qiris ya fara morar shi sai ya rasu ya bar wa duniya ta mora,wani kuma sai ya lalata tarbiyyar sai ya mutu ya bar wa duniya mugun iri ko rayuwar shi ta yi tsaho ai ta shan wahalar da shi,wanda ya kyautata ya na da lada mai yawa a wajen Allah, wanda kuma ya munana shi ma ya na da zunubi a wajen Allah .

*****************************

Talle ne ya shirya tsaf da yar jaka a hannun shi wadda ta qunshi kayan yara mace da namiji dan bai san me Salma ta haifa ba, ko ma dai me ta haifa zai kai mata kayan ya fi ya je hannun shi na dukan cinyar shi,sallama suke yi da Marka wadda can cikin qasan ranta kishi ne danqare,sai ta danne kishin nata saboda yanzu ta waye ba duhun qauyanci da mummunan jahilci a tattare da ita, miqa masa leda ta yi wadda ta daka kuka,daddawa, da kub'ewa, tace ya kai wa Salame, godiya ya yi mata,Huwaila ma shiga sashen nasu da qullin ledar gyada soyayyiya itama ta bashi, dan sana'ar ta kenan a yanzu, tace ya gaida su ya nema masu gafar ta, amsa ya yi ya fita bakin shi ɗauke da addu'ar fita daga gida........

*To masu karatu Talle fa ya yi shirin zuwa Ta dabo,kun dai ga ya koma islamiyya har da addu'ar fita daga gida...*
[04/08, 11:01 am] asiyahabibu93: 💅🏻 'YAN ABUJA 💅🏻

WRITTEN BY HAERMEEBRAEH

PAGE : 35

https://chat.whatsapp.com/I8ImAD44ZKU2x8N4dbCpDr
https://Wa.me/+2348036802447
*INA AMARYA INA UWAR GIDA HARDA MAI JOGO DA KE MAI SHIRIN ZAMA AMARYA MUNYI MAKU TANADIN KAYAN DA ZASU GYARA KU TSAB TSAB KIFITO DAGWAS DAKE KAMAR KE KIKA KERA KAN KI SANNAN KADA KU MANTA MUNA HADA JEGO PACKAGE BRADAL PACKAGE & SLIMMING PACKAGE WEIGGHT GAIN PACKAGE GA KUMA ANTI AGAIN PACKAGE SUPER WHITENING CAMBO BREAS AND HIPS PACKAGE GLOWING SET SKIN REPAIR ND REJUVENATIG PACKAGE BEAUTY START FRM WITHIN TAKE CARE OF THE*💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼

💅🏼 'YAN ABUJA 💅🏼

WRITTEN BY HAERMEEBRAERH

Page 35:

Ammar ne zaune a tsakar gida ya na wasa irin na yara, ƙasa ce yake kwab'a wa da ruwa a buta,tare da rero karatun da Mama Balki ke koya masa,daga ya yi na qur'ani sai ya saki ya kama na boko,ya na nan zaune ya ji ana buga kofa tare da yin sallama,tashi ya yi ya nufi k'ofar gidan da gudu tare da yin wurgi da karan hannun shi da yake juya tuwon qasar shi,ya na zuwa ya d'aga kan shi sama ya na kallon mai yi masu sallama.

Murmushi Talle ya yi da ya ga yaron nan take ya hango kamannin da ke tsakanin Salame da yaron, a hankali ya durqusa dai-dai tsahon Ammar ɗin sannan ya ce,

" Yaro ina malam,"

" Faya nan" ( Baya nan),

Talle ne yaga yaron ya kalli gaban shi yana dariya daga baya kuma ya fita da gudu yana fad'in

" Babana Oyoyo"

Wajen da Ammar ya nufa Talle ya bi da kallo,idanun shi ya sauka cikin na Baban su Salame,da saurin shi ya isa gaban Baba ya durqusa, gane wanene a gaban shi ne ya sanya Baba ya sauya fuska daga fara'a zuwa bacin rai, a hasale ya ce wa Talle,

"Me ya kawo ka k'ofar gida na a yau?"

Cikin sunkuyar da kai cike da tarin nadama Talle ya ce,
Chapter 59 · 0% Book details