Sashe 28
Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata gama rufe baki ba ya saki fitsari a wajen da yake tsaye fitsari kuwa ya sauka qasan qafafun shi ya gangara yatafi har qofar ta da aka lailaye da tiles,nan da nan ta hasalo kamar wadda aka watsa wa ruwan zafi, ta miqe ta fita kafin ta isa wajen shi kamar ya san wajen shi za ta je ya fara qoqarin tafiya yana kuka, da alama ba iya fitsarin zai yi ba ma, daidai nan ne Mama Balki ta fito daga d'akin ta ta na miqa tare da salatin Annabi,Sallama Baba Baballiya ya yi ya na Kiran Sunan Ammar da ya gani ya na tafe ya na koke koken yaran da ke buqatar wani abin.
Kafin kowa ya ankara ko ya ce wani abun Goggo ta saka hannun ta ta wanke Ammar da wani lafiyayyen marin da ko Mama Balki akai wa sai jikin ta ya gaya mata,
"Bar ganin wannan kinibabbun iyayen naka masu son abun duniya da har suke ganin D'a namiji ya fi 'Ya mace daraja ba zai hanani cin uban ka ba, in banda baqin ciki da aka koyawa yaro qarami tin yana ciki, duba fa ku ga yanda ya tsanyaran mini fitsari a qofata ya yi gaba, to ba zan lamunta ba,haka kawai ina zaune 'Ya'Yana mata da aka tsana Allah ya ɗaukaka su sun zama wani abu a rayuwa har sun gyara wa uwar su wajen zama a zo kuma a koya wa yaro qarami mugunta ya lalata min waje,"
Tsabar Ammar ya gigice sai ya kasa kukan ma sai neman inda zai je yake garin haka har kashin da yake ji ya biyo bayan fitsarin da ya yi,zuciyar Mama Bilki tafasa kawai take da b'acin rai,tin da Baba Baballiya yake da ita bai taɓa ganin irin wannan bacin ran nata ba, ita kanta Goggo Sarai ta tsorata da ganin fuskar Mama Balki, wandon Ammar Mama Bilki ta cire ta wurga a jikin qofar da aka canja wa Goggo Sarai, qofa ce irin ta qarfen nan mai kauri milk color,sannan ta aje Ammar din ta isa jikin qofar ta samu wandon ta goga sosai har labulayen, sannan ta dawo ta d'aga hannu zata wanka mata mari, sai ta tsaya bata maretan ba , ta kafe ta da wani irin kallon da ke huda gabobin jiki da tsoka ta na nuna ta da yatsan ta manuni alamar gargad'i.
Ko me ta tuna ta tsaya bata mare ta ba oho, sai kawai ta duba ta dauki Ammar da ke ta kuka yaqi yin shiru ta je ta fara gyara shi ta bashi ruwa da abincin shi ya sha ya yi bacci,sai da ta gama kula da yaron ta tsaff sannan taje ta dauke wandon nashi ta wanke ta shanya ta hau kiciniyar ɗora girki,wata irin wuta aka ɗauke a gidan gaba daya, kaff cikin gidan har Baba Baballiya ba mai iya cewa komai, Goggo Sarai na tsoron tace kanzil yanda Mama Bilki ta b'ata rai bata san me zai je ya zo ba, ita kuma Mama Bilki ta fasa marin ta ne ganin datajar Baba Baballiya dake bayan ta, shi kuma ya fuskanci hakan, sannan ya yi shiru ne saboda kar ya bata damar magana ya san kuka zata yi dan zuciyar ta cike take da baqin ciki, sai da ya tabbatar ta fara sauka tinda gashi ta ci gaba da 'yan aikace2n tsakar gida sannan ya samu waje a tsakar gidan ya zauna ya cewa Goggo Sarai,
"Yau kin ban mamaki Sarai ba kaɗan ba, ki duba ki ga abinda kika aikata, yanzu marin da kika yi wa yaron nan ko ni ki kaiwa ai sai na ji shi a jikina ba shi ba ma, dubi yanda yatsunki suka kwanta a kan fuskar shi kamar qunar wuta, haba dan Allah, kin kyauta kenan, baki taɓa ganin fushin Bilkisu a kaf rayuwar ku ba irin haka ko kin taɓa gani? to ina mai tabbatar maki ki kiyayi sakata a irin fushin nan bana kusa, dan duk abinda ta aiwatar akan ki ke kika jawo wa kan ki da kan ki tunda baki iya riqe girman da Allah ya baki ba,a iya yau dai ai kin ga misalin abinda zata iya aikata wa ko?"
Sai a sannan ne Goggo Sarai ta samu bakin magana,
" Eh tinda kun haifi ɗan gwal, dole mana ku fifita shi akan komai, to da dan da uwar na san meye matsalar ku ba komai ke damun ku ba face baqin ciki, kuma nan gani nan bari dumamen mayya in dai nice ni da 'Ya'yana yan albarka mun fi ƙarfin ku"
Cikin Fushi ta juya ta tafi fuuuu ta hau cire labulayen dika d'akin ta watso su tsakar gida ta dauki ɗaya a ciki ta goge qofar dakin da ya ɓaci da kashin Ammar da shi, ta saka ruwa ta wanke, ta qara gogewa da labulayen masu kyau din,duk kyau da tsadar labulayen haka ta saka hijab din ta ta fita waje ta watsar ta dawo, tana wani isa da taqama taje ta canja wasu,ta buga shewa da gud'a ta ce,
" Ahayyyeeeeee ayyuuuuririiiiii, to bari ku ji sau goma wannan shegen tsinannen yaron zai b'atan qofa sau go......."
Goggo sarai bata samu damar ida fad'in me take so ba ta ji qummmmmm a bakin ta, Mama Balki ce da ta hasala dan jin ana tsinewa ɗan ta ta saita bakin Goggo Sarai da ludayin da take juya miya ji ka ke kwalll ya daki fuskar ta, ihu Goggo Sarai ta saka ta na zagin Mama Balki, ita kuwa kamar ba ita ta aikata hakan ba ta je ta durqusa ta dauki ludayin ta ta juya ta ci gaba da aikin ta.
Mai Baba Baballiya zai yi da ya wuce, cikin dariya ya ce,
" Kai amma Gimbiya yau kam sai dai ace na zama munafukin mata, amma kin burgeni, ke kuma ɗan da kk kira shege, duniya ta san ni ne uban shi, sannan, tsinanne da kika kira min d'a ba za ki ga tsinewa a 'ya'yana ba inshaa Allah ina mai musu addu'a komai abinki Allah zai karen su, sai dai kiga tsinewar a kan kan ki dan ba yau na fara jin kin kira min D'a da wannann sunan ba, ke yanzu ba abin kunya bane ace ki na faɗa akan qaramin yaro har irin haka na shiga tsakanin ku ke da abokiyar zaman ki? To ina qara gargadin ki ki kiyayi randa bana gida ki taba wannan baiwar Allah ina tausaya maki "
Ya qarasa maganar cikin dariya ya fita qofar gida, duk abinnan da ake Mama bata ce uppan ba aikin ta take kawai, nan da nan kuwa bakin Goggo Sarai ya haye sama,to abinka da farar mace fatar wajen kanta ta yi jawur, d'aki ta shiga ta d'au waya ta danna Numbern su Suwaiba, dannawa ta yi tayi tana kira amma ana mata turanci, gashi yau harda Malam din aka yi fad'an ba mai duba mata yaji me ake fada, kama kan ta ta yi da taji yana ciwo ta hau kuka, zama ta yi a gefen tamfatsetsen gadon ta da ta sake mai matuqar kyau da girma, kukan ta sake fashewa da shi, sai da ta yi kuka ma'ishi sannan ta miqe ta kwanta, yau ita Bilki ke bigewa baki da luddai?
'Oh duniya, da kudin ka da komai ba za a ji tsoron ka ba yanda naga ana yi wa masu kudi, to kwarjini ne bani da shi ko me,'
Miqewa ta yi ta je gaban madubi ta kalli kanta daga sama har qasa, ga atampa nan mai tsada ta saka ta haɗa da sarqar gwal da zobuna komai ya ji, dubawa ta yi ta ga ashe fa har yanzu ko umara bata taba zuwa ba balle Hajji? Murmushi ta yi tace,
" Gaskiya mana, to ai ko kashin ku ya bushe dan kuwa dole ne wannan shekarar a sauke farali da ni naga ta raini"
komawa ta yi ta kwanta baccin wuya ya dauke ta cike da mafarkai kala2 na ban tsoro, ta dad'e tana irin mafarkan nan,a mafarkin sai ta ga 'Ya'yan ta na cikin matsala, amma sai ta dangan ta shi da sharrin maqiya masu yi masu hassada, in suka zo ganin gida za ta saka su a gaba su je neman taimako.
*****************************
Yau ce ranar da Juwairiyyah ta fi yin gyaran jikin ta kasancewar ta ranar jabeer na gida ba ya fita kasuwa,ta yi sa'a kuwa Yah Jabeer ɗin ta na gida bai fita ba,tun kafin ciki ma duk in da hannun ta ba zai iya kaiwa ba shi yake taimaka mata ya yi mata,kamar dai yanzu ma ba dika take iya wanke bayan ta ba,gashi kuma wannan abin gyaran jikin da zata yi yana buqatar a taimaka mata.
Zaune suke a tsakar gida sun fara haɗa kayan gyaran jiki,
Lemon zaqi 2,lemon tsami 1, sugar cokali 2 , Zuma cokali 1,gishiri qaramin tea spoon,dika waɗannan abubuwan ta matse ta zuba a mazubi ɗaya ta juya har Saida komai ya narke sannan ta d'akko soson wanka, ta miqa masa ta juya baya, Jabeer ne zaune a kujera 'yar tsuguno daga shi sai gajeren wando, dan kuwa ya shirya wa aikin Shima, ya na jin daɗin irin wadannan ayyukan saboda su na saka wa ya ji shi ma wani basaraken ne tun da dan shi ake gyarawa.
Gyara zama ya sake yi a Saman kujera 'yar tsuguno ya nad'e soson zai tsoma a wannan haɗin Juwairiyyah ta yi saurin riqe hannun sa ta ce,
" Yah Dan Allah sammin zan sha ya ban sha'awa"
Ta na magana tana turo baki cike da shagwab'a,
" ke fa kika ce kin ware kwanon nan ne dan gyaran jiki ko abu za a debo a ciki kin dinga kyankyami kenan shine yau zaki sha abun cikin shi?"
Cike da mamaki yake kallon ikon Allah,Sake kwab'e fuska ta yi irin na yara masu son yin kuka ta ce,
" Ni dai zan sha a haka Yayahhh"
Ɗiba ya yi a spoon din da ta gama juyawa ya bata, aiko ido a lumshe ta shanye kusan sai da ta shanye rabin haɗin, Jabeer na ganin haka yace,
"Tsaya,shin za mu yi abunnan ne ko na dawo ta gaba na qarasa baki ki shanye?"
Kafin kowa ya ankara ko ya ce wani abun Goggo ta saka hannun ta ta wanke Ammar da wani lafiyayyen marin da ko Mama Balki akai wa sai jikin ta ya gaya mata,
"Bar ganin wannan kinibabbun iyayen naka masu son abun duniya da har suke ganin D'a namiji ya fi 'Ya mace daraja ba zai hanani cin uban ka ba, in banda baqin ciki da aka koyawa yaro qarami tin yana ciki, duba fa ku ga yanda ya tsanyaran mini fitsari a qofata ya yi gaba, to ba zan lamunta ba,haka kawai ina zaune 'Ya'Yana mata da aka tsana Allah ya ɗaukaka su sun zama wani abu a rayuwa har sun gyara wa uwar su wajen zama a zo kuma a koya wa yaro qarami mugunta ya lalata min waje,"
Tsabar Ammar ya gigice sai ya kasa kukan ma sai neman inda zai je yake garin haka har kashin da yake ji ya biyo bayan fitsarin da ya yi,zuciyar Mama Bilki tafasa kawai take da b'acin rai,tin da Baba Baballiya yake da ita bai taɓa ganin irin wannan bacin ran nata ba, ita kanta Goggo Sarai ta tsorata da ganin fuskar Mama Balki, wandon Ammar Mama Bilki ta cire ta wurga a jikin qofar da aka canja wa Goggo Sarai, qofa ce irin ta qarfen nan mai kauri milk color,sannan ta aje Ammar din ta isa jikin qofar ta samu wandon ta goga sosai har labulayen, sannan ta dawo ta d'aga hannu zata wanka mata mari, sai ta tsaya bata maretan ba , ta kafe ta da wani irin kallon da ke huda gabobin jiki da tsoka ta na nuna ta da yatsan ta manuni alamar gargad'i.
Ko me ta tuna ta tsaya bata mare ta ba oho, sai kawai ta duba ta dauki Ammar da ke ta kuka yaqi yin shiru ta je ta fara gyara shi ta bashi ruwa da abincin shi ya sha ya yi bacci,sai da ta gama kula da yaron ta tsaff sannan taje ta dauke wandon nashi ta wanke ta shanya ta hau kiciniyar ɗora girki,wata irin wuta aka ɗauke a gidan gaba daya, kaff cikin gidan har Baba Baballiya ba mai iya cewa komai, Goggo Sarai na tsoron tace kanzil yanda Mama Bilki ta b'ata rai bata san me zai je ya zo ba, ita kuma Mama Bilki ta fasa marin ta ne ganin datajar Baba Baballiya dake bayan ta, shi kuma ya fuskanci hakan, sannan ya yi shiru ne saboda kar ya bata damar magana ya san kuka zata yi dan zuciyar ta cike take da baqin ciki, sai da ya tabbatar ta fara sauka tinda gashi ta ci gaba da 'yan aikace2n tsakar gida sannan ya samu waje a tsakar gidan ya zauna ya cewa Goggo Sarai,
"Yau kin ban mamaki Sarai ba kaɗan ba, ki duba ki ga abinda kika aikata, yanzu marin da kika yi wa yaron nan ko ni ki kaiwa ai sai na ji shi a jikina ba shi ba ma, dubi yanda yatsunki suka kwanta a kan fuskar shi kamar qunar wuta, haba dan Allah, kin kyauta kenan, baki taɓa ganin fushin Bilkisu a kaf rayuwar ku ba irin haka ko kin taɓa gani? to ina mai tabbatar maki ki kiyayi sakata a irin fushin nan bana kusa, dan duk abinda ta aiwatar akan ki ke kika jawo wa kan ki da kan ki tunda baki iya riqe girman da Allah ya baki ba,a iya yau dai ai kin ga misalin abinda zata iya aikata wa ko?"
Sai a sannan ne Goggo Sarai ta samu bakin magana,
" Eh tinda kun haifi ɗan gwal, dole mana ku fifita shi akan komai, to da dan da uwar na san meye matsalar ku ba komai ke damun ku ba face baqin ciki, kuma nan gani nan bari dumamen mayya in dai nice ni da 'Ya'yana yan albarka mun fi ƙarfin ku"
Cikin Fushi ta juya ta tafi fuuuu ta hau cire labulayen dika d'akin ta watso su tsakar gida ta dauki ɗaya a ciki ta goge qofar dakin da ya ɓaci da kashin Ammar da shi, ta saka ruwa ta wanke, ta qara gogewa da labulayen masu kyau din,duk kyau da tsadar labulayen haka ta saka hijab din ta ta fita waje ta watsar ta dawo, tana wani isa da taqama taje ta canja wasu,ta buga shewa da gud'a ta ce,
" Ahayyyeeeeee ayyuuuuririiiiii, to bari ku ji sau goma wannan shegen tsinannen yaron zai b'atan qofa sau go......."
Goggo sarai bata samu damar ida fad'in me take so ba ta ji qummmmmm a bakin ta, Mama Balki ce da ta hasala dan jin ana tsinewa ɗan ta ta saita bakin Goggo Sarai da ludayin da take juya miya ji ka ke kwalll ya daki fuskar ta, ihu Goggo Sarai ta saka ta na zagin Mama Balki, ita kuwa kamar ba ita ta aikata hakan ba ta je ta durqusa ta dauki ludayin ta ta juya ta ci gaba da aikin ta.
Mai Baba Baballiya zai yi da ya wuce, cikin dariya ya ce,
" Kai amma Gimbiya yau kam sai dai ace na zama munafukin mata, amma kin burgeni, ke kuma ɗan da kk kira shege, duniya ta san ni ne uban shi, sannan, tsinanne da kika kira min d'a ba za ki ga tsinewa a 'ya'yana ba inshaa Allah ina mai musu addu'a komai abinki Allah zai karen su, sai dai kiga tsinewar a kan kan ki dan ba yau na fara jin kin kira min D'a da wannann sunan ba, ke yanzu ba abin kunya bane ace ki na faɗa akan qaramin yaro har irin haka na shiga tsakanin ku ke da abokiyar zaman ki? To ina qara gargadin ki ki kiyayi randa bana gida ki taba wannan baiwar Allah ina tausaya maki "
Ya qarasa maganar cikin dariya ya fita qofar gida, duk abinnan da ake Mama bata ce uppan ba aikin ta take kawai, nan da nan kuwa bakin Goggo Sarai ya haye sama,to abinka da farar mace fatar wajen kanta ta yi jawur, d'aki ta shiga ta d'au waya ta danna Numbern su Suwaiba, dannawa ta yi tayi tana kira amma ana mata turanci, gashi yau harda Malam din aka yi fad'an ba mai duba mata yaji me ake fada, kama kan ta ta yi da taji yana ciwo ta hau kuka, zama ta yi a gefen tamfatsetsen gadon ta da ta sake mai matuqar kyau da girma, kukan ta sake fashewa da shi, sai da ta yi kuka ma'ishi sannan ta miqe ta kwanta, yau ita Bilki ke bigewa baki da luddai?
'Oh duniya, da kudin ka da komai ba za a ji tsoron ka ba yanda naga ana yi wa masu kudi, to kwarjini ne bani da shi ko me,'
Miqewa ta yi ta je gaban madubi ta kalli kanta daga sama har qasa, ga atampa nan mai tsada ta saka ta haɗa da sarqar gwal da zobuna komai ya ji, dubawa ta yi ta ga ashe fa har yanzu ko umara bata taba zuwa ba balle Hajji? Murmushi ta yi tace,
" Gaskiya mana, to ai ko kashin ku ya bushe dan kuwa dole ne wannan shekarar a sauke farali da ni naga ta raini"
komawa ta yi ta kwanta baccin wuya ya dauke ta cike da mafarkai kala2 na ban tsoro, ta dad'e tana irin mafarkan nan,a mafarkin sai ta ga 'Ya'yan ta na cikin matsala, amma sai ta dangan ta shi da sharrin maqiya masu yi masu hassada, in suka zo ganin gida za ta saka su a gaba su je neman taimako.
*****************************
Yau ce ranar da Juwairiyyah ta fi yin gyaran jikin ta kasancewar ta ranar jabeer na gida ba ya fita kasuwa,ta yi sa'a kuwa Yah Jabeer ɗin ta na gida bai fita ba,tun kafin ciki ma duk in da hannun ta ba zai iya kaiwa ba shi yake taimaka mata ya yi mata,kamar dai yanzu ma ba dika take iya wanke bayan ta ba,gashi kuma wannan abin gyaran jikin da zata yi yana buqatar a taimaka mata.
Zaune suke a tsakar gida sun fara haɗa kayan gyaran jiki,
Lemon zaqi 2,lemon tsami 1, sugar cokali 2 , Zuma cokali 1,gishiri qaramin tea spoon,dika waɗannan abubuwan ta matse ta zuba a mazubi ɗaya ta juya har Saida komai ya narke sannan ta d'akko soson wanka, ta miqa masa ta juya baya, Jabeer ne zaune a kujera 'yar tsuguno daga shi sai gajeren wando, dan kuwa ya shirya wa aikin Shima, ya na jin daɗin irin wadannan ayyukan saboda su na saka wa ya ji shi ma wani basaraken ne tun da dan shi ake gyarawa.
Gyara zama ya sake yi a Saman kujera 'yar tsuguno ya nad'e soson zai tsoma a wannan haɗin Juwairiyyah ta yi saurin riqe hannun sa ta ce,
" Yah Dan Allah sammin zan sha ya ban sha'awa"
Ta na magana tana turo baki cike da shagwab'a,
" ke fa kika ce kin ware kwanon nan ne dan gyaran jiki ko abu za a debo a ciki kin dinga kyankyami kenan shine yau zaki sha abun cikin shi?"
Cike da mamaki yake kallon ikon Allah,Sake kwab'e fuska ta yi irin na yara masu son yin kuka ta ce,
" Ni dai zan sha a haka Yayahhh"
Ɗiba ya yi a spoon din da ta gama juyawa ya bata, aiko ido a lumshe ta shanye kusan sai da ta shanye rabin haɗin, Jabeer na ganin haka yace,
"Tsaya,shin za mu yi abunnan ne ko na dawo ta gaba na qarasa baki ki shanye?"