← Book details Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 61

Sashe 39

Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Rufen baki sallamammiya kawai, an yi asiri da tuggu kala2 an raba ni dake, to ki je nima na huta da dawainiya da ɗan wani"

Juyawa ta yi tabar wajen Salma kuwa cikin qunan rai da baqin cikin halayya ta uwar ta ta shige d'akin Mama Bilki, wadda ta ji komai da ya faru, fad'awa kan cinyar ta  Salma ta yi tana kukan takaicin hali irin na uwar tasu, shafa kanta kawai Mama Bilki take, bata furta mata komai ba,cikin kuka Salma ta ce,

" Mama ni fa ba kwad'ayi ne ya sa na tambayi Adda Saudat kudi ba, na tambaye ta ne kawai saboda ki na ganin ko tirare bani da shi, ga shi yanzu sai da alimun ko lemon tsami nake amfani a hammata ta a madadin tiraren,da ace ina sana'a yaushe zan zauna haka? Tunanin da na yi na ina sana'a kudin zasu taimakan wajen kula da abinda ke ciki na da ni kai na shine ya sa na tambayi Addah Saudat kuma ta bani dubu biyar na ja jari, shine Goggo take fad'an maganganu marasa daɗi akai na da abinda ke ciki na"

" Hakuri zaki yi Salma uwa ba abin wasa bace, dole mu yi mata biyayya matsawar ba sab'on Allah a duk abinda ta sanya mu,dan haka ki yi hakuri, to tin da kin samu jarin yanzu me zaki na yi na siyarwa?"

Tashi zaune Salma ta yi ta share hawayen ta sannan ta ce,

" Mama Bilki ni da ina son na fara saida gishiri da omo da ɗan qulle qulle na gida, amma yanzu da na samu wannan kud'in mai yawa sai na ji ina son in fara Saida Meatpie, naga kina da injin yin taliya, kuma na kula kayan flour ana cinikin su, in ba su ba ban san me zan iya yin sana'a akai ba kuma"

Murmushi Mama Balki ta yi sannan ta ce,

" Hakan ma shawara ce mai kyau, Allah ya sanya albarka a ciki"

" Ameen mamana"

Kwantar da kanta ta sake yi a jikin ta ita kuma tana shafa gashin kan Salman a hankali.

******************************

Yau kusan sati ɗaya da kwana uku kenan Suwaiba na kwance tana jinyar qirjin ta da aka fafe wa albarkatun wajen, Alhj Salihu dayaga zata farka sai ya danna mata allurar bacci ta koma, ko ya shaqa mata wata powder ta koma baccin, a haka ta yi wadannan kwanakin,shine yake yi mata wanka ya canja mata kaya,sannan ya saka mata ruwa da allurai na kashe zafin ciwo da anti biotics,ya zama babban likita kawai a cikin gidan shi dan ya kula da Suwaiba, a haka sai da ya kula wajen ya warke tas sannan ya kyale ta da allurai na bacci da yake mata.

Ranar da ya bar ta kuwa bai yi mata allurar baccin ba da ta farka sai ta ji kan ta kamar an ɗora mata abu mai nauyi, da kyar ta tashi daga gadon ta ta isa gaban madubi a hankali ta d'aga rigar ta ta na kallon qirjin ta, nan take wasu hawaye masu azabar zafi suka hau zuba a kuncin ta, ina dukiyar Fulanin ta suke ne, me ya same ta?

Duk abinda take yi akan idanun Alhaji Salihu take aikata su, cikin rashin k'warin jiki ta koma ta kwanta a Saman gadon nata tare da nitsar da kan ta cikin pillow kuka take yi sosai mai taɓa zuciya, zama ya yi a gefen ta ya kama hannun ta ya na lallashin ta, a hankali ta d'aga kan ta ta na kallon shi,da kyar ta buɗe baki ta ce masa,

" Sweet wai me ya same ni ne, wanne mummunar qaddarar ce ta hau kirji na ni suwaiba ?"

" Shiiiiiiii kar ki na yin magana sosai, hatsari muka samu a gidan, yan fashi  ne suka suka shigo a ranar da ki ka dawo kina bacci suka yanke maki nono, ni kuma dana dawo na ganki kin suma shine na kai ki asibiti aka maki aiki daga nan na dawo da ke gida nake ta kula da ke"

A firgice ta miqe daga kwanciyar da take ta ce,

" Dama abinda ya faru kenan? Yanzu tsabar rashin imani su rasa me za su cire min sai wannan waje mai daraja?"

Ta fada tare da zaro idanun ta da ke ta zubar da zazzafan hawaye, cikin kukan nata ta ce,

"Na shiga uku ni Suwaiba,ya zan rayu ba mahaifa ba nono,yanzu nan gaba me zan rasa kuma, Alhj na fa san kai ne sanadin rasa nono na  ba wani 'yan fashi,Saudat ta fad'an min ban ji ba ban yarda ba, saboda ina son ka, ko da ina son kudin ka na yarda cewa a yanzu ina son ka so na gaskiya,zan iya rayuwa da kai ko ba mahaifa shine hakan  be ishe ka ba sai da ka qara da wata kadarar tawa yanzu ta ya zan rayu ba nono ba mahaifa"

Rushewa ta yi da wani irin kuka mai ban tausayi, cikin tausaya mata Alhj ya fara magana"

"ki yi hakuri Baby yau zan........"

katse shi ta yi cike da bala'i ta ce,

" Kar ka sake kira na da wata baby again, i hate u Alhaji, na tsane ka, na tsane ka da dikkan rayuwa ta"

Kukan ta ci gaba da yi mai ratsa zuciyar mai tausayi kai har da mara tausayin ma,matsawa ya yi ya kamo ta jikin shi, da sauri ta zame ta ci gaba da cewa,

" Kar ka taɓa ni azzalumi kawai,ka kuskura ka sake taɓa ni ni ma sai na yanke maka inda ba zaka taɓa amfanuwa ba a jikin ka"

Cike da matsanancin fushin da bai taɓa sanin suwaiban da yake wa kallon doluwa na da shi ba ta yi maganar,nan take wani irin shakkar ta ta shige shi, miqewa ta yi cike da jiri zata fita, cikin sassanyar murya Alhaji ya ce mata,

"Ina zaki je kuma"

"Gidan mu zani, na gama auren ka, na kuma gama aure a ABUJA har abada daga yau,daga rana mai kamar ta yau bani ba Abuja"

" Lallai ma Suwaiba, abinda baki sani ba shine, ba inda zaki qara fita ko nan da can ne kuwa sai da sani na, dan kuwa ni a yanzu ba zan iya rayuwa ba ke ba, kin ga kuwa sai ki shirya zama da masoyin ki na gaskiya, na amince ni zan jure rashin albarkatun qirjin naki tunda ni ne sanadi"

"Za kuwa ka mutu dan ba abinda zai hana ni barin gidannan, ko kana so ko baka so sai na bar gidan nan, in ka barni na tafi lafiya ba hukumar da zan haɗaka da ita, amma in ka hanani ba abinda zai hana ni haɗaka da hukuma zaɓi ya rage ya naka"

Wani shu'umin murmushin rainin hankali ya mata ya ce,

"To ai baki san wani abu ba, qungiyata babbar qungiya ce suwaiban,ni ɗin ba wai qaramin mutum bane ko baki gani bane?manyan gwamnati da yan kasuwa ba wanda babu a cikin qungiyar mu, ba yanda za ai ki had'a ni da hukuma kuma a samu hukunta ni din, mata kalar  ki da wanda suka fiki komai sun fi dubi kuma mun masu wannan aikin balle ke, dan haka hakuri zaki yi kawai mu qarasa rayuwa dake a haka, in kin tafi wa zai na baki abun daɗin da nake baki? wa zaina debe maki kewa? wa zai zauna dake babu nono? Hakura zaki yi kawai mu zauna a haka tun da kuɗi ki ke so ni kuma zan ci gaba da jiyar dake daɗi da dukiya ta"

Tallabo wuyan ta ya yi ya na kallon fuskar ta,iya kuwa gaba ɗaya ta qame ta dauke kan ta daga ganin shi hawaye kawai ke zuba mata, ga wani irin tsoron shi da ke kwance a qasan zuciyar ta, yau ya zata yi ta kub'uta daga hannun wannan azzalumin?

Kuka ne ya kwace mata sosai, key din motar shi ya ɗauka ya fice ya bar mata gidan, anan inda take tsaye ta durqushe tana kuka mai ban tausayi.
*****************************

Talle kam ya saka marka a tsaka mai wuya ita da yayan shi, dan baya son maganar ta fita waje shi yasa bai ce masu qala ba,sai kawai ya fito da wata mugunta, gonar shi ta daji mai shegen nisa ya ke sa su zuwa gyaran ta, duba da cewar damuna ta kusan zuwa, a cewar shi ya na da majiya qarfin zuciyar cim amana irin su ba abinda zai sanya shi biyan kud'in gyaran gona,in sun ga dama in sun shiga dajin ma su ci amanar shi ya yafe masu amma tabbas sai sun gyara masa gona kafin damina ta sauka.

kullum can suke tafiya ba abinci ba ruwa, amma shi zai je a machine din shi da abincin shi da ruwan shi ya yi shawagi ya sa ido ya ga ya aikin yake tafiya,su kuma su Baban gida gonar shi ta can wani qauyen dake kusa da su ya tura su, saboda ya yi yarjejeniya da su akan hakan, in ba haka ba ya kaisu birni ga hukuma a huhunta su akan yi wa 'ya'yan shi ciki da suka yi,da jin haka suka amince suka yi biyayya suma.

Kan kuce me Marka ta fita hayyacin ta, 'yan mazaunan nan da ake kad'awa ana jan hankali da su duk sun zube, duk ta dame qashi ya fito mata ko ta ina,mutanen gari kuwa sai gulmammaki suke yi akan abinda ke faruwa a gidan Talle, kowa da ruwayar shi akan abinda ke faruwa amma ba wanda ya san gaskiyar lamari.

Kowa ya rasa gane dalilin Talle na aikata haka, da damar mutane sai suka alaqanta hakan da tsantsar rashin mutuncin shi, su Huwaila kuwa kullum sai sun yi surfen abinda za ai tuwo da shi sun dake da hannun su sun mayar dashi gari, sannan su yi tuwon da za a ci a gidan, ga aikin qannen su da ya ɗora masu, walaka ta yi masu yawa kamar zata kashe su,ga qaramin ciki suna fama da shi.
Chapter 39 · 0% Book details