Sashe 29
Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kad'a kai ta yi alamar A'a su ci gaba da gyaran jikin, sai sud'e baki take kamar ta ci wani kayan daɗi, fara wanke mata fuskar ta ya yi zuwa wuyan ta har bayan ta da wannan haɗin da soson,sai ya d'aga hannun ta ya wanke mata hammatar ta, sai ya dawo ta gaba ya wanke mata tsakanin cinyoyin ta zuwa cinyoyin da guiwar ta a haka saida ya hade kaf jikin ta ya wanke mata shi da wannan haɗin da soso, bayan sun gama ne ta yi masa godiya, tare da furta masa kalmar da ta zama masu al'ada wato,
" Ina son ka"
Maimaita mata shima ya yi ya d'aga ta, cikin nishi ya ce,
"Wai wai waiiii Babyna gaba ɗaya kin yi nauyi yanzu, da kyar fa na d'ago ki"
Turo baki ta yi kamar zata yi kuka, dama yasan za ai haka tsokana ce kawai da ta masa yawa ya sanya shi tanka qibar ta,dariya ya fara yana kame bakin shi, tura hannun shi ta yi daga kafadar ta zata fara tafiya, cike da tsokana Jabeer ya furta,
" Mai ciki ihmmm ganinan tafe, me ciki, wallahi bani son sunan nan,"
Juyo wa ta yi ta biyo shi suka fara zagaye bangaren na su tana kukan shagwaba, tare da fad'in,
"Inna kama ka yau a gidannan sai ka yi tsallen kwado,"
Sai huci take yi tsabar ta gaji kuma da gaske ta ɗan qara qibar, dariya Jabeer yake tayi mata harda riqe ciki dayaga ta gaji ta nemi waje ta zauna kuwa sai ya je ya duqa tare da kama kunnen sa kamar na masu tsallen kwado, cikin marairaice murya yace,
" Haba Babyn Yaya, kiyi hakuri, in dai nine na yi alqawari ba zan sake tsokanar ki ba na tuba a yafe min"
Ya qarasa maganar tare da karkata kai gefe alamun yayi nadama,murmushi ta yi sannan ta ce masa,
"Na hakura amma ka jawa kan ka kai zaka kaini toilet a hannun ka ka dawo da ni, dama na kula tinda cikin nan ya yi girma sai dai ka tallebe ni ta gefe baka daukata, bazan lamunci hakan ba ehe"
"An gama ranki ya dad'e da imani"
Murmushi suka yi wa junan su a tare suka furta,
" Ina son ka/ki"
Wucewa ya yi ya je ya haɗa mata ruwa wanka mai d'umi ba mai zafi ba,sannn ya je ya ɗauke ta kan su tafi band'akin ne tace masa
"Ina zuwa zan dau wayata,"
A haka ta na hannun shi ya kaita d'aki ta miqa hannu ta dauki wayar ta,
" Kashhhh ashe ma Nafee bata da waya, bari inna fito na leqa na karbo dankalin in ta gama hada min din"
kai ta band'akin ya yi ya dauraye mata wannan danqon, sai ga jikin ta yana wani laushi da haske, kamar wata matar masu kuɗi irin wanda fatar su ta ji hutu ɗin nan, sun fito kenan yana dauke da ita a hannu ya bada baya za su shiga parlour Nafee ta yi sallama, dakata wa ta yi, sai da aka bata izini sannan ta shiga,baje ta tadda Juwaira a kujera a zaune cike da tsokana ta ce,
"Me ciki ! Auuu Yi haƙuri na manta,ga dankalin na mai da shi ya yi laushi kamar yanda kika ce na saka lalle da k'wai amma ba dika k'wan na juye ba farin ruwan kawai na saka, bayan na haɗa na zuba gishiri da kuma manjan kamar dai yanda ki ka ce,ai d'azu da ki na nan da sai kin ci dariyar Innarmu , wai fa cewa take wani abun daɗin za a haɗa, wai Nafee, irin abun rannan zaku mana mai kwai?"
Dariya suka saka harda jabeer, sai da suka yi mai isar su sannan ya b'ata rai ya ce,
"Ya ishe ku haka Innata ce fa"
Dariya suka qara tintsirewa da ita harda shi din,sannan Jabeer ya ce
" Feena taso ayi wannan dake, kuma kiyi a hankali kar ki ji ma mata ta ciwo"
" Hummmm Masu mata"
Nafeen ta furta a hankali Jabeer kuwa ya ji ta amma sai ya ce,
"Me kk ce?"
Cikin sauri Nafee ta ce,
" Niiiii me na isa cewa, ba abinda na ce ko nake shirin faɗa ma"
Dariya suka bawa Juwairah ta yi ta yi kuwa, daga baya suka samu wannan haɗin suka yi ta murza mata a jiki kamar dilka, kafin kace me juwairah ta yi kamar wata amarya, suna cikin yi Nafee ta miqe ta dakko ayaba daya, da k'wai, sai zuma da markadadden dankalin hausan da ta markade ya yi laushi, haɗe su ta yi har ayabar suka yi laushi sosai ta koma ta saman kan Juwairiyyah tana tsaga gashin kan ta tana shafawa a can qasan gashi,shi kuma Jabeer yana yi mata dilka, bayan ta kusa gamawa ne Juwairah tace,
" Amma dai Nafee baki saka albasa a hadin yau ba ko? Dan na ji ba warin ta"
"Eh ban saka ba na san ba zaki so ba maybe ya saka ki amai shine na bi ɗaya hanyar da ki ka taɓa faɗa min na yi wannan ɗin"
" kaiiii amma ko na gode yar uwa Allah ya kawo miji na gari mumini salihi wanda zai so ki ya qaunace ki fiye da yanda Yah Jabeer ke yi min, ko dake anya za a samu kamar Yah Jabeer d'ina a wannan zamanin kuwa?"
Ta karasa maganar ta cike da tsokanar Nafeen da ta kasa amsa addu'ar saboda kunyar Yayan nasu.
Wannan haɗin na dankalin turawa da lalle da kwai da manja kaɗan da gishiri ko baqar mace ce take yi zai sanya ta yi haske mai ɗaukan hankali,dan kuwa ya na fitar da kalar mutum ta asali ya sa kalar ta yi kyau, ga laushin jiki da santsi da yake sanyawa.
Shi kuma haɗin dankalin hausa yana qara tsahon gashi ne da hana shi karyewa,sannan ana yin zallahn na albasa madadin dankalin ko dankalin a madadin albasa, kowanne yana fidda gashi sosai kuma ya hana shi karyewa, ya yi laushi da santsi, sai dai na albasa na da wari, dan haka in uwargida ta gama ana son ta samu abun wanke kai mai qamshi sosai ta wanke kuma in an saka ana son a yi massaging scalf din sosai ya shiga ko ina.
Ba su suka gama ba sai wajejen azahar, Juwairiyyah tayi bacci kafin su gama, tashi Jabeer ya yi yana miqa ya ce,
"Wai gayu da daɗi da wuya"
"Hhhhh Yah to ai kai zaka mora gwanda ka taɓa ka ji ya take ji da da take yi ita daya"
"Waya faɗa maki da din ban taya ta wasu qana nan abubuwan? Ban dai taba irin wannan me hawalar bane, ashe haka take shan wuya duk dan ta burgeni baiwar Allah"
Ya fada yana shafa gefen fuskar ta, bude idon ta ta yi ta ce,
" Ku kuma ne kuke faɗa?"
Nan da nan ta tsargu ta zaci suna magana ne akan qibar da ta yi, haɗe fuska ta yi kamar bata taɓa dariya ba, Nafee kuwa da ta gane dariya ce taso kwace mata, amma tace bari nasan me zan yi masu na gudu na bar shi da aikin lallashi,
" Ni dai daya faɗa cewa na yi ba ruwana in kika ji, dan haka ba ruwana yanzun ma ni tafiya zan yi innarmu na kirana, Yah ka fada mata"
kama baki ya yi yana mamakin sharrin da yarinyar ke son haɗa masa, kan ya yi yunqurin wani abu yaji ta janyo hannun shi gaba daya ya zube agefen kujerar da take zaune hawaye ta fara ta dora kanta a qafar shi ta rushe da kuka,
"Shikenan yanzu dan na yi qiba sai a dinga tsokana ta, ai ba muni na yi ba, kuma da na haihu zan dawo daidai"
Tana magana tana shan majina irin na masu kuka, rasa me zai yi ya wanke kan shi ya yi,dan yasan sharri kam Nafee ta gama haɗa masa shi ta yi gaba bai da hanyar fita, kamo ta ya yi ya hau massaging kafadun ta sannan ya ce,
" kiyi hakuri princess, dama gani na yi cikin ya yi girma sosai shine nace ko yan biyu zaki haifa?"
Cikin zumud'i tashi zaune ta na goge hawayen ta ta kalle shi tace
"Allah yasa yayana"
" Ameen to tashi muje mu yi wanka an kusa kiran sallah"
miqewa ta yi da kyar, a ranshi yace,
'Waiii Allah ya taimake ni, Nafee Allah na son ki da ta burkicen yau sai kin wahala kema'
Wanka suka yi ya gyara mata kan ta ya saka mata riga doguwa har qasa mai bud'ad'd'en qugu, ba qaranin kyau ta yi ba, kallon ta yake kamar kar ya daina, ita ko murmushi take ta danga wa dan ganin kyau da laushin da fatar ta tayi sai fidda wani annuri take yi, bayan sunyi sallah ne Innarmu ta aika masu da abincin su suka ci, tin da ya saka mata ruwa ta sha ta bingire a zaunen ta hau bacci, daga ta ya yi da kyar ya na nishi ya kwantar da ita a Saman gado shima ya kwanta a gefen ta dan sha baccin su tare.
Yah Jabeer kam ya dad'e kan ya samu wannann bacci ya ɗauke shi, dan kuwa haƙuri kawai ya yi ba qaramin kyau Juwairiyyah ta yi masa ba, ga princess din shi a kusa da shi,yawan bacci irin na me ciki ya hana shi more gayun da ta sha domin shi,ni ko nace sai kun tashi asha bacci laaaafiyaaa masoya......
[21/07, 7:46 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 'YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 20:
Alhj Kallah, Alhj Salihu, Oga Zaks, su kad'ai ne mutanen da na iya ganewa a qaton table din da yake cikin wani makekeken waje a zazzaune, taron wajen ya haɗa da wasu manyan Alhazawa masu ji da kuɗi, izza, taqama da qarfin iko, wanda adadin su zai iya haura mutum ashirin.
Gaba ɗayan su sanye suke da shigar tasu da suka saba yi wato shigar farin kaya da ratsin ja, kowa ka gani a wajen muzurai yake kamar su na jiran wani abu mai mahimmanci,haka zalika kowa ji yake da kan shi tare da ganin Shima ya kai wani jan wuya a wajen.
" Ina son ka"
Maimaita mata shima ya yi ya d'aga ta, cikin nishi ya ce,
"Wai wai waiiii Babyna gaba ɗaya kin yi nauyi yanzu, da kyar fa na d'ago ki"
Turo baki ta yi kamar zata yi kuka, dama yasan za ai haka tsokana ce kawai da ta masa yawa ya sanya shi tanka qibar ta,dariya ya fara yana kame bakin shi, tura hannun shi ta yi daga kafadar ta zata fara tafiya, cike da tsokana Jabeer ya furta,
" Mai ciki ihmmm ganinan tafe, me ciki, wallahi bani son sunan nan,"
Juyo wa ta yi ta biyo shi suka fara zagaye bangaren na su tana kukan shagwaba, tare da fad'in,
"Inna kama ka yau a gidannan sai ka yi tsallen kwado,"
Sai huci take yi tsabar ta gaji kuma da gaske ta ɗan qara qibar, dariya Jabeer yake tayi mata harda riqe ciki dayaga ta gaji ta nemi waje ta zauna kuwa sai ya je ya duqa tare da kama kunnen sa kamar na masu tsallen kwado, cikin marairaice murya yace,
" Haba Babyn Yaya, kiyi hakuri, in dai nine na yi alqawari ba zan sake tsokanar ki ba na tuba a yafe min"
Ya qarasa maganar tare da karkata kai gefe alamun yayi nadama,murmushi ta yi sannan ta ce masa,
"Na hakura amma ka jawa kan ka kai zaka kaini toilet a hannun ka ka dawo da ni, dama na kula tinda cikin nan ya yi girma sai dai ka tallebe ni ta gefe baka daukata, bazan lamunci hakan ba ehe"
"An gama ranki ya dad'e da imani"
Murmushi suka yi wa junan su a tare suka furta,
" Ina son ka/ki"
Wucewa ya yi ya je ya haɗa mata ruwa wanka mai d'umi ba mai zafi ba,sannn ya je ya ɗauke ta kan su tafi band'akin ne tace masa
"Ina zuwa zan dau wayata,"
A haka ta na hannun shi ya kaita d'aki ta miqa hannu ta dauki wayar ta,
" Kashhhh ashe ma Nafee bata da waya, bari inna fito na leqa na karbo dankalin in ta gama hada min din"
kai ta band'akin ya yi ya dauraye mata wannan danqon, sai ga jikin ta yana wani laushi da haske, kamar wata matar masu kuɗi irin wanda fatar su ta ji hutu ɗin nan, sun fito kenan yana dauke da ita a hannu ya bada baya za su shiga parlour Nafee ta yi sallama, dakata wa ta yi, sai da aka bata izini sannan ta shiga,baje ta tadda Juwaira a kujera a zaune cike da tsokana ta ce,
"Me ciki ! Auuu Yi haƙuri na manta,ga dankalin na mai da shi ya yi laushi kamar yanda kika ce na saka lalle da k'wai amma ba dika k'wan na juye ba farin ruwan kawai na saka, bayan na haɗa na zuba gishiri da kuma manjan kamar dai yanda ki ka ce,ai d'azu da ki na nan da sai kin ci dariyar Innarmu , wai fa cewa take wani abun daɗin za a haɗa, wai Nafee, irin abun rannan zaku mana mai kwai?"
Dariya suka saka harda jabeer, sai da suka yi mai isar su sannan ya b'ata rai ya ce,
"Ya ishe ku haka Innata ce fa"
Dariya suka qara tintsirewa da ita harda shi din,sannan Jabeer ya ce
" Feena taso ayi wannan dake, kuma kiyi a hankali kar ki ji ma mata ta ciwo"
" Hummmm Masu mata"
Nafeen ta furta a hankali Jabeer kuwa ya ji ta amma sai ya ce,
"Me kk ce?"
Cikin sauri Nafee ta ce,
" Niiiii me na isa cewa, ba abinda na ce ko nake shirin faɗa ma"
Dariya suka bawa Juwairah ta yi ta yi kuwa, daga baya suka samu wannan haɗin suka yi ta murza mata a jiki kamar dilka, kafin kace me juwairah ta yi kamar wata amarya, suna cikin yi Nafee ta miqe ta dakko ayaba daya, da k'wai, sai zuma da markadadden dankalin hausan da ta markade ya yi laushi, haɗe su ta yi har ayabar suka yi laushi sosai ta koma ta saman kan Juwairiyyah tana tsaga gashin kan ta tana shafawa a can qasan gashi,shi kuma Jabeer yana yi mata dilka, bayan ta kusa gamawa ne Juwairah tace,
" Amma dai Nafee baki saka albasa a hadin yau ba ko? Dan na ji ba warin ta"
"Eh ban saka ba na san ba zaki so ba maybe ya saka ki amai shine na bi ɗaya hanyar da ki ka taɓa faɗa min na yi wannan ɗin"
" kaiiii amma ko na gode yar uwa Allah ya kawo miji na gari mumini salihi wanda zai so ki ya qaunace ki fiye da yanda Yah Jabeer ke yi min, ko dake anya za a samu kamar Yah Jabeer d'ina a wannan zamanin kuwa?"
Ta karasa maganar ta cike da tsokanar Nafeen da ta kasa amsa addu'ar saboda kunyar Yayan nasu.
Wannan haɗin na dankalin turawa da lalle da kwai da manja kaɗan da gishiri ko baqar mace ce take yi zai sanya ta yi haske mai ɗaukan hankali,dan kuwa ya na fitar da kalar mutum ta asali ya sa kalar ta yi kyau, ga laushin jiki da santsi da yake sanyawa.
Shi kuma haɗin dankalin hausa yana qara tsahon gashi ne da hana shi karyewa,sannan ana yin zallahn na albasa madadin dankalin ko dankalin a madadin albasa, kowanne yana fidda gashi sosai kuma ya hana shi karyewa, ya yi laushi da santsi, sai dai na albasa na da wari, dan haka in uwargida ta gama ana son ta samu abun wanke kai mai qamshi sosai ta wanke kuma in an saka ana son a yi massaging scalf din sosai ya shiga ko ina.
Ba su suka gama ba sai wajejen azahar, Juwairiyyah tayi bacci kafin su gama, tashi Jabeer ya yi yana miqa ya ce,
"Wai gayu da daɗi da wuya"
"Hhhhh Yah to ai kai zaka mora gwanda ka taɓa ka ji ya take ji da da take yi ita daya"
"Waya faɗa maki da din ban taya ta wasu qana nan abubuwan? Ban dai taba irin wannan me hawalar bane, ashe haka take shan wuya duk dan ta burgeni baiwar Allah"
Ya fada yana shafa gefen fuskar ta, bude idon ta ta yi ta ce,
" Ku kuma ne kuke faɗa?"
Nan da nan ta tsargu ta zaci suna magana ne akan qibar da ta yi, haɗe fuska ta yi kamar bata taɓa dariya ba, Nafee kuwa da ta gane dariya ce taso kwace mata, amma tace bari nasan me zan yi masu na gudu na bar shi da aikin lallashi,
" Ni dai daya faɗa cewa na yi ba ruwana in kika ji, dan haka ba ruwana yanzun ma ni tafiya zan yi innarmu na kirana, Yah ka fada mata"
kama baki ya yi yana mamakin sharrin da yarinyar ke son haɗa masa, kan ya yi yunqurin wani abu yaji ta janyo hannun shi gaba daya ya zube agefen kujerar da take zaune hawaye ta fara ta dora kanta a qafar shi ta rushe da kuka,
"Shikenan yanzu dan na yi qiba sai a dinga tsokana ta, ai ba muni na yi ba, kuma da na haihu zan dawo daidai"
Tana magana tana shan majina irin na masu kuka, rasa me zai yi ya wanke kan shi ya yi,dan yasan sharri kam Nafee ta gama haɗa masa shi ta yi gaba bai da hanyar fita, kamo ta ya yi ya hau massaging kafadun ta sannan ya ce,
" kiyi hakuri princess, dama gani na yi cikin ya yi girma sosai shine nace ko yan biyu zaki haifa?"
Cikin zumud'i tashi zaune ta na goge hawayen ta ta kalle shi tace
"Allah yasa yayana"
" Ameen to tashi muje mu yi wanka an kusa kiran sallah"
miqewa ta yi da kyar, a ranshi yace,
'Waiii Allah ya taimake ni, Nafee Allah na son ki da ta burkicen yau sai kin wahala kema'
Wanka suka yi ya gyara mata kan ta ya saka mata riga doguwa har qasa mai bud'ad'd'en qugu, ba qaranin kyau ta yi ba, kallon ta yake kamar kar ya daina, ita ko murmushi take ta danga wa dan ganin kyau da laushin da fatar ta tayi sai fidda wani annuri take yi, bayan sunyi sallah ne Innarmu ta aika masu da abincin su suka ci, tin da ya saka mata ruwa ta sha ta bingire a zaunen ta hau bacci, daga ta ya yi da kyar ya na nishi ya kwantar da ita a Saman gado shima ya kwanta a gefen ta dan sha baccin su tare.
Yah Jabeer kam ya dad'e kan ya samu wannann bacci ya ɗauke shi, dan kuwa haƙuri kawai ya yi ba qaramin kyau Juwairiyyah ta yi masa ba, ga princess din shi a kusa da shi,yawan bacci irin na me ciki ya hana shi more gayun da ta sha domin shi,ni ko nace sai kun tashi asha bacci laaaafiyaaa masoya......
[21/07, 7:46 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 'YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 20:
Alhj Kallah, Alhj Salihu, Oga Zaks, su kad'ai ne mutanen da na iya ganewa a qaton table din da yake cikin wani makekeken waje a zazzaune, taron wajen ya haɗa da wasu manyan Alhazawa masu ji da kuɗi, izza, taqama da qarfin iko, wanda adadin su zai iya haura mutum ashirin.
Gaba ɗayan su sanye suke da shigar tasu da suka saba yi wato shigar farin kaya da ratsin ja, kowa ka gani a wajen muzurai yake kamar su na jiran wani abu mai mahimmanci,haka zalika kowa ji yake da kan shi tare da ganin Shima ya kai wani jan wuya a wajen.