Sashe 45
Yan Abuja Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" kin ji ko ? Kin ji dai da kunnen ki yau 'Yar ki ba zata iya zama dake ba a d'aki ɗaya ba saratu ? Kar ki damu Suwaiba, wannan kud'in bai kamata ki yi amfani da su ba, kamata ya yi a bada sadakar su, ina da qasa da ciment da komai dama ina da aniyar yin d'aki saboda ku idan kun kawo mana ziyara tinda na kula rayuwar ku ta sauya nima dole na sauya maku d'aki ko da bai kai na masu aikin ku a can ba,sai kawai muka tashi babu neman izini na na fita na dawo na ga ta riga ni,har tana yi mana taqama da fankama tare da gore-gore akan Yaran ta su 'YAN ABUJA ne matan masu kuɗi,dan haka yanzu da kaina zan gina maku d'akin naku"
Juyawa ya yi ya fita dan ba zai iya zama a gidan ba ya na gani Goggo Sarai b'acin rai na sake lullub'e shi,kamar abun wasa bayan kwana uku da yin maganar sai ga Baban su ya fara haɗa qasa da kan shi dan gina wa Yaran nashi d'aki tinda dama aikin shi ne,nan da nan Suwaiba da yan uwanta suka haɗu suna taimakawa mahaifin nasu da duk abinda za su iya,suna tsaka da aikin Ammar ya taka dugui-dugui ya isa wajen su ya deb'o qasar a hannun shi ya miqawa Baban su, dariya suka yi gaba ɗayan su, a haka Ammar ya zama shi ne ke saka su nishad'i har yamma ta gabato sannan suka tashi suka bar wajen dan wanke Jikin su da yin alwalar sallar magariba.
Mama Bilki ko tana can tana masu girki har ta kammala,Hajiya Goggo mai jiran gadon tafiya Makka kuwa ba wanda yake kula da yin ta yanzu a gidan tun bayan dawowar suwaiban,babu mai kula da kukan ta balle a lallashe ta.
Gaba ɗaya sun maida hankali akan gina d'akin da zasu nesanta kan su da ita, dan kuwa har sun ɗora foundation, gaba ɗayan su tattare wa suka yi suka zauna bangaren Mama Bilki, wadda yau kusan kwana uku da dawowar suwaiba duk yanda za ta yi ta nuna masu rashin dacewar abinda suke yi ta yi amma sun qi jin maganar ta.
Yauma a babban faranti Mama ta zuba masu abinci kamar kullum, kowa ya saka hannu har Baban su suka fara ci, Mama Bilki ce ta miqe Baba ya kalle ta ya ce,
" Ina zaki kuma Gimbiya?"
" Baban su zan je na kira Yaya ne, mu ci abincin dika"
Gaba ɗayan su yaran sai suka zare hannayen su a abincin suna kallon ta tare da turo baki alamar basu yarda ta kirawo Goggo Sarai ba,
"Ai sai ki zauna ko? Tun da dai kin samu amsar ki a wajen Yaran dan haka zauna mu ci bincin mu"
Koma wa ta yi ta zauna jiki duk ba kwari,haka suka gama ci suka wanke hannayen su suka sha ruwa, wanke farantin Saudat ta yi ta ajiye a kwandon wanke-wanke ta dawo suka zauna suna ta hira, suna wasa da Ammar,
" Mama Ammar ya girma ya yi wayo sosai"
In ji suwaiba da ke kallon shi cike da soyayyar da bata taɓa zatan haka ake ji akan 'yan uwa wanda aka fito ba daga ciki ɗaya ba, a zaton ta 'yan d'akin su ne kaɗai 'yan uwan ta da zata so bayan su ba wata soyayyar d'an uba, Goggo ce ta yi murmushi ta ce,
" Aiko dai kinga dik sa'annin shi ya fisu girma da wayo, har yaron maqotan nan namu da ya bashi wata biyu Ammar ya fi shi wayo"
"Lallai kam ga alama nan na gani"
Mama Balki ce ta nisa kafin ta ce,
" Suwaiba, Saudat, Salma ina so ku bani hankulan ku nan dikan ku"
D'aga kai suka yi a tare suka kalle ta jin yanda ta ambaci sunayen su alamar babu wasa, amsawa suka yi gaba dayan su suka zuba mata ido,cikin kwantacciyar murya Mama ta ce,
" Ina son na baku shawara a matsayina na uwa, sannan ina son ku duba abinda zan faɗa maku da da kyau da kuma Kyakkyawar zuciya kuma ku qoqarta ku yi amfani da shi, kun ga da farko dai uwa ba kamar ta a rayuwar duniya, Allah ya ce abi shi sannan abi iyaye, Annabin rahama ya jaddada bin uwa sau uku kafin ya kira sunan uba, dan haka ni ina son ku yafe ma mahaifiyar ku abinda ta yi maku, tabbas bata kasance uwa ta gari ba wadda take bawa yaranta tarbiyyar da musulunci ya tanadar, amma ta baku so, ta nuna maku qauna, na uwa da yaranta, in kun kula ita a tinanin ta tayi abinda ya dace daku da rayuwar ku ne, amma koma dai menene ina son ku sani, wanda bai yafe ma wani ba, shima ya ji tsoron kar Allah ya qi yafe masa nashi laifukan, dan haka nake mai baku hakuri a madadin ta, ku taimaka ku yafe mata, kar ku ja wani ciwon ya kama ta dan Allah na roqe ku"
Cikin kuka sosai suka matsa kusa da ita suka rungume ta, Suwaiba ce ta yi magana a cikin su ta ce,
" Mama Bilki ke alkhairi ce a rayuwar mu, ki yafe mana abubuwan da muka yi maki a baya, tabbas mun cutar da ke da kalaman mu, da ayyukan mu, bamu zama yara masu biyayya ba, ki yi hakuri ki yafe mana"
"Indai nice na yafe maku, sai dai har yanzu baku ce min komai game da Yaya ba?"
Salma ce ta amsa masu dan Suwaiba da Saudat har yanzu akwai d'aci da wata irin qiyayya da suke ji game da mahaifiyar tasu, amma sun sani dole su yafe mata, su yi hakuri da abinda ta yi musu,
"Mun yafe mata Mama Allah ya yafe mana mu ma"
"To ya kamata yanzu ku je ku sanar da ita kar ta kwana cikin damuwa, na kula ko bacci bata iyawa tun ranar da ki ka dawo gidannan suwaiba"
Suwaiba ce ta yi saurin miqewa ta ce,
"Ni dai Mama ba zan iya zuwa yau ba, dan Allah kar ki tirsasa ni yin abinda ban jin zan iya yin shi a yanzu"
Ta qarasa maganar ta cikin kuka,baba ne ya ce,
"Bilkisu Allah ya miki albarka, amma ki bar su haka, zuqatan su cike yake da qunci akan abinda ta yi musu, daga baya a hankali komai zai warware masu"
"To Baban su Allah ya kaimu lokacin, Allah kuma ya sanyaya zuqatan ku ku yafe mata gaba daya har kai ɗin ma"
Amsawa suka yi dika da,
" Ameen"
Hankalin Goggo kam ya kai qololuwa wajen tashi da jin hirar Yaran nata da kishiyar ta da ta tsana nan take ta fara ganin wani irin duhu ya na lullub'e mata ganin ta,qoqari take yi ta buɗe ido da kyau ko ta yi magana amma ta kasa a hankali ta ji kan ta na juyawa har duhun da take gani ya mamaye ganin ta baki ɗaya ......
[04/08, 11:01 am] asiyahabibu93: 💅🏼 'YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HERMEEBRAERH
Page 27:
Kuka kawai talle yake ya kasa tsaida hawayen shi tsabar yanda mutuwar Jummala ta dake shi, wannan rayuwar da iyalin shi suka yi a baya ko kuma suke yi ya tabbata ba wanda ya ja ma su ita face shi, mugayen halayen shi ne da yi ma yaran mutane sakin wulaqanci da zinace-zinacen shi ne ya dawo masa ta haka.
Yau gashi an wayi gari tsabar lalacewa Yayan shi uwa ɗaya uba ɗaya ke neman matar shi ta sunna, Yaran yayan shi na neman na shi yaran, kaiii jama'a wannan wace irin musiba ce ta sauko mana a wannan zamani, Marka kam irin kukan qabilun nan ta dinga yi, ta yi girgiza ta yi girgiza sai ta kwarara ihu sai kuma caaan ta yi dif ta cigaba da gyad'a kai,itama abun ya shige ta sosai ba kadan ba, jummala ta mutu sakamakon yunqurin zubda ciki, ga Hawaila tana kallo a gaban ta da ciki dan kuyat ya fito a gaba,nata farkan kuwa na can gefe ya na jinyar dukan da ya sha, wace irin rayuwa suka jefa kansu a ciki ne ita da mijin ta da Yaran ta dika?
Maqota kowa ya zo ya yi gaisuwa sai ya tafi babu mai zama wai da sunan zaman makoki, ko sun shigo yada magana ne yake kawo su, wasu daga ciki ma cewa suke yi,
" Tohhhh abinda ya faru kenan hmmmm Allah dai ya jiqan ta amma zunubi kam an kwasa"
Ire-iren kalaman nan ne ke fitowa daga bakunan mutane suna yi suna kyab'e baki, wasu kuma bayan sun yi gaisuwar sai sun dora da cewa,
"Laaa ikon Allah kamar ciki nake gani a jikin Huwaila, ni dai bani da labarin auren ta, sannan mun san ba a shan ciki a ruwa, hmmmm Allah ya kyauta,gidan Talle kenan gidan ban mamaki, uwa ba kwab'a uba babu hantara"
Kusan kowa ya zo da abinda zai furta kafin ya tafi,baqin ciki kamar ya kashe Haule saboda ji da ganin munanan abubuwan da ke faruwa,wai yanzu nan ne gidan uban ta, gidan da babu tarbiyya ba kwab'a, banda Allah ya kare ta Itama da duk haka zata taso a lalace tinda duk abinda ke faruwa a gidan kenan,yanzu gashi wannan mummunan baƙin fentin ya shafeta, ai kuwa da an gama arba'in guduwa zata yi qauyen da ta ji wata qawar Marka da ta zo da jimawa ta faɗa acan mahaifiyar ta ke aure, qauyen baida wani nisa yana nan kusa da su ne,dan da alama idan ta ci gaba da zama a gidannan ko mashinshini rasawa za ta yi balle manemin aure, in ko ta koma can ko sunqi karb'ar ta ba zata dawo nan ba dole su sanya za su yi da ita.
Juyawa ya yi ya fita dan ba zai iya zama a gidan ba ya na gani Goggo Sarai b'acin rai na sake lullub'e shi,kamar abun wasa bayan kwana uku da yin maganar sai ga Baban su ya fara haɗa qasa da kan shi dan gina wa Yaran nashi d'aki tinda dama aikin shi ne,nan da nan Suwaiba da yan uwanta suka haɗu suna taimakawa mahaifin nasu da duk abinda za su iya,suna tsaka da aikin Ammar ya taka dugui-dugui ya isa wajen su ya deb'o qasar a hannun shi ya miqawa Baban su, dariya suka yi gaba ɗayan su, a haka Ammar ya zama shi ne ke saka su nishad'i har yamma ta gabato sannan suka tashi suka bar wajen dan wanke Jikin su da yin alwalar sallar magariba.
Mama Bilki ko tana can tana masu girki har ta kammala,Hajiya Goggo mai jiran gadon tafiya Makka kuwa ba wanda yake kula da yin ta yanzu a gidan tun bayan dawowar suwaiban,babu mai kula da kukan ta balle a lallashe ta.
Gaba ɗaya sun maida hankali akan gina d'akin da zasu nesanta kan su da ita, dan kuwa har sun ɗora foundation, gaba ɗayan su tattare wa suka yi suka zauna bangaren Mama Bilki, wadda yau kusan kwana uku da dawowar suwaiba duk yanda za ta yi ta nuna masu rashin dacewar abinda suke yi ta yi amma sun qi jin maganar ta.
Yauma a babban faranti Mama ta zuba masu abinci kamar kullum, kowa ya saka hannu har Baban su suka fara ci, Mama Bilki ce ta miqe Baba ya kalle ta ya ce,
" Ina zaki kuma Gimbiya?"
" Baban su zan je na kira Yaya ne, mu ci abincin dika"
Gaba ɗayan su yaran sai suka zare hannayen su a abincin suna kallon ta tare da turo baki alamar basu yarda ta kirawo Goggo Sarai ba,
"Ai sai ki zauna ko? Tun da dai kin samu amsar ki a wajen Yaran dan haka zauna mu ci bincin mu"
Koma wa ta yi ta zauna jiki duk ba kwari,haka suka gama ci suka wanke hannayen su suka sha ruwa, wanke farantin Saudat ta yi ta ajiye a kwandon wanke-wanke ta dawo suka zauna suna ta hira, suna wasa da Ammar,
" Mama Ammar ya girma ya yi wayo sosai"
In ji suwaiba da ke kallon shi cike da soyayyar da bata taɓa zatan haka ake ji akan 'yan uwa wanda aka fito ba daga ciki ɗaya ba, a zaton ta 'yan d'akin su ne kaɗai 'yan uwan ta da zata so bayan su ba wata soyayyar d'an uba, Goggo ce ta yi murmushi ta ce,
" Aiko dai kinga dik sa'annin shi ya fisu girma da wayo, har yaron maqotan nan namu da ya bashi wata biyu Ammar ya fi shi wayo"
"Lallai kam ga alama nan na gani"
Mama Balki ce ta nisa kafin ta ce,
" Suwaiba, Saudat, Salma ina so ku bani hankulan ku nan dikan ku"
D'aga kai suka yi a tare suka kalle ta jin yanda ta ambaci sunayen su alamar babu wasa, amsawa suka yi gaba dayan su suka zuba mata ido,cikin kwantacciyar murya Mama ta ce,
" Ina son na baku shawara a matsayina na uwa, sannan ina son ku duba abinda zan faɗa maku da da kyau da kuma Kyakkyawar zuciya kuma ku qoqarta ku yi amfani da shi, kun ga da farko dai uwa ba kamar ta a rayuwar duniya, Allah ya ce abi shi sannan abi iyaye, Annabin rahama ya jaddada bin uwa sau uku kafin ya kira sunan uba, dan haka ni ina son ku yafe ma mahaifiyar ku abinda ta yi maku, tabbas bata kasance uwa ta gari ba wadda take bawa yaranta tarbiyyar da musulunci ya tanadar, amma ta baku so, ta nuna maku qauna, na uwa da yaranta, in kun kula ita a tinanin ta tayi abinda ya dace daku da rayuwar ku ne, amma koma dai menene ina son ku sani, wanda bai yafe ma wani ba, shima ya ji tsoron kar Allah ya qi yafe masa nashi laifukan, dan haka nake mai baku hakuri a madadin ta, ku taimaka ku yafe mata, kar ku ja wani ciwon ya kama ta dan Allah na roqe ku"
Cikin kuka sosai suka matsa kusa da ita suka rungume ta, Suwaiba ce ta yi magana a cikin su ta ce,
" Mama Bilki ke alkhairi ce a rayuwar mu, ki yafe mana abubuwan da muka yi maki a baya, tabbas mun cutar da ke da kalaman mu, da ayyukan mu, bamu zama yara masu biyayya ba, ki yi hakuri ki yafe mana"
"Indai nice na yafe maku, sai dai har yanzu baku ce min komai game da Yaya ba?"
Salma ce ta amsa masu dan Suwaiba da Saudat har yanzu akwai d'aci da wata irin qiyayya da suke ji game da mahaifiyar tasu, amma sun sani dole su yafe mata, su yi hakuri da abinda ta yi musu,
"Mun yafe mata Mama Allah ya yafe mana mu ma"
"To ya kamata yanzu ku je ku sanar da ita kar ta kwana cikin damuwa, na kula ko bacci bata iyawa tun ranar da ki ka dawo gidannan suwaiba"
Suwaiba ce ta yi saurin miqewa ta ce,
"Ni dai Mama ba zan iya zuwa yau ba, dan Allah kar ki tirsasa ni yin abinda ban jin zan iya yin shi a yanzu"
Ta qarasa maganar ta cikin kuka,baba ne ya ce,
"Bilkisu Allah ya miki albarka, amma ki bar su haka, zuqatan su cike yake da qunci akan abinda ta yi musu, daga baya a hankali komai zai warware masu"
"To Baban su Allah ya kaimu lokacin, Allah kuma ya sanyaya zuqatan ku ku yafe mata gaba daya har kai ɗin ma"
Amsawa suka yi dika da,
" Ameen"
Hankalin Goggo kam ya kai qololuwa wajen tashi da jin hirar Yaran nata da kishiyar ta da ta tsana nan take ta fara ganin wani irin duhu ya na lullub'e mata ganin ta,qoqari take yi ta buɗe ido da kyau ko ta yi magana amma ta kasa a hankali ta ji kan ta na juyawa har duhun da take gani ya mamaye ganin ta baki ɗaya ......
[04/08, 11:01 am] asiyahabibu93: 💅🏼 'YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HERMEEBRAERH
Page 27:
Kuka kawai talle yake ya kasa tsaida hawayen shi tsabar yanda mutuwar Jummala ta dake shi, wannan rayuwar da iyalin shi suka yi a baya ko kuma suke yi ya tabbata ba wanda ya ja ma su ita face shi, mugayen halayen shi ne da yi ma yaran mutane sakin wulaqanci da zinace-zinacen shi ne ya dawo masa ta haka.
Yau gashi an wayi gari tsabar lalacewa Yayan shi uwa ɗaya uba ɗaya ke neman matar shi ta sunna, Yaran yayan shi na neman na shi yaran, kaiii jama'a wannan wace irin musiba ce ta sauko mana a wannan zamani, Marka kam irin kukan qabilun nan ta dinga yi, ta yi girgiza ta yi girgiza sai ta kwarara ihu sai kuma caaan ta yi dif ta cigaba da gyad'a kai,itama abun ya shige ta sosai ba kadan ba, jummala ta mutu sakamakon yunqurin zubda ciki, ga Hawaila tana kallo a gaban ta da ciki dan kuyat ya fito a gaba,nata farkan kuwa na can gefe ya na jinyar dukan da ya sha, wace irin rayuwa suka jefa kansu a ciki ne ita da mijin ta da Yaran ta dika?
Maqota kowa ya zo ya yi gaisuwa sai ya tafi babu mai zama wai da sunan zaman makoki, ko sun shigo yada magana ne yake kawo su, wasu daga ciki ma cewa suke yi,
" Tohhhh abinda ya faru kenan hmmmm Allah dai ya jiqan ta amma zunubi kam an kwasa"
Ire-iren kalaman nan ne ke fitowa daga bakunan mutane suna yi suna kyab'e baki, wasu kuma bayan sun yi gaisuwar sai sun dora da cewa,
"Laaa ikon Allah kamar ciki nake gani a jikin Huwaila, ni dai bani da labarin auren ta, sannan mun san ba a shan ciki a ruwa, hmmmm Allah ya kyauta,gidan Talle kenan gidan ban mamaki, uwa ba kwab'a uba babu hantara"
Kusan kowa ya zo da abinda zai furta kafin ya tafi,baqin ciki kamar ya kashe Haule saboda ji da ganin munanan abubuwan da ke faruwa,wai yanzu nan ne gidan uban ta, gidan da babu tarbiyya ba kwab'a, banda Allah ya kare ta Itama da duk haka zata taso a lalace tinda duk abinda ke faruwa a gidan kenan,yanzu gashi wannan mummunan baƙin fentin ya shafeta, ai kuwa da an gama arba'in guduwa zata yi qauyen da ta ji wata qawar Marka da ta zo da jimawa ta faɗa acan mahaifiyar ta ke aure, qauyen baida wani nisa yana nan kusa da su ne,dan da alama idan ta ci gaba da zama a gidannan ko mashinshini rasawa za ta yi balle manemin aure, in ko ta koma can ko sunqi karb'ar ta ba zata dawo nan ba dole su sanya za su yi da ita.