← Book details Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 71

Sashe 50

Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kada kayi tunanin zakayi wasa da abubuwan dake hannun ka, domin duk abinda kuka tattauna kaida Ubandoma ina jinku kuma nayi recording na komai a wayana, harna turawa aminaina ta whatsapp kusan su goma, yazame maka dole kayi duk abinda nakeso batare dako k'wandala ba kuma idan bakayi ba, in wulak'antar mafarin ka" jikin d.p.o yana rawa yace

"Yallab'ai babu yanda xanyi da matsalar Yallab'ai Ubandoma, idan ma banyiba ze b'ullo ne ta wata sigar" Gyaran zama yayi kafin yace

"Daga yanzu duk abinda nace ka gaya masa shi zaka gaya masa, sannan kuma duk abinda ya gaya maka kake gayamun ta hanyar lambar wayar dazan baka b'oyayyiya sabida a wannan suna bibiya ta, na biyun sa kuma wlh idan ka sake wanima yaji nazo nan wurin ko naji hirarrakinku senayi mafarin rufe ganin ka da k'asa" Nan take ya amsa da angama ya rufa masa asiri kodan aikin sa, sun tattauna sosai ya samu sirrikan su kafin ya buk'aci ganawa da Hafsa inda kai tsaye suka gabatar masa da ita har offishin D.P.O

Mik'ewa yayi tsaye ya matso da sauri inda take ya kama hannunta inda atake D.P.O ya basu wuri, hannunta yake murzawa wanda yaga alamun shatin sanda rud'u rud'u ajiki cikin tashin hankali ya kalleta

"Waye ya dakeki a hannu haka? Murmushi tayi ta shafi k'afad'arsa

"Ya raunin hannun ka, harbi da zafi ko? Sannu yaa mood, hankalina yana wurin ku kaida Me matraba da wannan Muhseen d'in" K'ara shafa hannun ta yayi sannan yace

"Cewa nayi waye ya dakeki Hafsah? Murmushi tayi kafin tace

"D.P.O naji kaman suna kiransa ko, so yake ince nice na saka a kasheku, tayaya zan amsa laifin daba nawa ba, kuma tayaya zance nasa akashe mahaifina da mijina? Kuma kaga dukan nan Allah da zafi" kawai seta soma sheshekar kuka ga alama dama kukan takeso tayi tuni amma taurin kai ya hanata tayishi agaban su, iskar bakinsa yasanya yana hure mata hurin da hannunta ya tashi cikin kulawa

"Dame ya dakeki? Tab'e baki tayi irin na yara

"Sanda ne babba baka ganshi ba, niba abinda na masa so suke su kasheni, nace su kasheni amma ni kowa yasanni bana k'arya bakuma zan fara k'aryaba sabida karsu dakeni" Zuciyarsa tazo masa iya wuya yama rasa mezeyi kallon juna sukeyi kowa da abinda yake sak'awa har lokacin kuka take, k'ara kallon ranin yayi farcenta d'aya harya kumbura

"Shidawa yazo? Ya tambaya yana k'ara hura mata iska agun

"Baba Usman ne, shugaban k'ungiyar aci ta duhu da fada"

"Ya akayi kika san shine" Tana me share k'walla da gefen kafad'arta sabida ya rik'e hannayenta tace

"Dama inaso in gaya maka komai kafin su kasheni" Had'e jikin sa yayi da nata

"Kisa wai kike magana, kinada hankali kuwa? Waye ze kasheki? Kukan ta ta k'arawa sauti

"Wannan mutumin da suke kira DPO wanda ya kawoni nan dakuma Baba Usman sune sukace sauramun kwana uku a kasheni" Runtse idansa yayi sanya fahimci sunyi nasarar tsoratar da ita, k'ara matseta yayi da hannun sa me lafiya

"Babu wanda ya isa ya kasheki ina numfashi, k'yalesu kedai duk abinda kika sani ki sanar dani"zare jikinta tayi a nasa sannan tace

"Wani zezo na aminta da aikinsa da gaskiyar sa sunansa Detective Sufyan Data, munyi akan zece dasu zeje dani special investigation centre nasu ya tuhumeni, amma gun matarsa ze kaini, inada manyan shaidu awurin wani dakuma kaina, ze taimakeni yace inna gaya masa komai ze fitar dani lafiya" kallonta yayi

"Nasan Data ai, dama dashi ne naso in had'a yayi mana bincike, zan masa waya yaxo ku tafi, gidansa akwai tsaro ba abinda ze sameki acen, amma kinsan wannan dukan da aka miki sena rama, Allah har Baba usman sena saka ammasa fiye da wannan" Murmushi tayi tana kallon sa

" Laa Babba ne fa? Shima dariya ta bashi yace yana kallon ta

"Hafsah mesa kika sanya rayuwarki a hatsari har haka, mesa baki tab'a yimun bayani akan komai ba, se Uncle Jay ne ya gayamun komai da komai d'azu" tana kallon sa ta shagwab'e fuska

"Kaine kace baka sona ai, kuma ka tsaneni, Bahar kad'ai ke sona se Ummi" Murmushi yayi kome yasa wowtar Hafsah take burgeshi?

Mom Nu'aiym.

*TSINTAR AYA*  FREE BOOK

    *BILLY GALADANCHI*

*SHAFI NA ASHIRIN DA SHIDA*
26.

Sanye ajikinta wata farar rigace shara shara me santsi, ta tufke gashin kanta a tsakiya, ta sanya wata shara sharar hula itama fara akanta, fatarta dake shek'in wani haske tana asalin glowing abar d'aukar hankali takai hannu ta murza gefen fuskarta lokaci d'aya tana lumshe idon ta

"Yaa Sufyan bacci nakeji, tara ya gota fa, kake shirin fita? Hannun sa yakai ya tallafota jikinsa daidai kunkurunta

"Laurah wannan babban al'amari ne daya zamar mun dole senayi fitar dare, a k'aida kowa yasan 8 ana gama sallan isha ina gida, to wannan fitar basaja ne kin gane? Nisawa tayi kafin tace

"Dabadan kayi nasarar tarwatsa gidan madubi ba, da bazan barka kafita ba, amma duba da yanayin sharrin dakafi k'arfin sa na tabbatar kaime bautar Allah ne, da wannan nakeda hak'ik'a akan cewar aduk inda kake Allah mabuwayi yana tare dakai" Sumba yakai mata a agoshi sabida yanayin gajarta irin nata yana dariya yace

"Acikin shekaru hud'u Laurah baki ya bud'e, girma ya kawo kanshi" Zame jikinta tayi tana murmushi sannan tace

"K'waila tasha raino zakace" sarai yasan neman maganar sa take amma bebi ta kanta ba, murmushin sa kawai yake yafita yabar gidan.

Ta k'ofar baya yabi, wata iriyar k'oface ta sirri wacce bazaka tab'a sanin akwaita awurin ba, Likitan yaso shammaz (Littafin Sa'a) shine yabi dare ya gina masa wannan k'ofar ta sirri... yayi tafiyar kusan mintuna goma kafin ya isa wurin wata motar ya bud'e ta ya shiga batare da yayi magana ba, kai tsaye police station ya nufa inda ya tarar D.P.O anata rafka gumi yana bakin kantarsu a tsaye, hannu ya mik'a masa suka gaisa sannan yace

"Detective Data" D.P.O ana muzurai akace

"Na gane sosai sir" hular daya sako wacce ke had'e da riga ya ture taje bayan wuyansa"

"Inaso zanyi magana da suspect tamu" Muryansa yana rawa

"What is the use? Tana tare da prince hammood shisam be yadda akan ita bace take neman ransu" Murmushi Data yayi

"Interesting, haka ma wani babban taimakon ne, because inaso nayi bincike da tushe, and right now am taking the suspect with me" kallon sa cikin tashin hankali

"Wai yallab'ai mesa baka tab'a bari muyi aikin mune? Waya turo ka kuma wannan karon" K'ank'ance idansa yayi

"C.P Mai doki ne ya turoni (ACP mai doki yake magana na littafin gidan madubi, yanzu ya tashi daga ACP ya zama babba shine commissioner.) Sosa k'eya D.P.O yayi kafin yace

'If that is the case, i will like to help" Murmushi yai masa

"Kai D.P.O Maharazu ka san waye ni kuwa? Bana son taimakon ka kamar yanda banason shishigi, wannan aikine na intelligence agency me zaman kansa, ka gayawa masu baka wasu kud'i kana shirin murd'e al'amura suyi hankali da kansu, maza abisa kansu inada tarin dukiya bazasu iya sayana ba, inada tarin gaskia k'aryarsu bazata rikitar dani ba, inada tarin basira datafi k'arfin masharranciyar basirar su, now lead the way? Juyawar dazasuyi sega Hammood a fusace janye da hannun Hafsat kallon A.C.P yayi sannan yace

"Waye acikin ku yakai hannun sa ajikin matana saraki ce fa? Kallon tuhuma duk yaran sukayiwa ogansu sannan wani jikinsa yana rawa yace

"Amun aikin gafara yallab'ai nine na daketa, alokacin anata so tayi magana tak'i tayi" Da mamaki Hafsa ta kalle sa, sannan ta narke fuskarta cikin shagwab'a tace

"Allah sarki me k'arya d'an wutane fa, wancen ogan nasu shine ya samu sandar sa me zafin tsiya, ya d'aura hannayena asaman bench ya dinga rotsamun seda na suma na farfad'o" ta k'arashe maganar tana sauke fuskarta asaman d'aya kafad'ar hammood me lafiya, hannun sa yakai yana patting bayan ta a hankali

"Koma waye wlh sena rama mata, sekunci ubanku a hannuna 'yan sandan kawai, kune kuke b'ata mana k'asa, haka ake bincike inaga ta kanku zan fara" Data ne ya matso ya mik'a masa hannu sukati musabaha sannan yace

"Ranka ya dad'e babban son ya akayi kazo nan bayan raunin dake jikin ka haka? Murmushi yayi cikin girmamawa sanin cewar Babban abokin Uncle Jay kenan ya sanya yace

"Am sorry Uncle Sufyan, hankali na yana kan yarinyar nan, she sacrifice alot for her family, and mak'iya are busy trying to accuse her of something big as this, yarinya da kind soul irin hakan nan ai gobe bazataji dad'in k'ara taimakon kowa ba" Nisawa Data yayi

"Polisawan k'asar nan gaba d'ayan su kaso 75 acikinsu sunada raunin saitin kai, Allah kad'ai ze mana maganin su" Anan suja tattauna kafin su shiga mota subar gidan, gaba d'ayan su gidan Data suka isa ata wannan b'oyayyiyar k'ofar. Da kansa yayi kiran matarsa lokacin 11. Yayi tazo ta gayar da Hammood yana mata murmushi yace

"Ga d'an gidan Jay fa, yaran da ake xuwa aita mana kuka akan sa, kai Jay wlh ya iya shak'iyan ci, shida matar sane, tana buk'atar taimakon ki Anty Laurah matar Data" Murmushi tayi

"Yanzu nice anty dan Allah? Ta furta tana shagwab'a, dariya yayi "Jibi zatayi 18yrs ina ke harkin cinye cake naki na 19, so ke antyn tane ai ko yaya? Murmushin ta ta k'arawa fad'i

"Hakane na zama anty, yanxu ina muka kwana,?" Murmushi yayi

"So nake ki nutsu mu saurari labarin ta" gyaran zaman ta tayi kafin tace "Malama Hafsat Bismillah" Seda tayi gyaran murya sannan tace
Chapter 50 · 0% Book details