Sashe 3
Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yanzu hajiya ace yarinyar dakika rik'a tsakani da Allah dukda abinda ubanta da uwarta suka aikata kika taimaketa da mugun sharrin dazata biki kenan? me kika tsare mata arayuwa? maganar bazan iya gaya miki itaba sabida nauyinta amma ita tazo ta maimaita da bakinta" Jikin 'yar shara (Hafsat) ne ya fara rawa sosai sabida tsoro ta k'ure a toilet anata kiranta amma bata fitoba, seda momy taje ta fincikota sannan ta fito tanata zare ido, Baba Lami tace
"Ke 'Yar sha maimaita abinda kikazo kika gayamun Hajiya da yaro sunayi agidan nan" Jikinta rawa yakeyi sosai yanzu kam har fitsari ya soma fito mata tace
"Baba Lami dan Allah ki rufamun asiri" Mari Baba Lami takai mata
"Na rufa miki asiri kamar yaya? kina neman tona mana asiri kice in rufe naki, kimga hajiya zuwa tayi tana gayamun waikeda yaro Lalata kukeyi kullum cikin dare nan yake kwana sanda bama nan" Da mamaki momy ta kalli'Yar sha sannan tace
"Hoo yaron zamani, Lallai na yarda duniya tayi gurb'acewar dabazata gyaruba sesa gyaran Allah, kokin san dabakwa nan bilal k'ararta ya kawomun, fita takeyi idan na fita na zaneta namata fad'a shine zaki dawo da sharrin akanmu? ko shakka banayi wannan yarinyar dalilin kenan dayasa mutan garinsu ma bame sonta, amma ni bazance miki komai ba, bari Bilal yazo ya maidaki garinku tunkan kinb'atan suna agari, aniyarki ta biki Yar shara" Haka suka tasata agaba da uwar Bilal da momy suka mata tatas!
kuka ta kwanayi a wannan daren babu k'auk'autawa, washe gari bilal da duka ya tashi mata tamkar ze kashe ta, haka suka fita akan ze kaita garinsu insunso su kasheta, ita tasan cewar bilal baze barta ta rayu a farin cikiba, tanada yak'inin cewan abinda yakeso ajikimta baze hak'uraba harse ya karb'a.
*MOM NU'AIYM.*
*TSINTAR AYA* FREE BOOK.
*BILLY GALADANCHI*
*Sak'on gaisuwa zuwaga Babbar Antyna, mace me karamci kuma me girmama, babba da yaro, Alkhairin Allah yakai miki a duk inda kike Anty mejidda musa*
*Makaranta Littafin tsintar Aya nagode da rububin son dakuka nuna masa tun a shafin farko, Allah yabar k'auna.*
*SHAFI NA BIYU*
Dariya ya kwashe da ita sanda ta shigo motar jikinta yana b'ari, sanda ya fita a gidan ya saisaita kan motar sosai akan titi sannan ya waigo ya kalleta yana wani kashe ido
"Tsuntsu daga sama gashashe, wato lallai 'yar sha bakida hankali, tsammani kike wai Baba zata tab'a yadda da zancenki,kokuma kina tsammanin kamar akwai abinda ze tab'a hanani cimma burina akanki, wlh sekin gane kurenki a hannuna" Batace masa komai ba banda kukan datake kanta asaman cinyoyinta.Batayi tsammanin cewa zekaita garin nasu ba, amma ga mamakinta setaga ya d'auki hanyar garin nasu se faman wak'e wak'en sa yakeyi tamkar wanda akawa bushara da gidan aljanna!
Harsuka isa be kuma koda kallon inda take ba, gidan nasu babban gidane sosai me yalwar shiguhu kala kala, kana kuma ko wane b'angaren bayan ka wuce shiguhun runface ta bunu da kuma d'akuna wasu ginin laka wasu kuma bukka ce, tsarin gidan kana ganinsa zaka shaida cewar irin gidan daya had'a dukka kowa da kowa ne, ma'ana Extended family.... Tun a soro na k'arshe Bilal yake rafka sallama har ya bazama cikin gidan, harya cire rai da za'a amsa masa sekuma kaman daga sama ya soma ganin mutane tamkar ana yayyafin su suna fitowa, Atare d'aukacin mutanen wurin suka had'a baki wurin ambatar 'yar shara! wanda hakan ba k'aramin k'ara rikitar da ita yayi ba cikin tsananin firgici take kallon kowa idan ta ya sauka akan Baba jere daya tsatsareta da ido tamkar ze cinyeta d'anya. Bilal gaggaisawa yayi da mazan ta hanyar musabaha sannan yace
"Hajiya Barira ce tamun umarni akan in dawo da 'Yar shara gida, tace in sanar daku kuyi hak'uri da k'in zuwan datayi da kanta ta dawo da ita, tanajin kunyar kune ta kasa rik'eta kamar yanda tayi alk'awari, tace hakan ya biyo bayan cikin shegen dake jikin 'Yar shara ne harna tsawo wata biyu, bazata iya abun kunya ba ita kam, sabida haka na dawo da ita tushiyar ta" Tas wurin ya d'auki salati yayinda lokaci d'aya duniyar ta soma juyawa da 'yar shara tana shawagi da ita, wannan wane mummunan k'azafi ne Bilal yake shirin manna mata, sama sama tajiyo muryar Baba jere yana cewa
"Kayi tafiyar ka Bilal, zamu mata hukuncin daya dace da ita" Haka.ta ruk'unk'une wuri d'aya tana gunjin kuka amma sam ta kasa magana har Bilal ya juya sekuma ya dawo kusa da ita ya sunkuya ya ajiye mata wata leda, ga kati nan ajiki lambar wayana, idan azaba tayi azaba kika yanke hukuncin bani kanki seki nemeni a waya kud'ine acikin wannan biredin sekiyita tattalinsa dan nasan kwana bazaki k'ara agarin nan ba zasu koraki" Batace masa komai ba, babu kuma wanda yaji maganar dasuke se ita kad'ai sabida yanda yazo daf da ita yana magana k'asa k'asa...... Haka ya tafi banda kuka babu abinda 'Yar shara takeyi.Kallon tsana Baba jere yabita dashi sannan yace
"'Yar k'wai bani kayan wuta da alamar k'ira" Inna suwai ce tayi azamar kallon sa, murya yana rawa tace
"Jere me zakayi? kallon ta shima yayi
"Bakiji tayi shege ba, yanda nayi da ubanta haka itama zan mata" Idanta ne ya kawo ruwa babu musu ko gaddama a atsakanin su, babu wanda yake ja da hukuncin jere shine me garin garin gaba d'aya kuma biyayya agaresa batada hijabi awurin su dole sesunyi jikinta yana karkarwa ta zube akan gwiwowinta
"Jere ka dubi girman Allah ka sassauta mata, karka manta azabar k'irane yayi sanadin Djoro, kabar 'Yar shara itakam ita kad'ai ne a tsatson Djoro dazan kalla inji sanyi" Wani kallo ta wurga mata yanzu a hautsine
"Bana buk'atar tsatson Djoro a zuri'a ta, Yanda Allah ya kashe Djoro Allah ya kashe D'iyatai daya bari, Idan zan mata k'ira har a tafukan hannayenta zan manna mata sabida azaban wutan yajewa d'an shegen dake shikinta shima ya mutu atare da ita" Kuka ta saka da iyakacin k'arfin ta ruga ta rungume 'yar shara, zuwa lokacin da aka kawo kayan k'ira aka hura huta aka soma d'o'd'in k'arfen iyakacin gigicewa Hafsat ta gigice, batasan me ma'anar hakan ba, amma menene ya kashe mahaifinta ance rashin lafiya yayi, itama ciwon zasu zasu saka mata kome? k'aramar akwatinta ta janyo ta cura wayarta aciki sannan a hankali ta ware biredin nan ta zaro kudinta ta cura a rigar mamanta tanabin kowa da kallo, katin da lambar wayar Bilal yake aciki ma sanda ta d'auka ta adana ajikinta se zare ido take, batasan me za'a mata ba amma tabbas tasan akwai alamun zata dauki yar mitsitsiyar akwatinta ta kwasa aguje inhar ya kasance azabace! Lokacin da k'arfen yayi azabar zafi se wasu maza tagani datakeda yak'inin yan uwanta ne sukazo suka daddafeta tun a nan ta soma ihu mik'ar da k'afarta akayi aka dafe Jere ya daddage ya manna mata k'arfen a tsakiyar tafin k'afarta!!! Wata uwar k'ara data k'walla tsabar azaba seda ta saki fitsari a wando ba shiri, haka ya mata tambari biyu a kowace k'afa zuwa wannan lokacin ta suma batasan inda kanta yake ba, k'ara dafa k'arafan yake yana ik'irarin manna mata a hannu Inna suwai ta rungumeshi tana kuka akan yabar ta a haka, kallon ta yayi yana yamutsa fuska
"kona manna mata kokuma akaita kan hanya ta kama gabanta" Dama bata saka ran ze barta ta zauna ba dan haka da sauri ta amince akan a koretan tasan koba jima koba dad'e zata nemi gida, koda babu ransu kuwa. Kallon masu dafeta yayi yace
"Ko inuwar wannan karku barmun agidana, ku fita da ita daga garin nan kuje cen bakin titi ku ajiyeta itada kayan ta da komanta" Haka suka amsa masa suka kwasheta a some ita da kayan ta, akan hanyar su aka soma ruwan sama ga duhu ya soma sauka wannan ya sanya babu wata tazara da garin suka ajiyeta suka ajiye mata akwatinta suka juya inda anan dukan ruwan sama ya dawo da ita cikin hayyacin amma seme ta farka cikin tsananin azaba da radad'i sannan babu akwatin kayanta a ranta ta ayyana acen aka kwace mata, ta godewa Allah daya sanya bata saka kud'inta a jakar ba, amma me tana lalubar rigar mamanta seta ji wayam! bata sani wad'an nan yan uwan nata sunga sanda ta saka kud'i a wurin, sune suka zace wayarta da kud'in suka barta da akwati wanda kafin ta farfad'o wani mara imani ya kwace. Babu takalmi a k'afarta batasan ammata lahani ba seda ta mik'e nan take ta zube awurin sabida wata sabuwar azabar data ziyarce ta ga ruwa ana tsulawa ga dare yayi, kukan ma a wannan lokacin gagararta yayi, jefi jefi motoci suke wucewa gata a gurfane bazata iya taka k'afarta ba bare ta saka musu hannu su taimaketa!
**************
*Washe gari*
Anan ta kwana cikin tsananin radad'i da fargaba me tsanani, ilahirin ruwan akanta ya kare a gindin wata bishiya, da asuba ma se taimama tayi tayi salla a zaune, har azahar ba yalwar mutane akan titin, tunanin abinyi takeyi ga azabar k'unar dake tafin k'afarta, haka ta mik'e tanaji tana gani ta soma tafiya akan duga duganta inda wutar bata kaiba, haka tayita tafiya se la'asar ta samu wata motar yaji ta d'auketa asama nanma da k'yar ta samu hawa sabida wuyar datake ciki,tare da alk'awarin zata bashi Naira hamsin idan sun isa gari.
"Ke 'Yar sha maimaita abinda kikazo kika gayamun Hajiya da yaro sunayi agidan nan" Jikinta rawa yakeyi sosai yanzu kam har fitsari ya soma fito mata tace
"Baba Lami dan Allah ki rufamun asiri" Mari Baba Lami takai mata
"Na rufa miki asiri kamar yaya? kina neman tona mana asiri kice in rufe naki, kimga hajiya zuwa tayi tana gayamun waikeda yaro Lalata kukeyi kullum cikin dare nan yake kwana sanda bama nan" Da mamaki momy ta kalli'Yar sha sannan tace
"Hoo yaron zamani, Lallai na yarda duniya tayi gurb'acewar dabazata gyaruba sesa gyaran Allah, kokin san dabakwa nan bilal k'ararta ya kawomun, fita takeyi idan na fita na zaneta namata fad'a shine zaki dawo da sharrin akanmu? ko shakka banayi wannan yarinyar dalilin kenan dayasa mutan garinsu ma bame sonta, amma ni bazance miki komai ba, bari Bilal yazo ya maidaki garinku tunkan kinb'atan suna agari, aniyarki ta biki Yar shara" Haka suka tasata agaba da uwar Bilal da momy suka mata tatas!
kuka ta kwanayi a wannan daren babu k'auk'autawa, washe gari bilal da duka ya tashi mata tamkar ze kashe ta, haka suka fita akan ze kaita garinsu insunso su kasheta, ita tasan cewar bilal baze barta ta rayu a farin cikiba, tanada yak'inin cewan abinda yakeso ajikimta baze hak'uraba harse ya karb'a.
*MOM NU'AIYM.*
*TSINTAR AYA* FREE BOOK.
*BILLY GALADANCHI*
*Sak'on gaisuwa zuwaga Babbar Antyna, mace me karamci kuma me girmama, babba da yaro, Alkhairin Allah yakai miki a duk inda kike Anty mejidda musa*
*Makaranta Littafin tsintar Aya nagode da rububin son dakuka nuna masa tun a shafin farko, Allah yabar k'auna.*
*SHAFI NA BIYU*
Dariya ya kwashe da ita sanda ta shigo motar jikinta yana b'ari, sanda ya fita a gidan ya saisaita kan motar sosai akan titi sannan ya waigo ya kalleta yana wani kashe ido
"Tsuntsu daga sama gashashe, wato lallai 'yar sha bakida hankali, tsammani kike wai Baba zata tab'a yadda da zancenki,kokuma kina tsammanin kamar akwai abinda ze tab'a hanani cimma burina akanki, wlh sekin gane kurenki a hannuna" Batace masa komai ba banda kukan datake kanta asaman cinyoyinta.Batayi tsammanin cewa zekaita garin nasu ba, amma ga mamakinta setaga ya d'auki hanyar garin nasu se faman wak'e wak'en sa yakeyi tamkar wanda akawa bushara da gidan aljanna!
Harsuka isa be kuma koda kallon inda take ba, gidan nasu babban gidane sosai me yalwar shiguhu kala kala, kana kuma ko wane b'angaren bayan ka wuce shiguhun runface ta bunu da kuma d'akuna wasu ginin laka wasu kuma bukka ce, tsarin gidan kana ganinsa zaka shaida cewar irin gidan daya had'a dukka kowa da kowa ne, ma'ana Extended family.... Tun a soro na k'arshe Bilal yake rafka sallama har ya bazama cikin gidan, harya cire rai da za'a amsa masa sekuma kaman daga sama ya soma ganin mutane tamkar ana yayyafin su suna fitowa, Atare d'aukacin mutanen wurin suka had'a baki wurin ambatar 'yar shara! wanda hakan ba k'aramin k'ara rikitar da ita yayi ba cikin tsananin firgici take kallon kowa idan ta ya sauka akan Baba jere daya tsatsareta da ido tamkar ze cinyeta d'anya. Bilal gaggaisawa yayi da mazan ta hanyar musabaha sannan yace
"Hajiya Barira ce tamun umarni akan in dawo da 'Yar shara gida, tace in sanar daku kuyi hak'uri da k'in zuwan datayi da kanta ta dawo da ita, tanajin kunyar kune ta kasa rik'eta kamar yanda tayi alk'awari, tace hakan ya biyo bayan cikin shegen dake jikin 'Yar shara ne harna tsawo wata biyu, bazata iya abun kunya ba ita kam, sabida haka na dawo da ita tushiyar ta" Tas wurin ya d'auki salati yayinda lokaci d'aya duniyar ta soma juyawa da 'yar shara tana shawagi da ita, wannan wane mummunan k'azafi ne Bilal yake shirin manna mata, sama sama tajiyo muryar Baba jere yana cewa
"Kayi tafiyar ka Bilal, zamu mata hukuncin daya dace da ita" Haka.ta ruk'unk'une wuri d'aya tana gunjin kuka amma sam ta kasa magana har Bilal ya juya sekuma ya dawo kusa da ita ya sunkuya ya ajiye mata wata leda, ga kati nan ajiki lambar wayana, idan azaba tayi azaba kika yanke hukuncin bani kanki seki nemeni a waya kud'ine acikin wannan biredin sekiyita tattalinsa dan nasan kwana bazaki k'ara agarin nan ba zasu koraki" Batace masa komai ba, babu kuma wanda yaji maganar dasuke se ita kad'ai sabida yanda yazo daf da ita yana magana k'asa k'asa...... Haka ya tafi banda kuka babu abinda 'Yar shara takeyi.Kallon tsana Baba jere yabita dashi sannan yace
"'Yar k'wai bani kayan wuta da alamar k'ira" Inna suwai ce tayi azamar kallon sa, murya yana rawa tace
"Jere me zakayi? kallon ta shima yayi
"Bakiji tayi shege ba, yanda nayi da ubanta haka itama zan mata" Idanta ne ya kawo ruwa babu musu ko gaddama a atsakanin su, babu wanda yake ja da hukuncin jere shine me garin garin gaba d'aya kuma biyayya agaresa batada hijabi awurin su dole sesunyi jikinta yana karkarwa ta zube akan gwiwowinta
"Jere ka dubi girman Allah ka sassauta mata, karka manta azabar k'irane yayi sanadin Djoro, kabar 'Yar shara itakam ita kad'ai ne a tsatson Djoro dazan kalla inji sanyi" Wani kallo ta wurga mata yanzu a hautsine
"Bana buk'atar tsatson Djoro a zuri'a ta, Yanda Allah ya kashe Djoro Allah ya kashe D'iyatai daya bari, Idan zan mata k'ira har a tafukan hannayenta zan manna mata sabida azaban wutan yajewa d'an shegen dake shikinta shima ya mutu atare da ita" Kuka ta saka da iyakacin k'arfin ta ruga ta rungume 'yar shara, zuwa lokacin da aka kawo kayan k'ira aka hura huta aka soma d'o'd'in k'arfen iyakacin gigicewa Hafsat ta gigice, batasan me ma'anar hakan ba, amma menene ya kashe mahaifinta ance rashin lafiya yayi, itama ciwon zasu zasu saka mata kome? k'aramar akwatinta ta janyo ta cura wayarta aciki sannan a hankali ta ware biredin nan ta zaro kudinta ta cura a rigar mamanta tanabin kowa da kallo, katin da lambar wayar Bilal yake aciki ma sanda ta d'auka ta adana ajikinta se zare ido take, batasan me za'a mata ba amma tabbas tasan akwai alamun zata dauki yar mitsitsiyar akwatinta ta kwasa aguje inhar ya kasance azabace! Lokacin da k'arfen yayi azabar zafi se wasu maza tagani datakeda yak'inin yan uwanta ne sukazo suka daddafeta tun a nan ta soma ihu mik'ar da k'afarta akayi aka dafe Jere ya daddage ya manna mata k'arfen a tsakiyar tafin k'afarta!!! Wata uwar k'ara data k'walla tsabar azaba seda ta saki fitsari a wando ba shiri, haka ya mata tambari biyu a kowace k'afa zuwa wannan lokacin ta suma batasan inda kanta yake ba, k'ara dafa k'arafan yake yana ik'irarin manna mata a hannu Inna suwai ta rungumeshi tana kuka akan yabar ta a haka, kallon ta yayi yana yamutsa fuska
"kona manna mata kokuma akaita kan hanya ta kama gabanta" Dama bata saka ran ze barta ta zauna ba dan haka da sauri ta amince akan a koretan tasan koba jima koba dad'e zata nemi gida, koda babu ransu kuwa. Kallon masu dafeta yayi yace
"Ko inuwar wannan karku barmun agidana, ku fita da ita daga garin nan kuje cen bakin titi ku ajiyeta itada kayan ta da komanta" Haka suka amsa masa suka kwasheta a some ita da kayan ta, akan hanyar su aka soma ruwan sama ga duhu ya soma sauka wannan ya sanya babu wata tazara da garin suka ajiyeta suka ajiye mata akwatinta suka juya inda anan dukan ruwan sama ya dawo da ita cikin hayyacin amma seme ta farka cikin tsananin azaba da radad'i sannan babu akwatin kayanta a ranta ta ayyana acen aka kwace mata, ta godewa Allah daya sanya bata saka kud'inta a jakar ba, amma me tana lalubar rigar mamanta seta ji wayam! bata sani wad'an nan yan uwan nata sunga sanda ta saka kud'i a wurin, sune suka zace wayarta da kud'in suka barta da akwati wanda kafin ta farfad'o wani mara imani ya kwace. Babu takalmi a k'afarta batasan ammata lahani ba seda ta mik'e nan take ta zube awurin sabida wata sabuwar azabar data ziyarce ta ga ruwa ana tsulawa ga dare yayi, kukan ma a wannan lokacin gagararta yayi, jefi jefi motoci suke wucewa gata a gurfane bazata iya taka k'afarta ba bare ta saka musu hannu su taimaketa!
**************
*Washe gari*
Anan ta kwana cikin tsananin radad'i da fargaba me tsanani, ilahirin ruwan akanta ya kare a gindin wata bishiya, da asuba ma se taimama tayi tayi salla a zaune, har azahar ba yalwar mutane akan titin, tunanin abinyi takeyi ga azabar k'unar dake tafin k'afarta, haka ta mik'e tanaji tana gani ta soma tafiya akan duga duganta inda wutar bata kaiba, haka tayita tafiya se la'asar ta samu wata motar yaji ta d'auketa asama nanma da k'yar ta samu hawa sabida wuyar datake ciki,tare da alk'awarin zata bashi Naira hamsin idan sun isa gari.