← Book details Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 71

Sashe 12

Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Good, zan yadda cewan kai friend d'inane sabida ka fad'a wannan code, badan hakaba ni bazan iya tuna inda naga face d'in kaba" Shiru yayi yaba zuba yak'e ita kuwa ta zauna tas ta cinye abinta sannan ta mik'e da zummar barin wurin yace da sauri yana kallonta

"Your highness ke nake jira fa" Sauke wata nannuyar ajiyan zuciya tayi sannan cikin kosawa tace

"Immaka me? Dukda yaji zafin kalamanta amma seyace

"Dama so nake ince dake wayanki koyaya nayi trying bayya tafiya" Yamutsa fuska ta kumayi kafin tace

"Did u try sending the code" shi ta soma k'ular dashi komai turanci ubanwaye be iya turancin ba, shegiya da iya kirsa kamar uwarta ya fad'a a zuci, a sarari kuma seyace

"Pardon i dont grab" "Idan harni na baka number na then try sending the code via sms to me, i will save ur number then zaka iya samuna,if not har abada bazaka sameni ba" Mik'ewa shima yayi

"But ur highness kene da kanki kika bani number ai" Ya k'arashe maganar abun tausayi, tab'e baki tayi

"Thats the main reason why i need to confirm, see i dont normally give my number to stranger's, and when ever i do i need to confirm first, so if kanaso ka kirani ka samu send the code for confirmation" Tana kaiwa nan ta soma tafiya bin bayanta yayi

"Your Highness the code is 3753"

"Via sms" Ta furta dad'an k'arfi sannan ta k'arawa tafiyarta sauri zuwa barin inda yake........Tsayawa yayi yana kallonta harta b'acewa ganinsa, gaba d'aya ta rikirkitasa @ first ya zata ya gama kamata a hannu, se yanzu ya gano cewar da sauran rina akaba, seyabi da lallab'awa kenan, amma ba komai kowane irin wulak'anci ze jure harseya cimma burinsa akanta kamar yanda uwarta tayi masa,tun yana d'an shekaru 17 yanzu gashi yana 25 amma bata bar tsuliyar sa ta hutaba kullum yana kanta yana sukuwa!

******************

Lokacin da Bahar ta fito daga fadar Sarauni kai tsaye fada ta wuce jikinta har rawa yake, hannunta rik'e da hannu Barra, se zare ido barra keyi alamun rashin gaskiya ita sam ba haka tasoba, so kawai tayi Bahar Sarauni ta nemi Me martaba daban bawai fad'a a fada ba! Seda suka shiga har cikin fada sannan ta saki hannun Barra ta daidaita nutsuwarta, gabaki d'aya mutanen fadar dake zazzaune sunyi zaman tamutela suna fuskantar juna ana tattauna maganganu masu muhimmanci ganin Bahar Sarauni mik'ewa sukayi suka sunkiya suka gayar da ita ta kwashesu kawai ta zubar bata amsaba, Barra kuwa jikinta se rawa yake dan kuwa ganin yanayi irinna sarki ya tabbatar mata ya gane me tayi, bayan sarki ya mim'e ya gayarda mahaifiyar sa dama tsarin fadar akwai wurin zaman manyan iyaye irinsu wanda yake agefen sarki idan maganar dole ta kama sesunzo to anan suke zama, Bahar sarauni bata zauna ba dukda tayin zaman da akayi mata ta kalli d'aukacin 'yan fadar tace

"Waye yazo da maganar yarinyar da ake cewa Hammude kurma yayiwa fyad'e?" Tsit fada ta d'auki shiru tamkar ba kowa agun" Gyaran tsayuwarta tayi

"Bazan k'ara maimaita tambaya naba, amsa nake jira" Me martaba ne yace

"Ammu Bahar, D'annGaladima ne da idan fada suka ganshi suka tabbatar da hakan" cikin takaici tace

"Suka ganshi k'irik'iri akan 'yar mutane yana mata fyad'e? Da sauri kowa ya kalleta

"Ba haka bane Ran Bahar ya dad'e" Sarki ya fad'a yana k'ara k'ask'antar da kansa cikeda ladabi

"Inajinka gayamun da bakinka yanda komai ya faru" Seda sarki ya kalli mutanen wurin sannan yace yana gyaran zaman rawanin sa

"Ku bamu wuri" D'aga murya tayi

"Zan La'anci duk la'anannen daya fita daga fadar nan, tare daku aka k'ulla agabanku za'a warware komai, Kai Tahir maza ka aika kiran Hammude da gaggawa" Cikin girmamawa ta bada umarnin kiram kurma, sannan ya fuskance ta sosai ya kwashe komai ya sanar da ita, seda yakai aya sannan tace

"Su waye shaidun kace"

"D'an galadima ne da kuma idan fada"

"Su waye idan fada, munafukan fada zakace, kai Tahir ashe bakada hankali? me irin tunaninka samshi ba sarki bane, ban tab'a ganin sarki mara adalci irinkaba, katab'a gani ko a hikayar marasa hankali mutum yayiwa yarinya fyad'e daga waje ya kawota gidansu to tamasa me? tukunna ma ka saurari nashi b'angarin dalilin kawota gidan? Cikin sanyin Jiki yace

"A'a Ammu, naga zahiri shisa ban nemi jin mezaice" Dage gira d'aya tayi ta k'ank'ance ido

"Zahiri kake k'ara gayamun ka gani, Tahir anya sanda malamin islamiyyar ku ke zuwa kana saurarar sa kuwa? bakasan musulunci baya karb'ar shaidun zinaba harse mutane hud'u sun shaida sunga mazinatan turmi da tab'arya, kai jini kawai shine shaidarka, tukunna ma wai ka shirya gayawa Allah ka sauya nashi shaidun zuwa naka dankai sarkine? cikin rawar murya yace

"Subhanallahi, Ammu ba haka nake nufi ha wlh" Suna haka segashinan ya shigo yauma kamar kullum da gudun sa, a gabanta ya tsaya ko haki gudun be cika sakashiba sabida ya zame masa d'abi'a, dafa kafad'arsa Bahar tayi tace

"Harse yaushe zaka dena wannan guje gujen Hammude? Murmushi ya sakar mata abinda yake fin wata beyiba sannan ya mata alama da hannu akan ze dena" Tana murmishi tace

"Nasanka da saurin rubutu, maza mazq rubutamun duk abinda ka sani akan yarinyar da ake zargin ka mata fyad'e" Jinjina kansa yayi lokaci d'aya annurin fuskarsa ya kau, ya zaro jotter da pen a aljihunsa, cikin lokacin dabe gaza 10mns ba ya fayyace labarin iyakar abinda ya sani!!!!!

Barra ce ta karance tsaf a tsanake kowa yayi tsit yana sauraren ta harseda ta kammala.Nisawa Bahar Sarauni tayi yanxu kam ta fahimci duk abinda ya faru, tana jinjina kanta tace

"A matsayinmu na masu hankali be dace sabida munga jini acikin yarinya muce fyad'e aka mata ba, musamman shi jinin kawar da budurci baya zuba bare harya d'iga, kai Galadima baka tab'a kawar da budurci bane, kainkuma D'an galadima kaima matanka biyu ko dukkansu ba sabon takinka bane ba, Sarkin yak'i kana me akayi wannan shirmen ina matanka hud'u harda k'wark'wara? so kake kacemun bakasan jinin kawar da budurci ba, kaikuma sarkin baka, inace matanka uku, dukkanin ku anan kunada mace sama da d'aya cikin hadda sarkin ku? idan har kun d'auka yawan jikin daya zuba haryana d'iga ajikin yarinyar jinin kawar da budurci ne to kuwa dukkanin ku anan an rigaku takin takalminku, in hakane har sarki sena saukeshi a kujerar mulkin sa? kokunsan a k'a'idar mulkin k'asarnan idan ka taki takalmin sauri a matsayin auren fari baka mulki? Kame kame kowa ya hauyi, atake ta tsawatar akayi tsit ta waigo ta kalli D'an galadima ido cikin ido tace

"La'anannen nan dukshi ya shirya komai, soyakeyi tarihi ya maimaita kansa, ba'a rufin asiri nina rufa maka, idan tunanin ka zanje kabari da sirrin ka tokama janye, d'anka yana naj ajiye, kuma kafin aurenka kayiwa baiwar ciki niwa na gayawa? na tilastaka aurenka ne ? abinda kake gudu nan gaba kad'an asirinka ya tonu mulki ya tashi a hannunka, hak'uri zakayi rashin kamun kanka ya b'ata komai, magaji kuma kurma ne, koda kuke cewa kurma ne kunyi kuskure, kurma shine wanda bayaji, Amma Hammude yanajin magana tsaf, lalurarsa a harshensa take bawai a kunnen saba, kuma inshaa Allahu ze mulkeku koda bakwa so, ina abun yin Allah ne bana la'anannun Allah bane irin ku" Kowa yayi tsit taci gaba

"Da D'an galadima da idan fada, suje su yad'a cewar Bahar tayi bincike ta gano cewar yarinya jinin hailarta ne ya zuba a k'asa bana kawar da budurciba, Kurma taimakonta yayi kamar yanda kukaji bayani yanzu a kuma tabbatar cewar lallai munafukai sunyi nasarar da kowa ze wanke kurma daga zargi" Amsa mata akayi cikeda ladabi ta waiga suka fuskanci juna da kurma tace cikin nutsuwa

"Acikin yaran guda biyu da akeso a aura maka waccece kake so,waye kuma bakaso, idan duka kana sonsu zansa a aura maka dukkansu, idan kuma duka baka sonsu zan tsinewa wanda yayi gigin koda tashin maganar ne in la'ancesa har k'arshen rayuwarsa" A hankali Kurma yake kallon ta ya gama karantar iyakar gaskiyarta kenan, sauke idansa yayi zuwaga mahaifin sa cikeda kulawa danyasan akan sa aka tozartar da mahaifin nasa agaban bayinsa da mukaraban sa, bashida zab'in daya wuce zube idanshi a wurin da ake kallon sa, gaba d'aya jikinsa yana bashi Uncle Jay yana kallonsa, jira yake yaji mexaice, kallon juna suka tsayayi na wuccin gadi, ga Uncle Jay acikin manyan fada a jere dan kuwa shine wakili a wannan masarautar amma ba bakin magana, seda ya gama karantar zuciyar uncle Jay sannan ya mayarda dubanshi zuwaga Bahar Sarauni......

******************

*To nima dai gani na kasa kunnen sauraren wacce kurma xe zab'a, shin anya ze zab'a kuwa, befasan koda fuskar khairiyta ba, gashi ya tsani Yar shara.....*

*Mom Nu'aiym.*

*TSINTAR AYA*   FREE BOOK

*BILLY GALADANCHI*

*JOIN OUR TELEGRAM PAGE THROU THE LINK BELOW*
https://t.me/joinchat/FgfKMiS_mYc-DIjC.

*Assalamu Alaikum, Readers hak'uri zamuyi da juna, kui hak'uri zakuyi inkeyin post yau gobe bazan yiba, kunga ina sab'a alk'awari gwanda na daina, dan Allah kumun wannan alfarmar, Nagode.*

   *SHAFI NA BAKWAI*

Jotter sa ya mik'a hannu ya karb'a a hannun Barra sannan ya rubuta

"Bahar i will marry them both, but please not now, se bayan shekara d'aya, and lastly i want to leave the country kafin lokacin auren, i really need some fresh air, this place is like a hell, bazasu tab'a bari in samu nutsuwaba" Barra ya mik'awa seda ta karance sannan seta sauya maganganun daga yanda yayisu, tace tana kallon Bahar

"Ammu Bahar, yace ze auri yaran duka amma yana neman alfarmar abari senan da shekara d'aya, kuma dan Allah a rok'a masa izinin sarki yanaso yabar k'asar kafin zuwan lokacin sabida akwai wasu ayyuka dazeyi k'asar dazeje" Nisawa Bahar tayi dajin hukuncin daya yanke tace a nuste tana kallon sa

"Kada tsoron wasu la'anannu ya sanya ka amsa abinda bashine bane aranka, ka tabbatar haka kakeso? A hankali ya gyad'a mata kai, yayinda me martaba ya sauke wata nannauyan ajiyan zuciya, ta waiga ta kalli Me martaba tace
Chapter 12 · 0% Book details