← Book details Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 71

Sashe 20

Tsintar Aya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

****************
A lokacin da akaje bikin k'addamar da Hafsat matsayin adopted child agidan, se kawai waziri ya zuga sarki akan shiya d'auki yarinyar mana matsayin 'yarda ya haifa kadafa ya manta banda Hammood bashida d'a bashida jika, bayaga haka 'ya mace ma rahama ce, yace daga baya seya nunawa bahar hikimar yin hakan gwanda ta zama kaka tunda koba komai aita tsufa..... Dukda Bahar tayi mamakin jin sauyawar maganar amma se hakan yayi mata dad'i koba komai ya nuna mata yafita son abinda take so, kowa se gulma yake tun a wurin, yarinyar da Mood yayiwa fyad'e tazama 'yar sarki, wasu suce ai ciki ne ya bayyana ajikinta ake b'oyewa, wasu suce ai an zubar da cikin kowa dai da abinda yake fad'a.... Mood sanda me martaba ya had'asu yana zancen sun zama d'aya banda gajerun tsaki mara sauti ba abinda yake zubawa, samun wuri da rainin hankali, wannan yarinyar tabbas yanzu ya k'ara yadda turota akayi, kuma dasanya hannun su galadima a faruwar komai, baya rab'a d'ayan biyu tabbas da sihiri suke aiki sun sihirce kakarsa da Mahaifinsa harma da mahaifiyarsa, kai kafatanin mutanen masarautar ma, banda haka bakusan asalin yarinyar ba sekuce kun mayar da ita 'ya 'yarma ta sarki wai taku, haba haba wannan maganar wlh da sake wai an baiwa me kaza k'afa.

Lokacin da Khairiyya tabar gidan su zuwa school tare da fadawa da direbobin motoci har hud'u dake rakata makaranta, ciki hadda bayinta mata guda biyu setayi umarni akan su jirata a waje idan ta kammala lecture d'inta zata fito su tafi, amma data shiga lecture hall d'in ta k'ofar k'asa, seta tattaka matattakalar dake kaika saman kujerun k'arshe tayi hanyar waje gaba d'aya tabar cikin hall ta sama, daga cen ta b'ulla bayan faculty nasu ta nufi daidai inda suka shirya itada Bilal, dama ba abinda ta d'auka se jakarta data k'arawa girma daga k'arama zuwa me size d'in small kit wanda card's d'inta kawai ne se wasu abubuwan mata irin su turaruka,powder da lipstic, tayi niyyan idan sunje garin dazasuje zata siya abayu haka take sakawa kafin sati ta cika.Tana zama a motar ta kallesa shi d'inma ita yake kallo

"Yaa Bilal" Ta furta tana kwantar da bayanta ajikin sit din motar tare da d'aura kanta saman head rest ba saman kan kujerar, lumshe idanta tayi ta zube masa su kafin tace

"Naga kurman nan yaa Bilal amma yanada kyau fa, dabadan kurman gaske bane ba Allah da manage zanyi dashi, kad'an kafishi kyau fa" Dariya siririya yayi

"Lallai bakida kunya Riyya, ni kike gayawa kamannin saurayin ki" Tab'e baki tayi a daidai lokacin da yake riverse yana shirin harbawa kan hanya da kyau

"Wai saurayina, Allah ya tsari gatari da saran shuka, kurma fa" Yanzu kam darawa yayi sosai

"Allah Riyya kin gama raina gayen nan, amma dai kinsan kyakyawa ba abun rainawa bane ko? Tana dariya tace

"Wani kyakyawan zezo amma dai ba kurma ba" Hannunsa ya d'aura akan nata suka kalli juna yace

"Inama Yaa Bilal ze aurawa talaka k'anwar sa, inama sarki ze yarda ya bada auren her royal highness wurin d'an me gadi, ina ma Her Royal highness zata yarda ta auri d'an megadi da yau nashiga yak'i tsakanina da kurma harsena tabbatar na rabata da auren kurma nina aureta" K'ura masa idanunta tayi wani abu na fizgar ta, zuciyar ta yana mata yawo akan abubuwan dataketa ji bata gano menene ba se yanzu akan Bilal, tunani ya mata kamun bazata seda ta tsinkayi muryarsa yana cewa

"Kiyi hak'uri Khairiyya, nasan wannan maganar danayi nayi ganganci, na tabbatar cewar na cancanci hukuncin kisa ma, ammun dukkanin abinda ya dace ambani matsayin aboki bayan ban cancantaba, aka kuma bani matsayin Yaya dukbe isheni ba seda nayi katsalandan akan harkar aurenki, tuba nake Princess Riyya nayi azarb'ab'i, ba laifina bane laifin zuciya tane dataketa gayamun in furta abinda yake cikinta" Murmushi ta sakar masa kafin tace

"Bilal kai jaruminane, komai naka yana burgeni,.kaina namiji na farko arayuwata dana tab'a magana dashi me tsayi bayan Yaa Bilal, ko me martaba Daddyna bana magana me tsayi sosai dashi, kowa yana yawan fad'ar ina masa k'warjini, a yanda nakeji akanka koda kaine kake gadin zan maka runfa" Da sauri ya kalleta

"Ban fahimci hausar ba Ur highness" Kawar da kanta tayi

"Nafiso kake kirana da suna Lil sis kawai, kabarwa wad'ancen suyita highness d'in" Murmushi yayi ya sake hannunts dahar ya soma sabawa da nasa sannan yace

"Mahaifina gadi yake a gidan wata ma'aikaciyar banki shekara da shekaru, ita tamin gata ta sanyani a makaranta taketa bani kud'i har kyauta gida katafare ta bani" Kallon sa tayi tace

"To a school kowa yasan ka ai, kaine kake kyautar kud'i a duk cikin d'aliban dasuke makarantar da abinci da suturu, kana d'anme gadi yaya akayi kakeda wannan kud'in" Murmushi yayi kafi yace yana kallonta ido cikin ido

"Har kyautar miliyan biyar take bani, kuma bayan wani lokaci seta kuma bani amma har yanzu albashin mahaifina na kowane wata dubu sha biyar ce bata k'ara masa ba, koda yake shekarun baya dubu uku ce maz zuwa zuwa yaketa samun karin albashi yana sana'arsa ta trader a k'ofar gidan" K'irjintane yayi mugun dokawa tace muryanta yana rawa

"Tambayoyi da yawa akaina sedai dan Allah wace unguwa kuke agarin? seda ya fahimci yanayinta sannan yace

"Shiyar Fada" Nannauyan ajiyan zuciya ta sauke kafin tace

"Amma mesa zatake baka wad'an nan kud'in, idan taimakon ku takeso tayi mesa bazata taimaki babanka ba sekai" Kafin ya bata amsa wayarsa yayi k'ara dama akwai bluethood a kunnensa d'aukan kiran kawai yayi yafi 40mns yana magana dame kiran nasa yana sharara gudu a k'walta, magana ce data shafi ginin daze fara wanda yake d'auke sa sunan sa, seda ya kammala sannn yace

"Zamu tsaya muci abinci anan ko" Batace masa komai ba, ita gaba d'aya Riyya abu biyu ta iya, daga cin abinci se karatu kamar alhuda huda.... Har suka isa garin da zasu basu sake maganar ba, bayan sun isa suka doshi wani matsaksicin gida me kyau 2bed room acikin sa se wani k'aramin parlor me dauke da set na kujeru ba masu tsada ba sosai amma very cute masu kyau na asali, akwai dining tables bugun sampurin nigeria coffee brown me kyau, labulaye karamar carpet da kayan kallo,akwai dining shelf shima zube da plate mugs nashan tea da sauran tarkacen abin dukda zaka buk'ata nadai cin abinci ko debarsa, gefen saman dining din kitchen me asalin kyau d'an matsakaici akwai Table gas ajiye asaman worktop d'in da tsirarun kayan kitchen dazaka iya amfani dasu a cikin drowers, kuloli kala ukune kawai, se k'ofar baya ajikin kitchen d'in, d'akunan kuwa sekad'anbi wani walkway tukunna zaka isa inda zaka shiga d'akunan da ko wanne ke kallon d'an uwan sa kuma kowanne gadone aciki k'irar Nigeria matsakaici da wardrop me kofa biyu se toilet dashima komai akwai aciki.na gayu, bayan ua gama nuna mata suka dawo d'akin dazata zauna seda sumaci abincin dasumazo dashi da ka shi ya wanke kwanukan sannan ya dawo ya zauna d'an nesa da ita yace

"Toh ban saniba ko akwai abinda zaki buk'ata ur highness amma daidai gwargwado komai akwai agidan nan, acikin shelf d'incen na dining akwai, goldenmn,cornflakes,rice crispies,coconot flakes, akwai kayan tea, na kawo loap of breads danasan yana kwana biyu beyi tauriba koya lalace, a fridge akwai lemuka iri iri akuma kwai fresh milk da youghurt" Kallon sa take harya kai aya sannan tace

"D'azu na tambayeka baka bani amsaba" Yasan me take nufi dan haka mayarda kallonsa yayi zuwaga TVn dake parlor d'in ya k'urawa TVn ido kafin yace

"She made me became her sex slave since i was 17, and now she want to marry me" Da sauri ta kallesa kafin tace

"Yaa Bilal, kace me? kallonta yanzu kam yayi sosai yace

"Yea abinda kikaji na fad'a haka nace, tunkafin insan ciwon kaina tun kafin insam meye sex, tun kafin insan na balaga kafin mafarki ya balagar dani itace ta tatseni ta fitar mun da ruwan maniyyin farko daseda na tambayeta meyeshi take cemun Bilal ai kawowa kayi maniyyi ne!! Da sauri ta toshe kunnenta seda yayi shiru sannan lokaci d'aya hankalinta ya tashi jikinta ya soma rawa ta mik'e tsaye

"Ni bance ka sanar dani wannan maganganun ba, Allah ya kyauta ya shiryar daku, mu kuma ya karemu da fad'awa halaka da aikata aikin dana sani" Murmushi yayi kafin yace

"Yanaga kin razana? kinsan zama da manyan mata, shisa bana shayin fad'ar magana ko kad'an"

"Yaushe zakazo ka tafi ne? nifa na saba kwana ni kad'ai" Murmushi yayi sannan yace ki zauna akwai abinda nakeso mu kalla a tare dake" Yamutsa fuska tayi

"Yaa Bilal banida nutsuwa wlh, da safe inka dawo zamu kallo" Mik'ewa yayi yazo daf da ita har suna jiyo bugun zuciyar juna sannan yace

"Acikin babban abinda nafi tsana arayuwa musu ne babba, dare yayi ne aise dare zan tafi, tayaya zan d'akko 'yar sarki inzo da ita nan inbarta ita kad'ai, d'aki biyu ne zan kawo me tayaki kwana, amma for now zama zakiyi zan miki wani bayani daga bisani semuyi kallo sannan seki yankewa kanki hukunci" Tsatsareshi tayi da idanu jikinta ya soma yin sanyi, wannan shine babban dalilin dayasa taso ta sanar da Yaa Bilal shirin ta amma wayarsa baya tafiya, dukda yake ta dire masa sak'on waya. Komawa tayi ta zauna tana sauke ajiyan zuciya masu nauyi a jere jere, idanuwan Bilal suna nuna mata cewar tabbas akwai cutarwa a d'akkotan da yayi ya kawota nan. shid'inma zama yayi yace

"Kamar yanda na sanar dake mahaifi na kutumin Niger republic ne, aikin ga ruwa yafara kawoshi Nigeria daganan ya fad'a harkar shoe shiner, bayan nan kuma se yasoma tunanin yin gadi a lokaci d'aya yana sayar da ruwan sa, Anace da mahaifina Baba tun zamanin k'uruciya mahaifiyata kuma sunanta Bilkisu amma Lami ake kiranta wannan ya sanya muke kiranta dasuna Baba Lami, munyi gadi a wurin mutane da yawa sedai kuma d'aya kawaice me kirki aciki wato Hajiya Binta wacce muke kira da momy" Da sauri ta kallesa, k'irjinta banda bugawa ba abinda yake
Chapter 20 · 0% Book details