Sashe 44
Komai Nisan Dare Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Duk yadda ta so ta ɓoye razanin da zuciyarta ta shiga hakan bai yiyu ba, sai da asirin hakan ya fallasu a kan fuskarta. Gwaggo dake amsa gaisuwarta ganin yanayinta ta ce. "Saratu!" Ɗan zabura Mommy ta yi tare da sauke numfashi, cikin ƙoƙarin ɓoye halin da take ciki ta ce. "Na'am Gwaggo."
"Ina hankalinki ya tafi Ina miki magana kin yi shiru?"
Yatsina fuska ta yi ta ce. "Na tafi wani ɗan tunani ne, zan yi abu yanzu na manta ban yi ba, bari na je na dawo." Taɓe baki Gwaggo ta yi ta ce. "Ai ke ba kya rabo da uzuri kodayaushe, sai ka ce mara gaskiya daga kin zauna burum kin tashi kamar wadda aka tsikara." Kicin-kicin Mommy ta yi da fuska ba ta ce komai ba ta tashi ta fita. Girgiza kai Abba ya yi ya miƙe ya nufi dinning area don cin abinci. Gwaggo na duban A'isha ta ce. "Wannan ce yarinyar? Allah Sarki, Allah ya ji ƙan mahaifiyarki ya ba ki haƙurin rashi, taso ki zauna nan kusa da ni kin ji." Ya Maamah ce ta kama hannunta ta zaunar da ita a kusa da Gwaggo, kanta a ƙasa ta ce. "Ina yini?" Gwaggo ta amsa cikin kulawa tana ƙare mata kallo.
"Tubarakallah ga ta kyakkyawa Masha Allah, Allah albarkaci rayuwarki Æ´ar nan, Addata mai sunan Yayata."
Ummi tana murmushi ta ce. "Mai sunanta ce kam, ga shi da alamu za ta yi haƙurin masu sunan." Ya Maamah ta ce. "Taɓ, ba su da wani haƙuri sunan tsofaffin, A'isha ta mana yawa gaskiya, duk an baibaye mu da su, kowa A'isha A'isha." Gwaggo ta ce. "Ja'ira sunanki ne dai."
Sun daÉ—e suna hira cikin raha da barkwanci, sai da A'isha ta fara gyangyaÉ—i sannan Gwaggo ta ce akai ta, ta kwanta.
Yadda Mommy ta ga rana haka ta ga dare, ta rasa me ya sa ganin A'isha ya firgita ta, ta ji wata muguwar tsanar ta lokaci ɗaya ta cika mata zuciya. Hakan ya sa ta ƙara ƙaimi akan ƙudirinta na korar A'isha daga gidan.
Washegari da safe bayan Gwaggo ta gama karyawa ta ce tafiya za ta yi. Abba ya ce. "Haba Gwaggo daga zuwa kamar wadda ake kora? Kin zo da daddare kuma yau da safe ki ce za ki koma?" Gwaggo ta ce. "Ƙyale ni na tafi, dama ba zama na zo yi ba, jaje na zo maka, Allah ya kiyaye ya tsare gaba, ya raba mu da sharrin ƙarfe. Ina ni ina zama cikin surukai, gara na yi tafiyata." Ummi ta ce. "Ki bari ko kwana ɗaya ki ƙara mana don Allah." Gwaggo ta ce, "Toh shikenan tunda kun matsa, kira mini mai sunan Adda mu yi hira, ta yi ta zama a ɗaki tana tunani ita kaɗai babu daɗi, goben idan Allah ya kai mu sai na tafi." Abba ya ce. "Allah ya kai mu, Dr mu je na sauke ki a school ɗin ko?" Ummi ta miƙe tare da faɗin. "Toh, Gwaggo bari mu je, sai na dawo, zan saka Maamah ta kawo miki Nanan."
"To shikenan, sai kun dawo, Allah ya kiyaye ya tsare."
Suka amsa da Amin tare da ficewa.
Har Rana A'isha suna tare da Gwaggo tana yi mata nasiha, ta ji daɗin kasancewa da Gwaggo sosai, don tamkar wadda ta daɗe da sanin ta haka ta nuna mata, babu ƙyara ko tsangwama sai zallar ƙauna. A'isha tana kan dardumar da ta yi Sallar Azhar bayan ta idar, Gwaggo ta tura mata abinci gabanta tana faɗin. "Ƙara ci sai ki sha magani ki kwanta." A hankali ta ce. "Na ƙoshi fa." Haɓa Gwaggo ta riƙe ta ce. "Abincin da kika ci nawa yake ƴar nan? Ki ƙara." Ba ta kuma magana ta lalubi plate ɗin ta fara cin abincin kamar ba ta so. Gwaggo ta ce. "Ko ke fa, abinci ai shi ne mutum, ke kuma daga gani za ki gaddamar cin shi, sai an dinga tsayawa a kanki, zan sanar da Zaran ta dinga tsaye a kanki idan za ki abinci." Ita dai A'isha ba ta ce komai ba ta cigaba da cin abincinta, tunda ta zo Gwaggo take ba ta abubuwan ciye-ciye, da ya Maamah ta kawo musu abinci ta zuba mata ta ci, yanzu ma ta ƙara mata. Kaɗan ta ci ta ture ta ce ta ƙoshi. Gwaggo ta ɓallo magungunanta ta ba ta. Tana gama sha ta kwanta bacci ya ɗauke ta.
"Ina hankalinki ya tafi Ina miki magana kin yi shiru?"
Yatsina fuska ta yi ta ce. "Na tafi wani ɗan tunani ne, zan yi abu yanzu na manta ban yi ba, bari na je na dawo." Taɓe baki Gwaggo ta yi ta ce. "Ai ke ba kya rabo da uzuri kodayaushe, sai ka ce mara gaskiya daga kin zauna burum kin tashi kamar wadda aka tsikara." Kicin-kicin Mommy ta yi da fuska ba ta ce komai ba ta tashi ta fita. Girgiza kai Abba ya yi ya miƙe ya nufi dinning area don cin abinci. Gwaggo na duban A'isha ta ce. "Wannan ce yarinyar? Allah Sarki, Allah ya ji ƙan mahaifiyarki ya ba ki haƙurin rashi, taso ki zauna nan kusa da ni kin ji." Ya Maamah ce ta kama hannunta ta zaunar da ita a kusa da Gwaggo, kanta a ƙasa ta ce. "Ina yini?" Gwaggo ta amsa cikin kulawa tana ƙare mata kallo.
"Tubarakallah ga ta kyakkyawa Masha Allah, Allah albarkaci rayuwarki Æ´ar nan, Addata mai sunan Yayata."
Ummi tana murmushi ta ce. "Mai sunanta ce kam, ga shi da alamu za ta yi haƙurin masu sunan." Ya Maamah ta ce. "Taɓ, ba su da wani haƙuri sunan tsofaffin, A'isha ta mana yawa gaskiya, duk an baibaye mu da su, kowa A'isha A'isha." Gwaggo ta ce. "Ja'ira sunanki ne dai."
Sun daÉ—e suna hira cikin raha da barkwanci, sai da A'isha ta fara gyangyaÉ—i sannan Gwaggo ta ce akai ta, ta kwanta.
Yadda Mommy ta ga rana haka ta ga dare, ta rasa me ya sa ganin A'isha ya firgita ta, ta ji wata muguwar tsanar ta lokaci ɗaya ta cika mata zuciya. Hakan ya sa ta ƙara ƙaimi akan ƙudirinta na korar A'isha daga gidan.
Washegari da safe bayan Gwaggo ta gama karyawa ta ce tafiya za ta yi. Abba ya ce. "Haba Gwaggo daga zuwa kamar wadda ake kora? Kin zo da daddare kuma yau da safe ki ce za ki koma?" Gwaggo ta ce. "Ƙyale ni na tafi, dama ba zama na zo yi ba, jaje na zo maka, Allah ya kiyaye ya tsare gaba, ya raba mu da sharrin ƙarfe. Ina ni ina zama cikin surukai, gara na yi tafiyata." Ummi ta ce. "Ki bari ko kwana ɗaya ki ƙara mana don Allah." Gwaggo ta ce, "Toh shikenan tunda kun matsa, kira mini mai sunan Adda mu yi hira, ta yi ta zama a ɗaki tana tunani ita kaɗai babu daɗi, goben idan Allah ya kai mu sai na tafi." Abba ya ce. "Allah ya kai mu, Dr mu je na sauke ki a school ɗin ko?" Ummi ta miƙe tare da faɗin. "Toh, Gwaggo bari mu je, sai na dawo, zan saka Maamah ta kawo miki Nanan."
"To shikenan, sai kun dawo, Allah ya kiyaye ya tsare."
Suka amsa da Amin tare da ficewa.
Har Rana A'isha suna tare da Gwaggo tana yi mata nasiha, ta ji daɗin kasancewa da Gwaggo sosai, don tamkar wadda ta daɗe da sanin ta haka ta nuna mata, babu ƙyara ko tsangwama sai zallar ƙauna. A'isha tana kan dardumar da ta yi Sallar Azhar bayan ta idar, Gwaggo ta tura mata abinci gabanta tana faɗin. "Ƙara ci sai ki sha magani ki kwanta." A hankali ta ce. "Na ƙoshi fa." Haɓa Gwaggo ta riƙe ta ce. "Abincin da kika ci nawa yake ƴar nan? Ki ƙara." Ba ta kuma magana ta lalubi plate ɗin ta fara cin abincin kamar ba ta so. Gwaggo ta ce. "Ko ke fa, abinci ai shi ne mutum, ke kuma daga gani za ki gaddamar cin shi, sai an dinga tsayawa a kanki, zan sanar da Zaran ta dinga tsaye a kanki idan za ki abinci." Ita dai A'isha ba ta ce komai ba ta cigaba da cin abincinta, tunda ta zo Gwaggo take ba ta abubuwan ciye-ciye, da ya Maamah ta kawo musu abinci ta zuba mata ta ci, yanzu ma ta ƙara mata. Kaɗan ta ci ta ture ta ce ta ƙoshi. Gwaggo ta ɓallo magungunanta ta ba ta. Tana gama sha ta kwanta bacci ya ɗauke ta.