← Book details Komai Nisan Dare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 55

Sashe 16

Komai Nisan Dare Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Cikin satin nan rayuwa ta fara yiwa su Inna tsanani, saboda yanzu ba ta sana'ar komai, sai aikin abincin sadakar nan, 500 kuwa a sati mai zata yiwa rai biyu, ga abubuwan da yawa, bayan abinci ga sabulun wanka da na wanki, ga man shafawa, ga omon wanke_wanke, ga siyan ruwan amfanin gida, ban da sauran abubuwan buƙata na yau da kullum. Jarin ayar da ɗan guntun kuɗin dake hannunta duk sun ƙare. Sai suka koma irin rayuwar daa, sai su farka ba su da ko ƙwayar hatsin da za su ci a cikinsu. Yau Alhamis, wanda ya kama sati biyu cif da tafiyar su Ma'u. Da rana A'isha ta gama shirin tafiya makaranta kasancewar ta yamma suke yi tunda su ƴan junior section ne. Jakar makarantarta ta laluba ta ɗauka, cikin sanyin murya ta ce. "Inna na gama mu tafi." Inna ta sauke tagumin da ta rafka ta ce. "Haka zaki je makarantar ba ki ci komai ba A'isha, da hak'ura kika yi na fita na dawo ko Allah zai sa in dace in samo miki wani abun ki ci, sai ki tafin." A'isha ta ce. "Toh Inna a ina zaki samu?" Inna ta ce. "Sabon Gari zan je gurin Hajiya mai k'uli_k'uli, idan da aiki in yi mata ta biya Ni, na san ma ba'a rasa aikin ba tunda gobe ne cin kasuwa za'a zo a sissiya." A'isha ta ce. "To mu je makarantar, idan kin samu sai ki kai mun can ɗin." Inna ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "Kin kawo shawara kuma, tashi mu je kar ki makara, daga can sai na wuce." Miƙewa A'isha ta yi, Inna ta kama hannunta suka fice.

Tun bayan da Inna ta tafi ba jimawa A'isha take saka ran dawowarta, domin wata irin yunwa take ji ba kaɗan ba, ɗan kokon Naira goman da ta sha da safe shi kaɗai ne a cikinta. Har aka fita Sallar la'asar Inna ba ta zo ba, gashi yau Malama Hajara ba ta zo ba, sai wata yarinya ta roƙa ta fitar da ita waje ta yi ta Sallah ta dawo da ita. Bayan an dawo aji tana ta jin yara na ta ciye_ciye abunsu, suka bar ta da jin ƙamshi. Har aka tashi Inna ba ta zo ba, zuwa lokacin yunwa ta fara galabaitar da A'isha, dauriyar ta ƙare ta fara hawaye. Gashi yara duk sun tafi gida sai ita kaɗai a bakin aji a tsugunne. Wani Malami ne ya hango ta ya taho inda take, da mamaki yake duban ta ya ce. "Ke lafiya kike zaune anan ke ɗaya?" A'isha ta ce. "Innata nake jira ta zo ta ɗauke ni." Malamin ya ce. "Ayya ke ce mai ciwon idon nan ko?" Gyaɗa masa kai A'isha ta yi. Ya ce. "To yanzu zama zaki yi ki ta jiran ta kuma? Yamma ta yi ga garin hadari ya haɗo sosai, mu ma duk tafiya za mu yi, amma abun da za'a yi bari na saka a raka ki gida, ina ne gidan naku?" A'isha ta ce. "A Ƙofar fada ne." Malamin ya ce. "To mu je a raka ki, wannan hadarin ai ba zai yiyu ki zauna ke kaɗai anan ba, gashi ba gani kike ba." Sai da suka fita daga cikin makarantar yana riƙe da hannunta sannan ya samu wani yaro ya ce ya raka ta gidan Sarki, daga nan sai ta samu wani ya kai ta gida, tunda shi yaron bai san gidansu ba. Kafin su ƙarasa, garin ya ƙara duhu, an fara iska mai ƙarfi haɗe da yayyafi. Yaran sai jan A'isha yake, duk ta ƙara galabaita, tafiya kawai take yi amma jin ta take kamar zata faɗi. Yaron yana kai ta ƙofar gidan Sarki ya juya ya yi tafiyarsa, saboda zuwa lokacin ruwa ya fara ƙarfi. Ɗan_juma suna zaune a soro akan benci shi da Hamza da wani abokinsa suna karta, kamar a mafarki ya hango A'isha tsaye ta rakub'e a jikin bango, ƙura mata ido ya yi yana tuna when last da ya gan ta, ya jima bai gan ta ba gaskiya. Sai ya ga ta ƙara girma ta fara zama ƴar budurwa. A'isha tana shekaru goma sha uku a yanzu, amma saboda tana da garin jiki da ɗan tsayi idan ka gan ta zaka yi tunanin shekarun ta sun fi haka. Ruwan da ya fara dukanta ya saka uniform ɗin jikinta duk ya mammanne mata a jiki. Ɗan_juma ya ƙurawa ƙirjinta da ya ɗan fara tasawa da irgen dangi ido, nan fa shed'an ya fara buga masa ganga akan mummunan k'udirinsa akan A'isha. Wani murmushi ya yi tare da lasar leb'ensa ya ce da su Hamza. "Tsuntsu daga sama gashashshe." Bai jira cewar su ba ya miƙe ya fita ya janyo A'isha cikin zauren ta ƙarfin tsiya, bayan ya duba gabas da yamma kudu da arewa ya ga babu kowa a wajen. A'isha ta ƙanƙame Jakarta a jikinta cikin rudu ta ce. "Waye wannan? Me na yi maka? Ni ka cika ni? Mene ne haka?" Ɗan_juma ya cika ta yana murmurshin mugunta, abokansa da sai yanzu suka gane mai yake nufi suna taya shi murmurshin. Laluben Hanya A'isha ta fara yi cikin hawaye, jikinta gaba-d'aya rawa yake yi saboda tsabar tsoratar da ta yi da janyon tan da Ɗan_juma ya yi, gashi ba ta san ko wanene ba. Garin neman hanyar fita ta ƙume goshinta da garu, kuka ta saka tare da kiran sunan Inna. Cikin rashin Imani ɗan_juma ya fizgo ta tare da fizge jakar hannunta ya cillar a ƙasa, wani uban ihu A'isha ta ƙwala ta fara tittirjewa, amma saboda ruwan da ake yi mai ƙarfi ne yasa babu wanda zai jiyo ihun nata balle ya kawo mata ɗauki, cak Ɗan'juma ya ɗaga ta ya shige da ita wani ɗaki dake cikin zauren ya kullo ƙofa. Ihu sosai A'isha take yi tare da ƙoƙarin k'wace kanta daga hannun Ɗan'juma amma ta kasa. Mara masa baya su Hamza suka yi zuwa cikin ɗakin, a ƙasa Ɗan'juma ya jefar da ita sannan ya saka ƙafa ya take ƙafafuwanta da take haurin sa da su, da ido ya yiwa su Hamza alamar su danne masa A'isha. Hamza ya ƙaraso ya saka hannunsa ya toshe bakin A'isha da ƙarfi saboda da ihun kukan da take, ɗayan kuma ya daddanne mata hannayenta da iyakacin ƙarfinsa. Cikin tsantsar zalunci Ɗan'juma ya cire Hijabin jikinta ya cillar, yana wani irin murmushin zallar iskanci da duniyanci ya fara cire kayan jikinsa...........✍️

*By*
*Zeey Kumurya*
*💖 KOMAI NISAN DARE.....! 💖*

_By_
_Zeey Kumurya_

*ELEGANT ONLINE WRITER'S*

*0️⃣9️⃣*

I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 08066268951

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_

_*infection*_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_
_07084653262_
Chapter 16 · 0% Book details