← Book details Komai Nisan Dare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 55

Sashe 1

Komai Nisan Dare Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

*💖 KOMAI NISAN DARE.....! 💖*

_By_
_Zeey Kumurya_

*ELEGANT ONLINE WRITER'S*

*0️⃣1️⃣*

*ALHAMDULILLAH I'M BACK*

I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 08066268951

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_

_*infection*_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_
_07084653262_

.........Unguwar *Ƙofar fada* dake cikin garin *Kumurya*. Yarinya ce wadda baza ta wuce shekaru goma sha ɗaya zuwa sha biyu ba a duniya take tafiya cikin ƙwaleliyar ranar da ta ƙwalle. Sanye take cikin uniform na makarantar government primary school dake cikin garin. Cikin sauri take tafiyar amma kana ganin yanayinta zaka gane a galabaice take. Ƙafafuwanta duk sun yi fututu cikin ɗan Madina slippers. Wani Babban gida ta shiga mai ɗauke da ɓangarori da dama kamar yadda duk yawancin gidajen garin suke. Bayan ta wuce dogon zauren gidan ta shiga ɓangare na biyu daga b'arin dama da ɗan gudunta tana ƙwala kiran sunan "Inna! Inna." Inna dake duƙe a cikin madafi gaban murhun duwatsu ci tana hura wutar kara wadda ta mutu, gaba-d'aya ta haɗa uban gumi hayak'i duk ya turnik'e ta. Sauri take wutar ta ruru dan ta dafa dankalin Hausa kafin *A'isha* ta dawo daga makaranta, dan ta san da yunwa zata dawo tunda ba wani karin kumallon kirki ta yi ba da safe. Sai dai haƙan ta bai cimma ruwa ba har A'ishan ta dawo, sakamakon wutar data rura ta mutu gashi kuma bata da ashana, guntuwar ta kenan ta yi amfani da ita. *Inna* ta ɗago idanuwanta wanda suka fara rinewa zuwa launin ja saboda hayak'i ta dubi A'isha wadda ta shigo kamar an cillo ta. Cikin ɗan faɗa Inna tana goge idonta da ya fara tara ruwa ta ce. "A'isha ban hana ki gudu da shigowa gida babu sallama sai dai aikin ƙwala mun kira kamar wata sabuwar makauniya ba?" A'isha ta turo ɗan ƙaramin bakinta bata ce komai ba ta koma ta fice daga ɓangaren ta sake shigowa bakinta ɗauke da sallama. Girgiza kai kawai Inna ta yi tare da amsa mata ta cigaba da abun da take yi. Jakar buhun hannunta ta ajiye akan tagar ɗakinsu ƙwaya ɗaya tal dake cikin zagayen nasu sannan ta cire takalminta ta matsa kusa da Inna tana kare fuskarta da hannunta saboda hayak'i ta ce. "Inna sannu da aiki." Inna ta gyaɗa mata kai kawai. A hankali ta ce. "Inna ki kunna masa ashana mana." Inna ta ce. "Ta ƙare ne A'isha, daa da ita ai da tuni na kunna." A'isha da yunwa ke ƙwaƙular hanjin cikinta ta ce. "Bari na aro miki a gurin innarsu Ma'u." Bata jira cewar Innan ba ta yi waje da gudu ko takalmi bata saka ba. Inna tana kiran ta tare da faɗa mata Innar Ma'un bata nan amma bata ma ji ta ba balle ta tsaya. Ɓangaren Innar Ma'u a jikin nasu yake, tana shiga ta tarar da ɗakinta a kulle da ƙaramin ɗan mukulli alamun bata nan. Juyawa ta yi ta shiga ɓangaren dake kallon nasu dan arowa Inna ashanar, duk da ta san zai yi wahala su bata saboda tsanar da suka yi musu ita da innarta, kaf faɗin gidan Innar Ma'u ce kawai take k'aunarsu idan ka cire Marigayi Malam Mijin Inna. A tsakar gidan ta tarar da matan gidan guda biyu, ɗaya tana daka a turmi ɗayar kuma suna zaune akan tabarma ita da wata mata, da alama bak'uwa ta yi dan matar bata yi kala da mutanen garin ba, duba yanayin shigar jikinta gami da buɗewar idonta da uban bleaching ɗin da ta ci. A'isha ta yi sallama tare da gaishe su, babu wanda ya amsa mata sai ma wani matsiyacin kallo data samu daga matan gidan. Matar nan kuma wani irin kallo take bin ta da shi mai kama dana mamaki. A'isha bata damu ba ta dubi wadda ke zaunen ta ce. "Baaba Ramatu dan Allah ki arawa Innata ashana zata kunna wuta." A harzuk'e Ramatu ta ce. "Idan Ubanki ne ko na Asaben ya siya mun ashanar sai ki zo ki ƙwata, shegiyar yarinya kawai." A'isha ta ɓata fuska tare da kallon wadda take daka zata yi magana, sai dai bata ba ta damar hakan ba ta hanyar daka mata tsawa da faɗin. "Fice daga gidan nan dan malafar Ubanki, ita Uwar taki uban wani ya hanata siyan ashanar, zaki kwaso jiki ki taho wai a baki aron ashana, Uwar ashanar za'a baki ba ashana ba." A'isha ta marairaice ta ce. "Dan Allah Baaba Hansai yunwa nake ji kuma wutar ta ƙi......" Zaburowar da Hansai ta yi yasa ta juyawa da gudu ta bar ɓangaren. K'wafa Hansai ta yi ta ce. "Da kin cigaba da tsaiwa ai dana yi ƙasa_ƙasa dake a gurin nan, Mayyar yarinya kawai ta tsare mutane da shegun idanuwanta kamar zata lashe mu." Matar nan data kasa ɗauke idonta daga kan A'isha har sai da ta fice, ta sauke numfashi tare da kallon Ramatu wadda ta bi bayan A'isha da muguwar harara kamar idonta zai faɗo ƙasa, cikin mamaki ta ce. "Ramatu wannan kyakkyawar yarinya fa a ina take?" Ramatu ta tab'e baki cikin baƙin ciki da hassadar an cewa A'isha kyakkyawa ta ce. "Gaskiya Hajiya kin dad'e baki zo garin nan ba, yanzu baki san Mayyar matar da Malam ya auro mana ba shekara fiye da goma?" Hajiya ta ce. "Kin manta Ramatu na yi zaman Saudiyya na shekaru, ai rabona da garin nan na kusa shekara goma sha biyar sai gaisuwar Malam dana zo." Ramatu ta ce. "To kin gan ta nan dai Malam ne ya auro mana jaraba dan Mayya ce." Cikin mamaki Hajiya ta ce. "Mayya kuma?" Ramatu ta ce. "Mayya mana, ban da haka daga ya tsince ta a hanya da shegiyar jaririya a hannu bai san asalinsu ba bai san daga inda suke ba kawai ya saka aka d'aura masa aure da ita ya kawo mana ita cikin gida ya gurɓata mana zuri'a, Ubangiji ma ya so mu da arzik'i bata haihu da shi ba. Ta shanye masa kurwa sai abin da ta ce Malam ya yi yake yi kafin ya rasu, ke in tak'aice miki zance cewa ya yi ko bayan ransa kar ta bar gidan nan, ya bar mata inda take ciki a zaune halak malak tunda shi ya gina abunsa, kin ga kuwa wannan abun ai ba na dan Allah ba ne, ko mu da muke iyayen ƴaƴansa bai yi mana irin wannan kyautar ba sai ita." Hajiya ta jinjina kai tare da sakin wani ɗan murmushi, wani tunani ya ɗarsu a ranta game da A'isha. Ta dubi Ramatu ta ce. "Allah ya kyauta."
Chapter 1 · 0% Book details