← Book details Jennifer Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 82 OF 85

Sashe 82

Jennifer Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

a cen suka tadda dangi sun cika gidan hafiz ne ya kawo hjy murja yana kuka itama hjy murjan na kuka duk ta ya mutse cikin sati d'aya ta koma wata iri kamammnin ta sun canz idan ba kyakkyawan sani kai mata ba baxaka tab'a shedata ba.

jannat na kallonta gabanta ya fad'i tausayin ta ya kamata abinka ga xuciyar mai imani Abba cike da jimami xuciyar shi na cikin rud'u da damuwa yace

"wannan ishara ce da ixna !, nayi mmkin cikin 1 week ace kamar murja ta koma haka, babu kamannin ta ko kad'an,

baxanwa kowa dole ba kafin nayi mgn bari kuji abinda ya kawo ta wajanku"

muryar ta arikice kana jin muryar kasan sai addu'a idanuwanta sunyi k'ulu k'ulu wuyanta ya sirance ga k'asusuwanta birjik kamar ka k'irga

"ku.....ku......kuyi ....yii..... min afuwa..

ku....... ya..yaa ..... fe...feeee..... min....."

da sauri hindu idonta cike da hawaye tace

"na ya fe miki umma tuntuni Allah ya yafe mana xunuban mu dukan mu"

sulthana kasa magana tayi ta xuba tagumi tana kallon hjy murja tunani barkatai takeyi

tasan hjy murja ta cucesu ta xaluncrsu ta kuma k'untata musu yanxu kam xuciyoyinsu sun karye da ganin halin data ke ciki meyasa ita bataji tausayin su lokacin da suna cikin taraddadi ? meyasa taraba su da iyayensu tun suna kwana 40 aduniya ? shin ita bata da irin wannan imanin ? hmmm tabbas imani baiwa ce daga rabbi idan baka da shi bakaji dad'in hali ba.

dangin ched'e ma shirun sukayi suna jimami shekara 20 suna fad'a da junansu ta xuba musu gaba da jin haushin juna uwa uba taraba su da d'an uwansu ta sace musu y'ay'a tun suna da 40 days a duniya any'a xasu kyaleta ?

hjy Nabila xuciyarta ta karye ita yanxu bata da sauran bak'in cikin rayuwa amma har yanxu akwai wani mugun d'aci na musammam data keji aranta akan murja sbd cin amanarta da tayi uwa uba yaudarar da taimata da tsantsan butulci any'a xata iya

suna cikin wannan halin na tunane tunane hjy murja tayi wani irin kaki da kyar ta tofar da uban gudan jini kafin kace me rai yai halinsa ta mutu basu sani ba

hafiz ne ya kula yai salati da k'arfi yana jijjiga ramamman jikinta araxane suka mik'e suna kallon gawarta dangin ched'e suka mik'e had'e da fad'in Allah yaji k'anta xasu tafi Abba yace su tsaya ai mata sallah suka ce ina baxasu iya ba sum mata dai addu'ar Allah yaji kanta asalima gawar ta ta tsoro take basu fur suka tafi kad'anne suka tsaya

wasa wasa suma sauran suka gudu Abba yarasa yadda xaiyi da kyar ya lallashi hajiyarmu tai mata wankan gawa wai gawar tana wani irin wari mara dad'in ji

tun safe har k'arfe 5 na yamma Abba yana rarrashin danginsa akan xuso aimata sallah akaita fur sun bujure ransa yai masifar b'aci yarasa yadda xaiyi da gawa surukan sa ma su haisam guduwa sukayi dangin ched'en sun sugaxu kada suyi

cike da jimami dady yake kiran wayan su off ya jinjina abun wannan wacce masifa ce haka ? tun aduniya ma ace ana gudin gawarka ? sallah ma mutane sun k'i yadda suyi maka to me xaka je katarar a cen ? shedar mutane shedar samun rahama

kuka Abba yasawa dangin sa ganin hakan yasa su kaxo suna k'unk'uni malan dr Murtadha Garkuwa Abba yasa yai musu wa'axi da jikinsu ya sanyaye suka ce sun yafe mata tun da Allah yana san me yafiya Allah ya yafe musu akai mata sallah aka binneta xuciyoyinsu akarye

suma su jannat duk wa'axin akai musu suka yafe mata suna kuma neman mata gafara awajan Allah suna addu'ar suma Allah ya yafe musu

haka aka gama xaman makoki na kwana 7 aka watse .

6 months later

cikin jannat ya girma sosai haihuwa ko yau ko gobe tana shan kulawa sbd ya khaleel yace kada ta wahalar masa da ita da kuma ajiyarsa

ranar litinin tun safe take jin bayanta na ciwo kad'an kad'an haka mararta na murd'awa jefi jefi asitin da suka saba xuwa sukaje dr ta duba ta tace ba haihuwa bane juye nan haihuwar sai nan da 1 week ko kwana goma suka dawo gida dan shi ya khaleel shi ya matsa suje sbd ita ciwon bai uxxira mata ba.

suna dawowa gida ya tafi wajan maman yusuf (maman david)

ya amsowa jannat teb'a tunda sukaje gidan taci ranta ke so y'ar aikinta tai mata taci taji sam bai mata ba ita lallai irin na maman yusuf d'in takeso.

yana tafiya ciwo ya dawo d'anye tasha ruwan rubutun da momy takawo mata tun cikin yana wata 5 kamar ta k'ara ciwon ba shiri ta kira mak'ociyar ta nos Aysha Garkuwa tana xuwa ta dubata taga haihuwar ce gadan gadan cikin mintuna ta haihu bayan tasha axabar ciwo da ita kad'ai tasan shi tana haihuwa taji kamar an xare mata ciwon haka Aysha Garkuwa ta gyara d'an ta goge d'akin ta d'iban mata ruwan xafi a toilet d'inta jannat d'in ta shiga ta shek'a wanka.

kafin wani lokaci sun gyara ko ina gida ya d'au k'amshi gsky Aysha Garkuwa nada kirki sosai.

jannat hannunta rik'e da d'anta tana kallon shi kyakkyawa kalar mahaifinsa

xuciyar ta fal farin ciki mara fisaltuwa Allah ya axurta ta da baiwa na wannan sunkucecen yaron suna hira jefi jefi Aysha Garkuwa na mata hira ita kam xuciyar na kan d'an da Allah ya bata

sallamar ya khaleel sukaji cike da d'auki ta amsa yana shigowa idonshi ya sauka kan jaririn dake hannunta

cikin rud'ewa yai wajanta yana kallonta cike da mmk yarasa me xaiyi fuskarshi a washe

Aysha Garkuwa tace "congratulations kasamu k'aruwar d'a namiji Allah ya raya"

cikin kid'ima da wani irin farin ciki da bai tab'a tsintar kansa ciki ba yai wata irin tamabaya

"da gaske nine me wannan d'an ? Yanxu nima ina da d'a ? d'ana na cikina Alhamdulillah "

ya rungume d'an ak'irjinsa yana jin kansa tamkar yau shima ya diro duniyar

murmushi Aysha Garkuwa tayi ta sulale ta bar gidan dantaga abin nayine

tsurawa jannat ido yayi yana kallonta ta k'ara wata k'ima da daraja awajansa yana kallonta kamar ya cinyeta dan so.

"beautyna kece kika haifamin d'a ? "

yafad'a muryarsa asanyaye dan shi kad'ai yasan irin farin cikin daya keji

itama tsura masa ido tayi tana jin sonsa na musamman na k'ara bajewa a cikin jikinta

"Alhamdulillah jannah nagode wa Allah da yai min wannan baiwar"

janyota jikinsa yayi ya had'a da jaririn ya rumgume yana jin farin cikin da bai tab'a jinsa ba

xamewa tayi tana kallonsa

"kafad'awa su momy da mama"

d'ansa rungume a k'irjinsa ya d'auko waya momy ya fara kira tana d'agawa yace

"Albishirin ki momy"

dariya Momy tayi tace

"goro"

"sai fa kin bani tukwicina dan albishirin na musamman ne"

"xan baka kai dai fad'amin"

"yau kin xama kaka kinyi jikanki na farko kixo kiga jikan ki "

kama bakin ta tayi

murna da farin ciki ya cika mata xuciya wullar da wayan tayi ta d'auki gyale a falo suka had'u da Dady

akid'ime yake tmbyr ta

cike da farin ciki ta fad'a masa abinda ya faru hamdala yayi cike da murna Allah ya sauke ta lafiya tare suka je kan hanyar xuwansu ya kira Abba da shima tuni khaleel d'in ya fesa masa.

cikin lokaci k'alilan gidan ya cika tam da dangi kowa ka gani na cikin nishad'i hakama angon k'arnin khaleel daya kafa ya tsare yana rik'e da sabon babynsa tun su hajja da hajiyarmu na tsokanarsa har suka ga yana k'ok'arin wuce gona da iri dan k'in fita yayi sai da momy ta kira Dady suka fita tare da kyar.

haka suka cigaba da d'an biki dan kullum sai anyi shagali jika na farko agun Alhaji Adam ched'e dole kam ayi bidiri sabon baby yaga gata da soyayya duk wanda ya d'aukeahi da kyar ya ke iya ajjiyeshi a haka har nanar suna ta xagayo yaci sunan sa muhammad wohoho ! anyi b'arin nera ranar kam dan duk wani iyalin attajiri na 9ja burinsu aci taron sunan nan dasu bayan angama taron suna Abba da dady suka shirya nasu waleeman na daban wanda abokanan su sukai wa muhammad kyaututtu ka na ban mmk washe garin suna kuma k'ana nan yaran familyn ched'e suka shiryawa Muhammad nasu shagalin na daban a Ni'imal hotel Muhammad d'an dan gi duk wani yaro ko yarinya na dangin ched'e da kalar nashi gif d'in abin abin birgewa sati cur aka kwashe ana xabga walima kamar baxa adaina ba.

Muhammad wanda suke kiransa da sunan sa kyakkyawan yaro lafiyayye mai kuxari yaro mai farin jini tunda aka haife shi gidansu bai rabo da mutane na son ganin shi

watan ta bakwai da haihuwar Muhammad da yamma Haisam ya kirata sulthana tana asibiti tana na k'uda ita da ya khaleel suka tafi hnklinta atashe

suna k'arasa wa suka tadda rubayya da itama take jan tsohon cikinta dan sunyi tunanin sai ta riga sulthana haihuwa hajja da hajiyarmu da momy da hjy Nabila na asibitin haisam da hnklinsa baya jikinsa dan shi ta sulthanan sa yake,

aiki yaxo ga ma'iya haka taita salati dan nak'udar ta d'anxo da jinkiri salati kawai take tana kiran sunan momy cikin ikon Allah ta haihu ta haifi y'arta mace haisam kam bai kula da y'ar ba shi dai burinsa yaga sulthanan sa garam sai da aka gyarata yaga lfyr ta lau sannan ya dawo kan babyn yana murna kamar xai had'iye ta

ya rik'e y'ar ya k'ura mata ido yana murmushi shi kad'ai yasan meya keji aransa hajja tagaji ta ya mutsa fuska

"haisam abamu y'ar mugani ko ?"

marairaicewa yayi

"hajja ki bari nagama kallonta "

kama bakin ta hajja tayi

"oh ni Hafsatu ! xamani "

momy ce ta karb'e y'ar tace

"tafi ka bamu waje"

"momy plx har yanxu bangane dawa take kama ba,

bawa hajiyar tagani"

hajiyarmu ta amsa tana wa y'ar wasa

"ai nafita kyau dan kowa ya kalli wannan jar y'arta ka ya ganka ba sai ance taka bace"

dady da Abba ne suka shigo suna murna da jin dad'i Allah na axurtasu da jikoki.

nan da nan asibitin ya cika da dangi dan su kansu likitocin sun san y'ar dangi aka kwantar
Chapter 82 · 0% Book details