Sashe 17
Farhatul Qalbi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ingiza shi. Da shi kansa ya kasa gane menene dalilin? Ya sake matse idanu ya bude. Wannan karon kuma ba ita yagani ba. Wasu ne daban yan makarantar su ma su uku suna tafe. Girgiza kai yayi kawai. Kenan yarinyar nan gizo ta fara masa.? Har idanun sa ke nuna masa hotanta bayan ba ita din ba ce. Ya sauke zucia . Hade da kunna rediyon motan. Labarai akeyi na kasa da yadda ruwa ya yi gyara awasu guraren. Wayar sa ce ta shiga kara. Mahaifin sa ne ke kiran sa. Nan da nan ya dauka ya dauka. "Hello Abiey. Na'am, Wallahi Abiey ban karasa ba. Wani hold off ne ya tsare ni. No! Mota ce ta lalace. Amma suna gyarawa. Alright insha Allah." Dakyar aka iya gyara babbar motar data lalace. Aka samu aka mayar da ita gefe yayin da motoci suka shiga wucewa hanyar su . Zayn yaja dogon tsaki yana waiwayar motar. Banda rashin bin kaidar tuki na garin kano. Taya babbar gingimari zata biyo hanyar kananun motoci? Da takaicin hakan ya karasa gidah. Tun daga nesa masu gadi suka wangale masa gate ya shige, Kai tsaye ya wuce sashen da su Ummimi ke zama idan sun zo. Hannun sa dauke da notepad da pen. Ya shiga zagaye parlukan sashen da dakunan ciki. Harta bandakuna da duk wasu sockets na gidan sai daya dudduba komai. Ya rubuta abubuwan da suke bukatar a canza da wadanda babu a kawo. Yana gama rubutawa ya shiga mota ya koma office. Kai tsaye ya wuce babban ofishin mahaifin su dake cikin kamfanin. Dankareren ofishin mai dauke da manyan rubutun: Professor Adams Nasser. Sai daya fara knocking kafin ya bude kofar ya shiga bakinsa dauke da sallama. Mahaifin nasa na zaune akan wata kujera mai cin mutane uku. Center table na gabansa yana cike wasu takardu. Tsugunna wa yayi har kasa ya gayshe da mahaifin na su. Kafin ya miqa masa takardar da yayi rubuce rubuce ajiki. Mahaifin nasa ya karba yana dubawa. Hade da gyara zaman gilashin da ke jikin fuskar sa. Take Waheedah ta sake fado masa a zuciar sa. Ya runtse idanun sa da sauri. Kamshin turaren ta na dawainiya a kofofin hancin sa. Mahaifin nasa ya daga kai ya dube shi. "Ya akai Zayn?" Ya bude idanu da saurin sa yana girgiza kai hade da soso kasan keyar sa. "Bakomai Abiey...." "To masha Allahu. Kana ji ko?" "Eh Abiey." "Zan turawa su Simon list dinnan. Sai su kai komai gidan. Yanzu ka biya wajen Lajawa kace gobe idan Allah ya kai mu yazo gida " "Tohm Abiey. Insha Allahu " "Yauwa Allahumma bareek." "Aamin..." "Zaka iya tafiya." "Tou Abiey . A huta lapia " Ya bude kofa ya fice zuwa inda suke buga snooker shi da abokan sa, A bakin wani pool site Ko da yaje ma kasa tabuka komai yayi. Ya koma kan kujera ya zauna kawai . Useey abokin sa dake gefen sa da wayar sa a hannu yace dashi, "Maza ya ne?" "Steady oga." "Nagan ka yau pale. Akwai damuwa ne?" "Bakomai fa. Kawai nagaji ne." "Toh Allah yabamu saa. " "Aamin." Cikin haka sai ga wasu yan mata su biyu sunje wucewa, sunci ado cikin dogayen riguna fitted. Mayafan su shara shara kamar na tatar koko. Lameen dake buga snooker da Awais ya riqe bakin sa. Karasawa wajen su Useey dake zaune shi da Zayn "Wow woah, wawwww" "Meye hakan sekace ambulance. Haba kaman wasu yan kwana kwana." "Wasu masu zafi na hango mana. ." "Suna Ina?" "Gasu can zasu tsarar da me napep." Useey ya miqe yana hango su. Tsayawa sukayi su na kallon su banda Awais da Zayn. "Kallo daya bisa ka'ida dai akace." Cewar Zayn da ke zaune yana duba wayar sa. Don shi ko tashi bai yi ba. Ussey da Lameen suka tsallaka har inda suke a tsaye sunata tsara su. Kowanen su ya karbo number wadda tayi masa. Useey ya zaro sabuwar dari biyar ya mikawa mai napep din. Yaja suna masu daga musu hannu Suka tsallaka sunata dariya. Awais yace dasu, "Ba dai kyau wallahi. Zaku batawa yaran mutane lokaci. Soo not fair. " "Sai mu zauna mata su bace mana? Ga dama agaban mu?" Lameen ya amsa shi yana daria. "Rabu dashi. Kasan meyasa yace haka lameen?" "A'ah." "Saboda already an hadashi da matar aure." "Dan an hadani da wadda zan aura sai akace bani da damar kara wasu ukun? " "Eh dukda hakan kasan dai baka isa ka auro wata nan kusa ba. Sai ka fara aurar sury.." "Kyale su aboki na. Tunda sunada hankali sukayi fatali da sanin hakan." Cewar Zayn . Fuskar sa a hade. Ussey ya tuntsire da dariya har yana riqe ciki, "Banda kai da abun ka abokina. Kai da shi ai du kanwar ja ce. Kai har gwara gwara shi ma, A iya cewa yana da damar karo uku. Kai fa you can't marry any other girl da bata cikin naku family . Dole sai yarinya yar cikin dangin ku. Jinin ku, Kuma tsatson ku daya . Na yan uwan ku The Adams family.." "Ku inda ake nuna muku a har kullum ba shi kuke hanga ba. " "Rabu dasu maza, Su je suci gaba da yaudarar yaran mutane. At the very end su zo su auri wadanda basu taba tsammani ba." "Kai de banza ne Awais. Ji wani mugun fata." Dariya suka kyalkyale baki daya. Kafin su cigaba da yin snooker din su. "Ni yunwa ma nake ji." "To ina zamu je.?" "Okay I'm out. Later." Zayn yace dasu. Domin shi gaba daya baya cin abokcin eateries ko roadside ko na ordering. Harta na masu aiki bayaci sai wanda Maa ta dafa masa da hannun ta ... *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_* [11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ _NA_ _NANA HAFSATU_ _(MX)_ _AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_ _ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_ _PG:18_ Nadra ce ta shiga kitchen din. Hango Umma Hadiza tayi a kwance tanata baccinta hankali kwance, Tausayi ta bata. Ta rufo mata kofar ahankali don kada ta tashe ta. Tana komawa parlor ba dadewa sai ga mahaifiyar su ta dawo, Dr. Hameedah. Bakinta dauke da sallama, "Wa'alaykm Salam., Maaa" "Naam Nadra." Ta karasa fada a gajiye hadi da zubewa a kan kujera . Saboda madaukakiyar gajiyar data kwaso. "Ban ruwa mara sanyi Nadra " "Aha M Da sauri ta dakko ruwan a wani mini cooler kaman fridge dake gefen side tables. "Gashi." Karba tayi in da sauri tafara sha bayan tayi Bismillah. Sai data shanye tukun sannan ta yi hamdala. "Ina Hadiza?" "Tana bacci." "Allah sarki baiwar Allah." "Amma kitchen floor fa Maa." "Haba Nadra ya zaki bar ta ta kwanta a kitchen ? Bayan ga maids restroom nan ." "Maa bansani ba fa. Kawai na shiga kitchen an ba dadewa naga tana baccin. " "Ke tun dazu kina Ina?" "Moha ne ya dame ni sena solving masa puzzle. So Ina sama." "Mtssss " Dr. Hameedah ta saki tsaki hade da miqewa tsaye tayi kitchen din. Sam bataji dadin kwanciyar da Umma Hadiza tayi a tsakiyar kasan kitchen ba. Bayan ga dakin maaikata nan da suke hutawa da gado da kayan kallo aciki "Hadiza... Hadiza." "Naam Hajia. " Umma Hadiza ta tashi da sauri. Da ke batada nauyin bacci. Har damkwalin ta ya zame.Kanannadedden gashin fulani baqi wuluk me sheki ya bayyana. "Kin dawo.,? Sannu da dawowa Hajia. Bacci ya dauke ni. A gafarce ni. " Ta karasa fada kanta a k sa. "Haba Hadiza meye haka? Uhm?" "Nayi lefi Hajia. Banda sharri na bacci ya kwasheni a wajen aiki na? Dan Allah k." "Ya isa haka mana Hadiza bar bada hakuri Dan Allah. Kaman wadda kikayi wani lefi? Dawowata kenan nima. Nake tambayar Nadra kina Ina tace kina bacci a kitchen. Kinji abunda yaban haushi kenan. Taya ga dakin maaikata nan da gado aciki. Meyakwan ta nuna miki. Tayi shiru." "Wallahi batada lefi Hajia. Don basusan ma nayi bacci ba Allah. Ni kai na na gama duk abunda zanyi. Sena janyo tabarma dake iska na busawa. Wallahi bansan sanda bacci barawo ya sace ni ba. Don ko a gidah bana wannan baccin. Naurar nan ce masha Allahu take ta busa ni. " Ta karasa tana mai nuna air conditioner din dake buso sanyi Dr. Hameedah tayi murmushi kawai. "Muje na nu na miki dakin." "Da girman Allah Hajia baccin nan na gama shi haka nan. " "Kinyi sallah?" "A'ah. Anyi ne? Lalle na jima ina bacci." "Uku fa ta kusa " "Kai! Lalle na jima. SubhanAllah; bara nayi alwala. " "Ga dakin can da bandaki aciki " "Toh Hajia." Bakinta dauke da sallama ta shiga cikin dakin. Kwarai matuka ya tafi da ita. Yanayin tsaruwar sa harda kayan kallo. Tamkar dakin amarya amman ace dakin masu aiki ne? Ta jinjina kai tana sake yabawa da tsaruwar bandakin bayan tayi addua ta shiga ciki. Ta kama ruwa hade da dauro alwala bayan ta kuskuro bakinta saboda baccin da tayi. Tuni har an shimfida mata sallaya da hijabin sallah. Nan da nan ta ta zura ta fara sallah. Cikin nutsuwa da bin ka'idojin sallah. Tana idarwa ta yi adduointa daga bisani ta mayar da komai yadda yake ta koma cikin parlorn. "Hadiza kinci abincin dazun?" "Eh Hajia. Bayan naci nema