← Book details Bin Abinda Zuciya Ke So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 102

Sashe 44

Bin Abinda Zuciya Ke So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Da azuban fari yatashi wanka yasakeyi ya shirya tsaf cikin jallabiya yawuce masallaci bayan yatada mai gadi, around 6 ya shigo gidan ya wuce flat dinshi ya chanza kayan shi zuwa sport wears dinshi yadau towel ya rataya awuya yafita jogging sai around 8 yadawo zufa yagama wanke shi flat dinshi yayi yay wanka ya shirya tsaf cikin uniform dasukamai mahaukacin kyau sai uban kamshi yakeyi yafito rike da car key dinshi da waya yay flat din Ummi da sallama ya shiga Ummi na zaune kan kujera tana lazimi Asiya kuma tana dinning itada mai aikinsu suna jera breakfast akan dining tana hangoshi tun kafin ma yagaida Ummi ta taho da gudu, hannunshi takama tarike cikeda murna tace "Yayan mu ina kwana, kasan menene?" girgixa matakai yayi yana tafiya tana biyeda shi tace "yau nina hada breakfast namana abinci mai dadi" dan kallonta yayi yace "kin mana jagwalgwalo dai" da sauri tace "wlh a'a na iya girki sosai fa yayan mu, dan Allah kaci kaji, zomuje kaci" ahankali yace "ok jeki karasa abinda kikeyi, bari na gaida Ummi am coming" gyadamai kai tayi cikin wani irin murna tajuya tai dining shikuma yawuce inda Ummi kenan zaune, akusada ita ya zauna ahankali yace "good Morning Ummi" fatiha Ummi ta shafa ta kallai tace "morning soja na" kafin tace "wai wat have you been up to kwanan nan ba'a ganinka sai safe, u come back late hope everything is fine awurin aikin kako" gyadamata kai tayi yace "everything is fine Ummi na" ahankali tace "shikenan ubangiji Allah ya taimaka, yakare ka yakuma baka sa'a kaji" murmushi yayi cikeda jin dadi yace "Ameen" Ummi tace "tashi muje muyi breakfast Asiya tahanani yin komi wai ita zata mana breakfast" baice komiba suka karasa dinning din, kujera yajama Ummi zama tayi sanan ya zauna shima yana daddanna wayanshi dayaji tai karan shigowan sako, budewa yayi number Abba ne yaga yamai message hakan yasa yabude sakon.
_"Lieut is Maryam, wai I mean Mummy su Siddiqa ne, Alhaji condition is critical to the extend kusan Dr shima kwana yayi agidan nan sai dazun nan yatafi yaje yayi wanka ya shiryo yadawo, b.p shi yay high sosai, tunda safen nan daya tashi sunanka kawai yaketa kira, please nasan mun takuramaka da yawa, amma please in kanada chance come and see him kafin kaje wurin aiki dan bansan mezai fadama ba yaki fadi mani, sai kazo"_
Ajiye wayan yayi kan dinning bayan yagama karanta sakon daidai Asiya takawomai breakfast dinshi.

35&36

07012181461 chat me up a watsapp in kinason this book dan inhar kika karanta batare dakin biyaba Allah ya isa.
Sandwich tahada musu da kunun gyada, zama tayi kusadashi itama ta zuba nata duk suka faraci tanamai surutu da baya wani amsata saidai ya gyada mata kai Ummi sai murmushi take tanajin dadi, she just wish zai auri Asiya dan taga yanda Asiya ke mugun sonshi, zasuyi zamansu peacefully, koma wani matsalan gareshi Asiya yar uwanshi ce akashe arufe babu wanda yasani, but girman kai dashegen son girma irin na Sameer bazai taba barinshi ba, bazai taba barinshi ya auri Asiya ba dan gani yake kanwar kanwar kanwarshice, yana gamaci yatashi yana goge bakinshi ya kalli Ummi data bishi da kallo ganin ya mike tsaye yace "Ummi natafi" yashafa kan Asiya dake kallonshi yace "bye little girl" washemai baki tayi tace "bye yayan mu, yayan mu yaushe zaka fita dani eh?" yana tafiya yace "don't know yet" da sauri Ummi tace "a'a Soja, gobe fa asabar Sameer baka zuwa ko ina basaika fita da ita ba, kullum ita kadai agida dole gidan ya gundureta da kaman ma Mu'az na nanne tom" fado sunan Mu'az da tayi yasa tace "wai yaushe zasuyi nasu mid semester Sameer" ahankali yace "C.A sukeyi yanzu, maybe saisun gama" saikuma yajuyo ya kalli Asiya dake kallonshi duktai wani iri yace "okay shikenan get ready tommorow" washe baki Asiya tayi cikeda murna tace "thank you Yayan mu" yajuya yafita, motarshi ya shiga yafita daga gidan yadau hanyar gidansu Rahima.
Be aware of masu saida novel dinan su karbi kudaden ku kuji shiru, make sure wanan number kikama magana 07012181461 M Shakur watsap.

Inkika karanta baki biyaba Allah ya isa.
Horn yayi aka budemai Gate din gidan, babu kowa tsakar gidan sai Gardner dinsu dake watering flowers yakarasa ciki yay parking awurin parking yafito, knocking yayi agaban flat dinsu batare daya shigaba, Siddiqa ne tabude kofan idanunta sunyi jajir da alamun taci kuka ahankali tace "ina kwana" gyadamata kai yayi batare daya amsaba tace "ance ka shigo" yana biyeda ita suka shiga cikin falon, su Zeenatu yagani suna aiki, Luba na goge gogen TV, Zeena kuma na kokarin kwashe warmers din kan dinning tai kitchen dashi, atare duk suka gaidashi. "ina kwana" ahankali yace "Alhamdulillah" Siddiqa ne tace "Mummy tace inkazo inkaika wurin Abba" gyadamata kai yayi yace "okay let's go" hanyar corridor tayi yana biyeda ita har gaban dakin Abba, bude kofan tayi ahankali ya shiga ciki yana kallon Abba dake kwance kan hadadden gadonshi ga karin ruwa idanunshi a lumshe, maida kofan Siddiqa tayi tarufe tawuce tafita, ahankali yakaraso yazauna ta baki bakin gadon yakama hannun Abban yarike ahankali yana kallonshi yay shiru sai yana tuna lokacin da mahaifin su baida lpy, hawan jini da ciwon sugar ya kashe shi, haka kullum safe zaije yarikemai hannu yayta kallonshi harsai hankalinshi ya kwanta, yakai almost 5min adakin rikeda hannun Abban batare dayace komiba, bude idanu ahankali Abba yayi dasuka mai nauyi sosai ya kalli Sameer, cikin muryan marasa lafiyan nan yace "kazo Sameer?" gyadamai kai Sameer yayi yace "yes Abba nazo, ya jikin naka?" ajiyan zuciya Abba yasauke kafin da muryan ciwo sosai yace "Son kagako ni kadai mahaifiyata ta haifa kafin tarasu banda wa banda kani the only child, banda kowa Sameer but hakanan you are someone da rana tsaka dana daura idanuna akanka ka shiga raina, na yarda da tarbiyan ka, na yarda dakai Sameer, na daukeka amatsayin d'ana" yay shiru yana sauke ajiyan zuciya, kafin yay magana dawata irin murya yana sauke ajiyan zuciya yace "Ya Rahima Son? Zata warke?" gyadamai kai Sameer yayi cikin dakewa irin nashi yace "zata warke Abba karka damu, zasu bata treatment na wata shida, kadinga mata addu'a bataza kara shaye shaye ba da izinin Allah, and karka damu tana safe hands the rehabilitation centre are good babu wata matsala I can assure you that" ajiyan zuciya Abba ya sauke yace "Alhamdulillah, Alhamdulillah, Sameer inaso nafada maka wata magana? Banson kowa yajimu" ahankali Sameer yace "to Abba" murya chan kasa yace "nabaka amanan family na, na damka komi nasu a hanunka, bansan kozan tashi ba" da sauri Sameer yace "Ab...." girgiza mai kai Abba yayi yace "listen to me Son" shiru Sameer yayi ahankali Abba yace "nabaka amanan yarana, Siddiqa nada wanda zata aura sunanshi Sadiq, dukansu su hudun nariga nasai musu share a campanin Takaful, password din din shine date of birth din Rahima, Sameer duk cikin yarana Rahima batajin magana, batada hankali, she don't know what is good for her, inason kasamata tsaro da idanu sosai, sauran basu da matsala saidai wanda ba'a rasaba yauda gobe duk Allah ne maishi, dukansu insun samu miji kafara bincikawa in nagari ne ka aurar dasu, inada account guda uku, daya family account ne, daya my personal account, dayan kuma na kampanoni nane, duka password dinsu date of birth din Rahima ne which is 2000, an haifeta 1st December 2000, please Sameer karka aurar da Rahima ga kowani namiji kaji, sai namiji mai hankali, hakuri da hangen nesa da sanin yakamata" yadanyi tari da sauri Sameer yatashi zai daukomai ruwa Abba yarike shi gam yace "don't worry banjin kishi, base on little bincike danayi duk yan kwarorin samari kokuma nace abokanai da Rahima kedasu yarane, yaran dako 25yrs basufi ba, please karka aurar da ita ga mutane irinsu, nafison Rahima ta auri namijin daya mallaki hankalinshi gabaki daya, yasan me yakeyi, nasan maisa nake fada maka haka karka manta da abubuwan nan kaji d'ana" gyadamai kai Sameer yayi yace "naji Abba, amma kadena magana haka babu abinda zai sameka, zakaji sauki sanan da kanka zaka aurar da yaranka kaji Abba" gyadamai kai Abba yayi murya chan kasa yace "zuciya na namin ciwo sosai bacci nakeji, bari nai bacci Sameer" gyadamai kai Sameer yayi batare dayace komiba har lokacin yana rike da hannunshi yanamai addu'o'i, ahaka wani bacci mai mugun nauyi yay awon gaba dashi dan dama harda alluran bacci akamai.
Allah ya isa ga wacce ta karanta batare data biyaba
Chapter 44 · 0% Book details