Sashe 4
Bin Abinda Zuciya Ke So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ahankali Zeenatu ta lallabo tafito daga bayin tafito tana leke leke ganin babu kowa yasa da gudu ta kwasa tai kitchen dinsu, babban kitchen ne sosai irin family kitchen dinan dake dauke da komi irin na yan gayun nan, Siddiqa da Lubabatu tagani suna aiki, Siddiqa dake wanke kayan miyane agaban tap ta kalleta ganin ta shigo tace "zogashi kiyi blending kayan miyan nan nariga na wanke miki, stew zanyi" da sauri takaraso ta karba ahankali itakuma Siddiqa takoma gaban gas, blender ta dauka ta zuba komi ta nika saida tagama blending din tass sanan ta juye a bowl tazo wajen ta mikama Siddiqa dake zuba rice a pot bowl din, karba tayi ta ijiye agefe tana kallon fuskarta ganin duk tayi wani iri hakan yasa tace "menene Mummy tamiki fadane?" girgiza kai tayi hakan yasa Lubabatu dake yanka su carrot itama ta tsaya tana kallon Zeenah tace "to menene duk kikai wani iri?" hawayen dake kokarin zubo mata tasa hannu ta share cikin wani irin yanayi na bakin ciki tace "Ya Siddiqa wai mesa Mummy batason mu tafison Rahima, kuma muyakamata ta......" hannu Siddiqa tadaga mata tareda girgiza kai tace "Zeenah karma kifadi abinda kikeso kifadi nasan me kikeso kifada, konima nasan banson rashin kunyan Rahima but sometimes nafi putting blame din akan Mummy, Mummy ko kadan bata barinmu mu nunama Auta the difference between right and wrong kuma itama bata nuna matan, sometimes ba iskanci zalla takemana ba she really feels is very okay abinda take mana dan haka Mummy take nunamata, Mummy kullum kallon yarinya take mata, yarinyar da aka haifa jiya batasan ta girma ba yanzu, Allah dai ya shiryata, she will change eventually I know that komujima komu dade, now muci gaba da aiki kar Dady yadawo bamu gamaba" cigaba da aikin sukeyi su uku gwanin ban sha'awa sunadan taba hira.
Babansu bala'in mai kudine amma irin mutanen nanne da bai yarda ya shagalar da iyalinshi ba, dudda Mummy ta dameshi asamo musu mai aiki ki yayi acewarshi gashi da yara mata dasuka tasa tadinga koyamusu komi sunayi da kansu, saisa breakfast kawai Mummy keyi kullum shima dan suna zuwa makaranta da safene but weekend suke hadawa dakansu, gyaran gida ma haka sukeyi, dudda kudinshi bai irin ginin mansion dinan ba, gidanshi daidai daidai na rufin asiri ne 6 bedroom flat ne dakeda babban compound daya wadatu da fulawowi.
5:38pm
Horn akayi mai gadi yafito da gudu yabude gate danko a bacci yasan horn din motar Alhaji, shigowa wata babbar mota jeep tayi tai parking awurin da aka tanada dan parking, da sauri Mai gadi yarufe gate yadawo wajen parking din daidai wani magidancin mutum dake sanye da bakaken suit da neck tie ga wasu manyan littafai guda biyu masu kama da textbook a hannunshi idanunshi sanye da fararen glass kana ganinshi zaka gane daga aiki yake sabida yanayin shigan dake jikinshi, akalla mutumin zaiyi 64-65yrs, da sauri Mai gadi yadan russuna yace "barka da dawowa Alhaji ya kotu?" Mai gadi yay maganan yana mikamai hannu danya tayashi karban yan littafan hannun nashi dan murmushi yayi yabashi yace "Sani, barka da warhaka, ya aiki?" murmushi Mai gadi yayi yace "Alhamdulillah Alhaji" "to, to barkan mu" mutumin yay magana yanabin gidan da kallo wanda dabi'an shine kullu yaumin idan yadawo daga aiki saiyabi tsakar gidan da kallo yay inspecting gidanshi tsaf, idanunshine suka sauka kan kayan da aka shanyasu kan flowers yace "menake gani haka? Ban hana adena shanya a tsakar gidaba ga backyard nan inda akwai igiyan shanya kala kala, waye da wanan aikin?" Alhajin yay magana azafafe ayanda yay maganan zaka gane irin iyayen nanne masu fada da masifa sosai, cikeda girmamawa Mai gadi yace "Allah huci zuciyan Alhaji laifinane wlh, kayan Auta ce kuma tariga tafadimani idan suka bushe na shigan mata dasu na shafa'a ne, a yakuri bari na kwashe su yanzu nakaima ta su ciki" da sauri Mai gadi yajuya zaije wurin kayan cikin fada Alhajin yace "zonan, dawonan Sani" da sauri Sani yadawo, yace "this should be the last time da Rahima zata saka aiki irin wanan kayi kanajina ko?" gyadamai kai Mai gadin yayi Alhaji yajuya yay hanyar flat dinsu Mai gadi biye dashi, da sallama mai kara as usual yayi yabude kofa ya shiga ciki yana kallon ko'ina jin sallaman Abban su yasa da gudu har suna yar rige rigen fitowa su Siddiqa suka fito daga kitchen din sukai wurin Mahaifin nasu cikeda murna. "Abba oyoyo, Abba sannu da zuwa, Abba Sannu dazuwa" sosai ya shigo da masifa amma ganin yaranshi duk sun fito daga kitchen da gudu suna mai oyoyo da sannu da zuwa cike da farin ciki yasa yasakin musu murmushin dabai shirya yiba ya tsaya yace "yaran Abban su" karban littafan shi Siddiqa tayi daga hannun mai gadi, itakuma Zeenah tace "Abba nizan cirema neck tie" murmushi yayi yace "to yar albarka gashinan zoki ciremin" itakuma Lubabatu da saurinta ta zaremai jacket din suit din jikinshi har rige rige suke, murmushi mahaifin nasu yayi sosai ganin sun gama cirewa yasa yazauna kan kujera yana sauke ajiyan zuciya yace "to nagode, Allah yamuku albarka yabaku mazaje nagari" duk zama sukai kusada shi sukace Ameen Abba, Siddiqa tace "Abba yaya aiki ya kotu? Mutane nawa kasa akai kai gidan yari yau?" dariya dukansu sukayi harda Abban nasu dan Judge ne shi a federal High Court din Abuja kullum inya dawo sai sunmai wanan tambayan, murmushi yayi sosai yace "yau babu kodaya, case akayi za'a sake zama sanan za'a yanke hukunci, me kukeyi a kitchen dukanku gidan ya dumame da kamshin girkin yan matan Abban su" da sauri Lubabatu dake kusada Abban tace "girki mukeyi Abba mai dadi" waigawa yayi kafin ya kallesu duka, babu alamun wasa kan fuskarshi yace "ina Rahima?" da sauri Zeenah kaman jira take tace "Abba tana daki, Abba kagani Ya Luba saida taje takirata tazo muyi salla taki, tun sallan asuba batayiba, Abba kagayau dazu data dawo daga school tama Ya Siddiqa da Ya Sadiq rashin kunya harda cema Ya Siddiqa mayya, tacema Yaya Sadiq dansa ido, sanan muma tamana rashin kunya, kuma kaga Abba mukadai keta girki bata tayamu komiba wlh Mummy wai mubarta tahuta tagaji tana kwance adaki" shiru Abba yayi yana sauraron ta duk cikin yaran nan nashi hudu baiga wacce take bashi matsala marajin magana irin Rahima ba, gashi harga Allah kusan yafi sonta kan dukansu wanan natural haka Allah yadauramai but bataji saisa ko kadan baya wasa da ita, basa shiri, duk gidan shi kadai take tsoro, horata yake da kyau, sabida Rahima ne yanzu yake kokarin yasan yanda zaiyi yadena tafiye tafiyen nan, babu randa baya mata addu'a kan Allah ya shiryar da ita, koya zaneta taci kukan ta koshi baya hana anjima takara laifin dayadaketa akai saisa yanzu yarage dukanta sosai danta girma baiso yamata illa koyaji mata rauni tana mace, ajiyan zuciya yayi ya kalli Siddiqa babban yarshi ta farko dan dukta fisu hankali ga fadan gaskiya, ahankali yace "hakane Mamana?" gyadamai kai tayi tace "hakane Abba" kwala mata kira yashiga yi. "Rahima! Rahima, Rahima!!!"
A mugun zabure Auta ta tashi daga kan gadon jin muryan Abban su na kiranta, tsoron Abba take sosai bana wasaba, bakinta har rawa yake tsabagen firgita tace "na.....Na'am Abba, ganinan zuwa" gyara daurin towel dinta tayi tsabagen rudewa tama manta yahanata yawo agida da towel tafita daga dakin da sauri sauri gudu gudu tai falon.
Shigowa falon tayi harta karaso gaban Abba jikinta bari yake, sosa keya tayi arude tawani kwantar da murya looking so innocent kaman ta Allah, ahankali tace "sannu da dawowa Abba" tundaga kafa Abba kebinta da kallo daga ita saidan mustard towel din dake daure a kirjinta data daura tun dazu bayan tafito daga wanka ya tsaya mata acinya kanta babu dan kwali tai zuru zuru tana kallonshi, ko jiya saida yamata fada kan wanan daurin towel din gashi yauma same thing still saida ta daura, Zeenah Abba yataba batare daya janye idanunshi daka kan Auta datai zuru zuru tana kallonshi ba yace "je dakina ki dauko min dorinar nan mai baki hudu Zeenatu" dorina dataji Abba ya ambata yasa tafashe da kuka sosai jikinta narawa kaman mazari tace "Abba dan Allah ka yakuri menayi eh? Dan Allah karka dakeni banison dorinar nan please, Ya Siddiqa please kar Abba yadakeni" taja hannun Siddiqa takama tarike tana kuka sosai tana yarfe dayan hannun tana kallon Abba dahar lokacin kallonta yake irin kallon nan dake saka hanjin cikin yara kadawa in fear.
Babansu bala'in mai kudine amma irin mutanen nanne da bai yarda ya shagalar da iyalinshi ba, dudda Mummy ta dameshi asamo musu mai aiki ki yayi acewarshi gashi da yara mata dasuka tasa tadinga koyamusu komi sunayi da kansu, saisa breakfast kawai Mummy keyi kullum shima dan suna zuwa makaranta da safene but weekend suke hadawa dakansu, gyaran gida ma haka sukeyi, dudda kudinshi bai irin ginin mansion dinan ba, gidanshi daidai daidai na rufin asiri ne 6 bedroom flat ne dakeda babban compound daya wadatu da fulawowi.
5:38pm
Horn akayi mai gadi yafito da gudu yabude gate danko a bacci yasan horn din motar Alhaji, shigowa wata babbar mota jeep tayi tai parking awurin da aka tanada dan parking, da sauri Mai gadi yarufe gate yadawo wajen parking din daidai wani magidancin mutum dake sanye da bakaken suit da neck tie ga wasu manyan littafai guda biyu masu kama da textbook a hannunshi idanunshi sanye da fararen glass kana ganinshi zaka gane daga aiki yake sabida yanayin shigan dake jikinshi, akalla mutumin zaiyi 64-65yrs, da sauri Mai gadi yadan russuna yace "barka da dawowa Alhaji ya kotu?" Mai gadi yay maganan yana mikamai hannu danya tayashi karban yan littafan hannun nashi dan murmushi yayi yabashi yace "Sani, barka da warhaka, ya aiki?" murmushi Mai gadi yayi yace "Alhamdulillah Alhaji" "to, to barkan mu" mutumin yay magana yanabin gidan da kallo wanda dabi'an shine kullu yaumin idan yadawo daga aiki saiyabi tsakar gidan da kallo yay inspecting gidanshi tsaf, idanunshine suka sauka kan kayan da aka shanyasu kan flowers yace "menake gani haka? Ban hana adena shanya a tsakar gidaba ga backyard nan inda akwai igiyan shanya kala kala, waye da wanan aikin?" Alhajin yay magana azafafe ayanda yay maganan zaka gane irin iyayen nanne masu fada da masifa sosai, cikeda girmamawa Mai gadi yace "Allah huci zuciyan Alhaji laifinane wlh, kayan Auta ce kuma tariga tafadimani idan suka bushe na shigan mata dasu na shafa'a ne, a yakuri bari na kwashe su yanzu nakaima ta su ciki" da sauri Mai gadi yajuya zaije wurin kayan cikin fada Alhajin yace "zonan, dawonan Sani" da sauri Sani yadawo, yace "this should be the last time da Rahima zata saka aiki irin wanan kayi kanajina ko?" gyadamai kai Mai gadin yayi Alhaji yajuya yay hanyar flat dinsu Mai gadi biye dashi, da sallama mai kara as usual yayi yabude kofa ya shiga ciki yana kallon ko'ina jin sallaman Abban su yasa da gudu har suna yar rige rigen fitowa su Siddiqa suka fito daga kitchen din sukai wurin Mahaifin nasu cikeda murna. "Abba oyoyo, Abba sannu da zuwa, Abba Sannu dazuwa" sosai ya shigo da masifa amma ganin yaranshi duk sun fito daga kitchen da gudu suna mai oyoyo da sannu da zuwa cike da farin ciki yasa yasakin musu murmushin dabai shirya yiba ya tsaya yace "yaran Abban su" karban littafan shi Siddiqa tayi daga hannun mai gadi, itakuma Zeenah tace "Abba nizan cirema neck tie" murmushi yayi yace "to yar albarka gashinan zoki ciremin" itakuma Lubabatu da saurinta ta zaremai jacket din suit din jikinshi har rige rige suke, murmushi mahaifin nasu yayi sosai ganin sun gama cirewa yasa yazauna kan kujera yana sauke ajiyan zuciya yace "to nagode, Allah yamuku albarka yabaku mazaje nagari" duk zama sukai kusada shi sukace Ameen Abba, Siddiqa tace "Abba yaya aiki ya kotu? Mutane nawa kasa akai kai gidan yari yau?" dariya dukansu sukayi harda Abban nasu dan Judge ne shi a federal High Court din Abuja kullum inya dawo sai sunmai wanan tambayan, murmushi yayi sosai yace "yau babu kodaya, case akayi za'a sake zama sanan za'a yanke hukunci, me kukeyi a kitchen dukanku gidan ya dumame da kamshin girkin yan matan Abban su" da sauri Lubabatu dake kusada Abban tace "girki mukeyi Abba mai dadi" waigawa yayi kafin ya kallesu duka, babu alamun wasa kan fuskarshi yace "ina Rahima?" da sauri Zeenah kaman jira take tace "Abba tana daki, Abba kagani Ya Luba saida taje takirata tazo muyi salla taki, tun sallan asuba batayiba, Abba kagayau dazu data dawo daga school tama Ya Siddiqa da Ya Sadiq rashin kunya harda cema Ya Siddiqa mayya, tacema Yaya Sadiq dansa ido, sanan muma tamana rashin kunya, kuma kaga Abba mukadai keta girki bata tayamu komiba wlh Mummy wai mubarta tahuta tagaji tana kwance adaki" shiru Abba yayi yana sauraron ta duk cikin yaran nan nashi hudu baiga wacce take bashi matsala marajin magana irin Rahima ba, gashi harga Allah kusan yafi sonta kan dukansu wanan natural haka Allah yadauramai but bataji saisa ko kadan baya wasa da ita, basa shiri, duk gidan shi kadai take tsoro, horata yake da kyau, sabida Rahima ne yanzu yake kokarin yasan yanda zaiyi yadena tafiye tafiyen nan, babu randa baya mata addu'a kan Allah ya shiryar da ita, koya zaneta taci kukan ta koshi baya hana anjima takara laifin dayadaketa akai saisa yanzu yarage dukanta sosai danta girma baiso yamata illa koyaji mata rauni tana mace, ajiyan zuciya yayi ya kalli Siddiqa babban yarshi ta farko dan dukta fisu hankali ga fadan gaskiya, ahankali yace "hakane Mamana?" gyadamai kai tayi tace "hakane Abba" kwala mata kira yashiga yi. "Rahima! Rahima, Rahima!!!"
A mugun zabure Auta ta tashi daga kan gadon jin muryan Abban su na kiranta, tsoron Abba take sosai bana wasaba, bakinta har rawa yake tsabagen firgita tace "na.....Na'am Abba, ganinan zuwa" gyara daurin towel dinta tayi tsabagen rudewa tama manta yahanata yawo agida da towel tafita daga dakin da sauri sauri gudu gudu tai falon.
Shigowa falon tayi harta karaso gaban Abba jikinta bari yake, sosa keya tayi arude tawani kwantar da murya looking so innocent kaman ta Allah, ahankali tace "sannu da dawowa Abba" tundaga kafa Abba kebinta da kallo daga ita saidan mustard towel din dake daure a kirjinta data daura tun dazu bayan tafito daga wanka ya tsaya mata acinya kanta babu dan kwali tai zuru zuru tana kallonshi, ko jiya saida yamata fada kan wanan daurin towel din gashi yauma same thing still saida ta daura, Zeenah Abba yataba batare daya janye idanunshi daka kan Auta datai zuru zuru tana kallonshi ba yace "je dakina ki dauko min dorinar nan mai baki hudu Zeenatu" dorina dataji Abba ya ambata yasa tafashe da kuka sosai jikinta narawa kaman mazari tace "Abba dan Allah ka yakuri menayi eh? Dan Allah karka dakeni banison dorinar nan please, Ya Siddiqa please kar Abba yadakeni" taja hannun Siddiqa takama tarike tana kuka sosai tana yarfe dayan hannun tana kallon Abba dahar lokacin kallonta yake irin kallon nan dake saka hanjin cikin yara kadawa in fear.