← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 81 OF 83

Sashe 81

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Nan take na kara tabbatar ma da kaina Sultana bazata tab'a sona ba.
Sannan ko kwanta mata na ke yi bazata bar kishi da ni da gasa dani ba.
Na fahimci duk wani abu da zata ganni da shi sai ta yi kokarin mallakan wanda ya fishi a Tunaninta ta fini, sannan ta na ganin Assadiq ya fi sona shiyasa ya ke nuna mata rashin adalci.
Alhalin adalci daidai gwargwado yana yi mata kishinta da Zarginta da Rashin mutumcinta yasa ta kasa gane komai.
Tundaga Lokacin na fahimci ita Rayuwa ba ta cika 100% bisa dari  in kaji dad'i a wani bangaren Dole ta wani bangaren asamu akasin haka.
Sai ka yi hakuri da yadda taka Rayuwar ta zo, haka kila kafi wasu wasu ma sun fika.
Cikin ikon Allah na Cigaba da Renon cikina Amna wajen wata uku ta yi min sannan ta koma gida tunda za ta shiga makaranta.
Saboda nuna godiya da ni da Assadiq muka maidata har gida tare da shatara na arzikin da Assadiq ya yi mata.

Mun yi mata sabbin d'inkuna kayan kwalliya littafan makaranta da jaka da takalma Assadiq har karaman Ipad ya siya mata saboda karatu.
Adda Rukayya na ta godiya da Mijinta Adamu dai kamar ba shi ba.
Ya zauna da Mijina suna ta Hira har yana kallona yace"Ikon Allah Hasiya ki yi hakuri da abubuwan da na rika aikata miki a baya, wlh sai daga baya na kara gane cewa duk zencen mutane ne, sannan naji wani wa'azin kwanaki da akace rashin yarda da Allah nw in wani ya samu bawa yana nuna mutum bai yarda da musulunci da ya ke ciki ba kenan."
Assadiq yace"Kwarai ma da gaske, ai acikin shikan shikan musulunci akwai yarda da kaddara mummuna ko kyakyawa."
Sai ga shi zamu tafi Amna na hawaye nima wlh na saba da yarinya mai kwazo ga hankali.
Assadiq yace ta bar kuka duk sanda ta samu hutu zai rika zuwa yana Daukanta.

A gidan mu na zariya muka sauka da ya sha kura, Allh sarki maman suhailat sun tashi d anta ya gina gida sun koma can wajen kabama.
Ummi ma sun tashi gidan duk bakin Fuskoki ne.
Dakin ma Assadiq yace zai sake shi, sai dai in ya samu kudi ko karamin gida ne ya gina mana in da zamu rika sauka in mun zo garin.
Wannan zuwan da muka yi Amma ta matsamin sai na ne gidan Baba Tanko tare da Assadiq muka je  har gidan Baba Saminu.
Sannan na kaisa gidan Goggon kona itama suka gaisa sai kuma jin kunya, suna ta kame kame a raina nace ku kuka sani ta bakin Amma tace mu mun riga mun sauke hakkin zumumcin da ke kanmu.
Kuma Assadiq ya yi musu alheri suna ta Tambayan yan biyu nace suna Gusau.
Hatta wasu daga cikin yayansu masu zagina da mugun baki na gansu, sai kunya da sunne kai.
Mugun abun da suka Rika jefani da shi ya koma musu.
Tunda cikin ya'yan Baba Tanko akwai sakakkiya auranta uku baya zama ta na gida, nidai nace alhakina ne ya kamasa da ya rikamin mugun baki in ma na yi aure bazan zauna ba Tunda na zama bakar Annoba gobara daga kogi mganinta sai Allah ba.
Daga zariya ne muka je Gusau nan  muka yi jima Tunda Lokacin hutun karshen shekara ne.
Su Asim sun zama yan gusau ina wuri ma kamar ba na nan Umma da Mama ne iyayensu yanzu.
Muna garin Siyama ta haihu har aka yi shagalin suna.
A sunan ne su Anty Sakeena  ta yi ma Sajida tsiya lokacin da bazawarinta ya kirata a waya.
Sai a lokacin naji ashe wani Tsohon saurayinta da ya nemeta tun tana Budurwa ne ya Dawo kuma abun mamaki bai yi aure ba shi har yanzu.
Saleema ta zo sunan itama da Cikinta Tunda sau biyu ta na samun b'ari.
Ita kuma asibiti ta ke zuwa Tunda in dai ta samu ciki sai ya zube.
Duk ta rame ta zub'e ba wannan gayun sai a hankali.
Shahida ke bada labari a wajen suna irin yadda Baba Jibril ya rika nuna ko Salimar ne ke da wani Laluran a jikinta? Kamar ya na nuna shi fa matsalan daga wajen salima ne ya manta Allah ke kashewa da Rayawa.
To ina Baba Jibril yasan Allah shi ban da neman duniya ai bai saka ma komai gaba ba.
Don ma Saboda Abba ne yana karuwa ta bangarensa da Tuni salima ta wulakanta kuma domin mijinta na sonta.
Ammh in akace Salima ta yi b'ari suna asibiti ji ya ke yi kamar kud'insa ne za su yi kuka ya yi ta mganganun rashin Takwalli.
Ni tausayi ta bani, ina auna irin yadda Rayuwar mata ke fuskata a wannan zamanin Allah dai yasa mu dace
Ya kuma cika zuciyoyin mu da Takwalli da yakana.

Wannan karon a Abuja na Haihu ammh kuma a Gusau aka yi taron suna. Kuma na haihu da kaina batare da an sake Farkani ba
Ban samu macen da na dinga kwad'ayi ba namiji na kara haifa.
Assadiq kuma ya saka masa suna TAHIR.!
Tahir ya yi murna Farincikin da ya Hauwa'u ta yi min sati a Gusau ta kuma zo min da kayan arziki daga Takwaransa Tahir Yusuf Daura.
Tahir da ya zo barka ya Dauki takwaransa ya rike cikin Farinciki yace"Abokina me na yi maka da na Cancanci ka Tsallake sunayen mutanen da suka fi daraja ka saka ma d'anka sunana?
Kai tsaye Assadiq yace"Da taimakon ka na auri Siya, Tahir ka yi min komai da  bani da bakin da zan gode maka."
Tahir kamar ya yi kuka yace"Me na yi maka! Ni da na rika adawa da auran ina ta cewa baku dace da juna ba, ashe muna namu Allah ya gama nashi ashe ashe har Takwara ma yar Zabiyar matarka zata Haifa min Nagode kwarai Allah ya raya Junior Tahir yasa ya Biyo mai halinsa."
Assadiq na jijjjiga kafad'ansa yana fad'in "Ameen ammh dai ka kara sani sunan Matata Hasiya ba Zabiya ba."
A tare duk muka saka musu dariya ni da Hauwa'u.
Kowa yaji sunan yaro sai yace Tahir ya cancanta.

A gusau na yi jego na Umma da Mama na Tsaye kaina suna kula da ni.
Sai dangina suka zo nan gusau karon Farko da su Adda Fati suka tako gidan su Assadiq.
Wajen kwanansu hud'u sun kuma ga karamcin da mutuntatawa.
Ramatu ta zo har da Inna Talatu itama Habiba ce bata zo ba tunda ta jima wajen Amma.
Bani da matsalan komai ina Bangaren Assadiq Sajida na shigowa ta zauna dani mu yi ta hira kamar bamu tab'a fad'a ba.
Assadiq kuma na tare da matarsa yar Rigima, Sultana dai bata samu ciki ba ta gama rigimamta ta Hakura.
Ammh har yau har gobe ba wani jituwa tsakanina da ita.
Ni kuma in muka had'u ni ke fara gaisheta ko da bazata amsa ba.
Daga baya da taga ina tura mata Aniyarta sai ta dawo tana gaisheni in muka had'u ammh shima ba koda yaushe ba.
Wannan karon na tada ma Amma Rigima sai da tazo har Gusau ta ganni ita da Matar Hamma Isuhu da Habiba da Badd'o
Umma ta yi musu kyakyawan karb'a.
Sai anan taga kammanina da Amma.
Ta ga inda na Dauko hasken Fatata kamar ita jajir.
Duk da yanayin Rayuwa da yasa Hasken Fatan Amma ya dishe ammh har yanzu da haskenta sannan Zanenta na Fulani na nan a gefe da gefen bakinta.
A bangaren Umma ta sauka nan Taga su Asim sun girma da suka ganta sun manta da ita sai da suka kara ganinta sannan suka fara yarda da ita.
Umma da ta kai Amma bangaran Innani tace mahaifiyata ce.
Innani na saman kekenta ta rika sakama Amma albarka ta na fadin ni alheri ce ga Rayuwar magajin gida.
Amma bata so ta jima ba kwana Biyu ta  sobsu yi su koma na lallab'eta ni da Assadiq ta amince zata yi sati.
Anty Surayya ta zo ta gaida Amma kuma har girki ta yi ta aiko mata dashi.
Ana gobe Amma za su tafi, yan'uwan Saurayin da ya ke son auran Sajida suka zo har gida har Falon Umma suka yi tijaransu.
Da sunan cewa su dan'uwansu bazai auri bazawara alhalin bai bata aure ba ita kuma Sajidan suka ja mata kunnin ta rabu da d'anuwansu ruwa ba sa'an kwando ba ne.
Tana bazawara sai ta makale ma Saurayi tace zata aura ko kunya bata ji ba?
Umma da ta yi musu magana tace ai hakan ba Haramun ba ne.
Wata cikin su ta kalleta kai Tsaye tace"Malama Rufe ma mutane baki, kinsan da haka nan da d'anki ya auro miki bazawara ki ka tada tsiyan sai ya saketa? A she wanzami baya son Jarfa ita wato ba yar ki bace tunda yanzu yarki ce kin ce ba Haramun ba ne mana."
Sai Umma ta yi shuru ta koma ta na kuka Sajida ce tace su bar musu gida in Allahu ta rabu da Isma'il tunda abun ya zama haka.
Har da Amma a masu ba ma Umma hakuri tunda suna wajen aka yi ni sai daga baya Sajida ta zo ta na fad'amin.
Umma ta yi ta kuka ta na fadin alhakina ne ya kamata.
ta tozartani da Farko gashi itama abunda ta aikata ya na dawo mata a kanta.
Chapter 81 · 0% Book details