Sashe 28
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har gaban Innani Surayya ta kaini na gaisheta ta amsa ta na kallon Surayya kafin tace"Ita wannan fa?
Ta fad'a a gatsine Surayya tace"Matar magajin gida ce Asiya."
Da Sauri innani ta washe baki kafin tace"Allah Sarki sannu yar nan, ki yi hakuri da abunda ya faru jiya duk sharrin shed'an ne, mu bamu ki karban ki ba ne, Daman saboda marainiyar nan ne Sulsana ba ta da kowa sai mu, kuma ni daman ban ja ba ina Ruwana da shiga Hurumin Allah. Ni dai yar nan rokona gareki ki rike magajin gida Amana kina dai gani bayan shi Sulaimanu ba shi da wani magaji sai shi, in ya rasashi bansan wani hali zai shiga ba, ni dai fatana kada wani abu ya samu magajin gida shine kawai damuwata."
Sai kuma ta saka kuka ta na wani gyara gilashinta kafin tayi kyafci ta na jan hanci tace"Ashe da rabon zan ga kwan magajin gida ina Raye? Allahu akbar yar nan Allah ya rabaku lafiya.'
Ta ke fad'a ta na jan majina, Surayya na gefe ta na mirmishi.
Sultana da tun shigowarmu ta maida kanta ta sunkuyar sai da ta dago ta na kallon Innani lalle ka tsoraci Duniya ka Tsaraci Innani, yanzu nan fa zagin Hasiyar ta gama yi ta na fadin sai magajin gida ya saketa ammh shine har ta sauya mgana.
Ni dai kaina na kasa, Innani ta na ta addu'a ina amsawa da Amin sai da wayar Surayya tayi kara ta fita waje sai gashi ta dawo ta na cemin na tashi mu tafi Sadiq yace sun shirya.
sallama na yi ma Innani ta amsa ta na Fad'in "Yanzu chan Zariya zaku tafi?
Sai na amsa mata da Eh da sauri tace"To Allah ya tsare haka sulaimanu yace min da ya shigo da safe ya gaisheni, Sulaimanu bawan Allah nan ya zauna yana ta min nasiha, tuni ni na Saduda daman Saboda Sulsana ce in naga ta na kukan nan duk sai na Rude na rasa bayan wa zan bi."
Sai kuma ta yi shuru kafin tace"Ni fa an sakani a Tsakiya magajin gida ma fushi ya ke yi dani Tun jiya ko shashen nan bai kara kallo ba, oh ni Dije in nabi bayan Sulsana ace na yi son kai, in nabi bayan wannan yar Farar sai ace na so bare naki nawa."
Ta ke fad'a kamar gaske ni kaina sai da ta bani Dariya.
Surayya tace"Bakomai Innani in kika so nakin kika had'a da baren kika so gabadaya baki yi laifi ba."
Da haka ta kashe bakin Innani muka fita tana mana fatan Allah ya kaimu lafiya.
Har ta na fadin"Yar nan sai yaushe?
Na kasa bata amsa Anty Surayya tace"Sai tazo gabanki, ai ke zaki karbi zuwan d'an magajin gida."
Innani sai kuka,ta na fadin Allah yasa tana raye zata gani har muka fita bata daina kuka ba.
Muna fita Siyama ta kalli Innani kafin ta yi mgana Sultana ta mike fuu ta shige uwar dakin Innani.
Daga innani har Siyama suka bi ta da kallo, Innani ta tce"Ita kuma wannan me aka yi mata?
Siyama tace"Ba ke bace, yanzu kina nuna kina goyon bayan mu, ammh kuma yanzu kina ganinta kika wani ware mana baya."
Innani ta saki baki kafin ta yi mgana Siyamar ta mike tabi bayan sultana su bacin ransu Yaya Sadiq baisan ma yazo ya Lallashi Sultanan ba.
Innani ta bi su da kallo kafin ta tabe baki tace"Kaji min tsiya, yaran da ba su san abun arziki ba, na yi mgana Sulaimani da magajin gida sun ce ina ja da Ubangiji ai dole nayi shuru da bakina."
********
Mun dauki hanya wajen goma saura na safe, Kamar kada mu rabu da Anty Surayya saboda kirkinta Abba ma ba ruwansa kafin ma na gaishesa shi ya fara gaisheni.
Sadiq ke tukin Abba na gidan gaba ni kuma ina baya, suna tafe sai hiran su suke yi gwanin sha'awa.
Abba ne ke juyawa yana sakoni a Hirar shi kuma Assadiq bini bini sai ya Waiwayoni yana tambayata ya ya? Saboda yaga ina ta mutsu mutsun Tunda Cikin nan ya fara nauyi zama ya ke min wahala.
Ina jin su suna waya da Tahir yace shima ya na kan hanya, sai bayan azahar muka isa Zariya tunda su Abba sun tsaya sun yi sallah Sadiq ya siyamin Tsire da Lemu ni ban ma ciba saboda zuciyata naji ta na tashi.
A samaru muka Dauki Tahir, na gaishesa ya amsa a dakile sai dai ya gaida Abba cikin Fara'a.
Ni na rika numa musu hanyar gidan Baba Tanko har muka iso.
Naga motarsa ma a waje yasa nace musu yana gida, sai Abba yace na shiga nace suna jiransa.
Ina shiga gidan da sallama da duka matansa naci karo suma sun yi mamakin ganina.
Muka gaisa kai tsaye nace"Baba na gida?
Sukace min eh yana gida sai nace a waje ana jiransa nazo tare da baki.
Amaryar ce ta shiga dakinsa ta gayamasa ina tsaye ko wurin zama ba su bani ba sai dai naga sai kallona suke yi kamar sun ga bakuwar Fuska.
Baba Tanko ya fito yana saka Hula Cikin mamakin ganina yace"Hasiya? Ko ba Hasiya bace?
Kai Tsaye nace'Ni ce Baba, ina yini?
Bai amsa ba illah ce min da ya yi"Lafiya? Wasu baki ne ke nemana?
Nima kai Tsayen nace"Mijina ne da mahaifinsa."
Ido ya waro kafin yace"Wai daman auran naki bai mutu ba?
Sai da kuma ya fad'a yaga cikin jikina sai ya yi gaba yana fad'in"To to bari naje na gani."
Na bisa da kallo ina jin wani abu na sukan raina, gajiya na yi da Tsayuwa har sai da na jingina.
Ganin haka ne yasa Amaryan baba ta bani kujeren tsugunno na zauna ina jin bayana sun kara kagewa.
Achan waje kuwa Baba Tanko na fita wazai gani? Sai yaga Alhaji Sulaiman Shinkafi Surukin Alhaji Jibril.
Ya bashi hannu suka ka gaisa lokaci d'aya yana fadin"Ah wa na ke gani kamar Alhaji Sulaiman?
Abba ya yi mirmishi kafin yace"Ni ne, kamar yan'uwan Alhaji Jibril na Zariya ko?
Baba Tanko jiki na rawa yace"Ba Shakka baka manta ba?
Ya fad'a ya na kallon su Sadiq wanda ke sanye da Shadda Deep Blue da Hula Tahir ma manyan kayane ajikinsu nan take ya gane su.
Cikin mamaki ya kalli Abba yana fadin"kada dai kace min wannan d'an ka ne?
Abba ya kalli Sadiq kafin ya yi mirmishi yace"Eh yaron wajena ne."
Baba Tanko sai ya kasa mgana, jiki na rawa ya Bude musu falonsa na waje suka shiga.
Bayan sun gaisa sai gashi ya Dawo cikin gida yana rawan baki a kawo Ruwa ya kalleni zaune ya na fadin"Ke ashe mijin naki surukin Baban ki Jibril ne? Gidansa ai Mubarak ya Dauko mata."
Ina jinsa bance masa komai ba matansa ne ke ta mamaki, suna ta neman jin mgana a bakina na yi musu gum.
Abba ne kadai ya sha ruwa ban da su Sadiq bayan an kara gaisawwa Abba ya kalli Baba Tanko Lokaci daya ya na nuna su Sadiq kafin yace"Ina fatan ka gane su ko?
Baba Tanko yace"Tabbas na gane su shekaru uku haka nan suka zo na Daura masa aure da Daya daga cikin ya'yan dan'uwana da ya rasu cikin Shedu masu yawa"
Abba ya jinjina kai kafin yace"Daman tabbacin hakane na ke so na samu, Saboda alokacin da ya yi auran bai sanar dani ba sai daga baya."
Baba Tanko ya rike baki kafin yace"Kaji ko? Daman sai da na tambayesa, domin nasan da sanin ku dai bazaku bari ya auri bakar tsiya ya kawo muku cikin zuru'a ba"
Abba ya yi mirmishi bai yi mgana ba sai kawai Baba Tanko ya gyara zama yana ba ma su Abba labarin irin bakin tsiyar Hasiya da maganar cewa ita ta yi sanadiyar mutuwar dan'uwansu bayan ya rasa komai.
Tahir ya kalli Sadiq alamun kadai ji ko?shi kuma sai ya yi kamar bai gani ba.
Abba ne ya dakatar da Baba Tanko da cewa za su tafi, 10k ya ijiye masa a gabansa sannan ya mike.
Har waje ya rakosu kamar ya yi musu Sujjada, Sadiq ne yace a kira ni mu tafi sai gashi ya shigo zakada zakadan yana fadin na taso suna jirana.
Na yi ma matansu sallama na fito sai gashi yau nice Baba tanko ke sakama albarka Harda Allah ya Saukeni lafiya.
Daganan har gida suka kaini, Sadiq kunyar tasa bai shiga ba sai da Abba yace ya taikamamin da jakata mana.
Sannan ya fito daga Motar
Ni kuma sai na Roke Abba ya shigo yaga dakina ko ruwa ya sha.
Abba bai yi gaddama ba ya Bude mota ya fito kuma yace Tahir yazo shima ya shiga.
Sai ga Abba da Tahir a falona jikina na rawa naje na kawo musu Ruwa, Abba ya sha shi da Sadiq Tahir kuma yace shi baya jin kishi.
Abba ya saka albarka ba jimawa yace bari su kama hanya tare da Tahir suka fita Assadiq kuma sai da ya Tsaya ya Rumgumeni ya sumbaceni.
Sannan yace na kula da kaina zamu yi waya.
Nice har waje na rakasu sai da naga Fitar motarsu layin sannan na dawo cikin gida Maman suhailat nagani Bakina na rawa nace mata Baban Assadiq ne da abokinsa suka kawoni gida.
Sai ta faramin fad'a ashe ba na garin ammh shine ban ce zan yi tafiya ba kamar ana zaman gaba.
Sai na fahimci laifina na kuma bata Hakuri.
Ranar na kwana cikin Farimciki ko bakomai abubuwa suna Faruwa A yadda ban yi Tunani ko tsammani ba.
Ta fad'a a gatsine Surayya tace"Matar magajin gida ce Asiya."
Da Sauri innani ta washe baki kafin tace"Allah Sarki sannu yar nan, ki yi hakuri da abunda ya faru jiya duk sharrin shed'an ne, mu bamu ki karban ki ba ne, Daman saboda marainiyar nan ne Sulsana ba ta da kowa sai mu, kuma ni daman ban ja ba ina Ruwana da shiga Hurumin Allah. Ni dai yar nan rokona gareki ki rike magajin gida Amana kina dai gani bayan shi Sulaimanu ba shi da wani magaji sai shi, in ya rasashi bansan wani hali zai shiga ba, ni dai fatana kada wani abu ya samu magajin gida shine kawai damuwata."
Sai kuma ta saka kuka ta na wani gyara gilashinta kafin tayi kyafci ta na jan hanci tace"Ashe da rabon zan ga kwan magajin gida ina Raye? Allahu akbar yar nan Allah ya rabaku lafiya.'
Ta ke fad'a ta na jan majina, Surayya na gefe ta na mirmishi.
Sultana da tun shigowarmu ta maida kanta ta sunkuyar sai da ta dago ta na kallon Innani lalle ka tsoraci Duniya ka Tsaraci Innani, yanzu nan fa zagin Hasiyar ta gama yi ta na fadin sai magajin gida ya saketa ammh shine har ta sauya mgana.
Ni dai kaina na kasa, Innani ta na ta addu'a ina amsawa da Amin sai da wayar Surayya tayi kara ta fita waje sai gashi ta dawo ta na cemin na tashi mu tafi Sadiq yace sun shirya.
sallama na yi ma Innani ta amsa ta na Fad'in "Yanzu chan Zariya zaku tafi?
Sai na amsa mata da Eh da sauri tace"To Allah ya tsare haka sulaimanu yace min da ya shigo da safe ya gaisheni, Sulaimanu bawan Allah nan ya zauna yana ta min nasiha, tuni ni na Saduda daman Saboda Sulsana ce in naga ta na kukan nan duk sai na Rude na rasa bayan wa zan bi."
Sai kuma ta yi shuru kafin tace"Ni fa an sakani a Tsakiya magajin gida ma fushi ya ke yi dani Tun jiya ko shashen nan bai kara kallo ba, oh ni Dije in nabi bayan Sulsana ace na yi son kai, in nabi bayan wannan yar Farar sai ace na so bare naki nawa."
Ta ke fad'a kamar gaske ni kaina sai da ta bani Dariya.
Surayya tace"Bakomai Innani in kika so nakin kika had'a da baren kika so gabadaya baki yi laifi ba."
Da haka ta kashe bakin Innani muka fita tana mana fatan Allah ya kaimu lafiya.
Har ta na fadin"Yar nan sai yaushe?
Na kasa bata amsa Anty Surayya tace"Sai tazo gabanki, ai ke zaki karbi zuwan d'an magajin gida."
Innani sai kuka,ta na fadin Allah yasa tana raye zata gani har muka fita bata daina kuka ba.
Muna fita Siyama ta kalli Innani kafin ta yi mgana Sultana ta mike fuu ta shige uwar dakin Innani.
Daga innani har Siyama suka bi ta da kallo, Innani ta tce"Ita kuma wannan me aka yi mata?
Siyama tace"Ba ke bace, yanzu kina nuna kina goyon bayan mu, ammh kuma yanzu kina ganinta kika wani ware mana baya."
Innani ta saki baki kafin ta yi mgana Siyamar ta mike tabi bayan sultana su bacin ransu Yaya Sadiq baisan ma yazo ya Lallashi Sultanan ba.
Innani ta bi su da kallo kafin ta tabe baki tace"Kaji min tsiya, yaran da ba su san abun arziki ba, na yi mgana Sulaimani da magajin gida sun ce ina ja da Ubangiji ai dole nayi shuru da bakina."
********
Mun dauki hanya wajen goma saura na safe, Kamar kada mu rabu da Anty Surayya saboda kirkinta Abba ma ba ruwansa kafin ma na gaishesa shi ya fara gaisheni.
Sadiq ke tukin Abba na gidan gaba ni kuma ina baya, suna tafe sai hiran su suke yi gwanin sha'awa.
Abba ne ke juyawa yana sakoni a Hirar shi kuma Assadiq bini bini sai ya Waiwayoni yana tambayata ya ya? Saboda yaga ina ta mutsu mutsun Tunda Cikin nan ya fara nauyi zama ya ke min wahala.
Ina jin su suna waya da Tahir yace shima ya na kan hanya, sai bayan azahar muka isa Zariya tunda su Abba sun tsaya sun yi sallah Sadiq ya siyamin Tsire da Lemu ni ban ma ciba saboda zuciyata naji ta na tashi.
A samaru muka Dauki Tahir, na gaishesa ya amsa a dakile sai dai ya gaida Abba cikin Fara'a.
Ni na rika numa musu hanyar gidan Baba Tanko har muka iso.
Naga motarsa ma a waje yasa nace musu yana gida, sai Abba yace na shiga nace suna jiransa.
Ina shiga gidan da sallama da duka matansa naci karo suma sun yi mamakin ganina.
Muka gaisa kai tsaye nace"Baba na gida?
Sukace min eh yana gida sai nace a waje ana jiransa nazo tare da baki.
Amaryar ce ta shiga dakinsa ta gayamasa ina tsaye ko wurin zama ba su bani ba sai dai naga sai kallona suke yi kamar sun ga bakuwar Fuska.
Baba Tanko ya fito yana saka Hula Cikin mamakin ganina yace"Hasiya? Ko ba Hasiya bace?
Kai Tsaye nace'Ni ce Baba, ina yini?
Bai amsa ba illah ce min da ya yi"Lafiya? Wasu baki ne ke nemana?
Nima kai Tsayen nace"Mijina ne da mahaifinsa."
Ido ya waro kafin yace"Wai daman auran naki bai mutu ba?
Sai da kuma ya fad'a yaga cikin jikina sai ya yi gaba yana fad'in"To to bari naje na gani."
Na bisa da kallo ina jin wani abu na sukan raina, gajiya na yi da Tsayuwa har sai da na jingina.
Ganin haka ne yasa Amaryan baba ta bani kujeren tsugunno na zauna ina jin bayana sun kara kagewa.
Achan waje kuwa Baba Tanko na fita wazai gani? Sai yaga Alhaji Sulaiman Shinkafi Surukin Alhaji Jibril.
Ya bashi hannu suka ka gaisa lokaci d'aya yana fadin"Ah wa na ke gani kamar Alhaji Sulaiman?
Abba ya yi mirmishi kafin yace"Ni ne, kamar yan'uwan Alhaji Jibril na Zariya ko?
Baba Tanko jiki na rawa yace"Ba Shakka baka manta ba?
Ya fad'a ya na kallon su Sadiq wanda ke sanye da Shadda Deep Blue da Hula Tahir ma manyan kayane ajikinsu nan take ya gane su.
Cikin mamaki ya kalli Abba yana fadin"kada dai kace min wannan d'an ka ne?
Abba ya kalli Sadiq kafin ya yi mirmishi yace"Eh yaron wajena ne."
Baba Tanko sai ya kasa mgana, jiki na rawa ya Bude musu falonsa na waje suka shiga.
Bayan sun gaisa sai gashi ya Dawo cikin gida yana rawan baki a kawo Ruwa ya kalleni zaune ya na fadin"Ke ashe mijin naki surukin Baban ki Jibril ne? Gidansa ai Mubarak ya Dauko mata."
Ina jinsa bance masa komai ba matansa ne ke ta mamaki, suna ta neman jin mgana a bakina na yi musu gum.
Abba ne kadai ya sha ruwa ban da su Sadiq bayan an kara gaisawwa Abba ya kalli Baba Tanko Lokaci daya ya na nuna su Sadiq kafin yace"Ina fatan ka gane su ko?
Baba Tanko yace"Tabbas na gane su shekaru uku haka nan suka zo na Daura masa aure da Daya daga cikin ya'yan dan'uwana da ya rasu cikin Shedu masu yawa"
Abba ya jinjina kai kafin yace"Daman tabbacin hakane na ke so na samu, Saboda alokacin da ya yi auran bai sanar dani ba sai daga baya."
Baba Tanko ya rike baki kafin yace"Kaji ko? Daman sai da na tambayesa, domin nasan da sanin ku dai bazaku bari ya auri bakar tsiya ya kawo muku cikin zuru'a ba"
Abba ya yi mirmishi bai yi mgana ba sai kawai Baba Tanko ya gyara zama yana ba ma su Abba labarin irin bakin tsiyar Hasiya da maganar cewa ita ta yi sanadiyar mutuwar dan'uwansu bayan ya rasa komai.
Tahir ya kalli Sadiq alamun kadai ji ko?shi kuma sai ya yi kamar bai gani ba.
Abba ne ya dakatar da Baba Tanko da cewa za su tafi, 10k ya ijiye masa a gabansa sannan ya mike.
Har waje ya rakosu kamar ya yi musu Sujjada, Sadiq ne yace a kira ni mu tafi sai gashi ya shigo zakada zakadan yana fadin na taso suna jirana.
Na yi ma matansu sallama na fito sai gashi yau nice Baba tanko ke sakama albarka Harda Allah ya Saukeni lafiya.
Daganan har gida suka kaini, Sadiq kunyar tasa bai shiga ba sai da Abba yace ya taikamamin da jakata mana.
Sannan ya fito daga Motar
Ni kuma sai na Roke Abba ya shigo yaga dakina ko ruwa ya sha.
Abba bai yi gaddama ba ya Bude mota ya fito kuma yace Tahir yazo shima ya shiga.
Sai ga Abba da Tahir a falona jikina na rawa naje na kawo musu Ruwa, Abba ya sha shi da Sadiq Tahir kuma yace shi baya jin kishi.
Abba ya saka albarka ba jimawa yace bari su kama hanya tare da Tahir suka fita Assadiq kuma sai da ya Tsaya ya Rumgumeni ya sumbaceni.
Sannan yace na kula da kaina zamu yi waya.
Nice har waje na rakasu sai da naga Fitar motarsu layin sannan na dawo cikin gida Maman suhailat nagani Bakina na rawa nace mata Baban Assadiq ne da abokinsa suka kawoni gida.
Sai ta faramin fad'a ashe ba na garin ammh shine ban ce zan yi tafiya ba kamar ana zaman gaba.
Sai na fahimci laifina na kuma bata Hakuri.
Ranar na kwana cikin Farimciki ko bakomai abubuwa suna Faruwa A yadda ban yi Tunani ko tsammani ba.