Sashe 43
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Washegari likita ya sallameni bayan ya bani dokoki saboda mikin dake jikina, kenan kwana shida na yi a asibitin gidan Adda Fati kuma aka wuce dani Direct dakin da Habiba ke kwana aka saukeni ni da yarana a ramar kuma Inna talatu ta saka Ruwan masu zafi ta yi ma yaran nan wanka suka yi ta tsala ihu nima kuma ta iza keyata zuwa bayi ta gasamin jiki na sosai ina wash wash ta na fadin kwana nawa na yi a asibiti da d'anyen jiki ba gashi ballatana wanka sai dai gogemin jiki kawai suke yi acan.
Bani da zannuwa Atamfa Adda Fati ta siyamin guda d'aya ta farkamin zannuwa uku ina sakawa, su kuma jarirai Adda Fati ta shiga kasuwa ta kara siyo musu wasu, kuma daman dayan akwatina duka kayan haihuwan da Anty Surayya ta siya ne aciki, Anty surayya washegarin ranar da aka sallamomi ta dawo ita da Anty Sa'ima ta zo min da Ferfesun kayan ciki mai yawa tare da Kayan jarirai sannan kuma ta ce ta zab'o ma ya'yanta sunayen yan gayu, Asif da Asim tace zamu rika kiransu Saboda Sakayawa.
Da ita ma mun yi mganar taron suna tace Sadiq yace sai sati ya zagayo za'a yi taron suna, bayan kuma ita cikin yan'uwan Assadiq ba wacce ta kirani sai Anty Saddiqa daga kebbi sai kuma Saliha da ita ba sau daya ta kirani ba sai Anty Sa'ima ta kirani Lokacin muna asibiti ina jin Anty Surayya ke ba su Lambar Adda ta nan suke mgana da ni.
Sun tafi da cewar sai ranar taron suna za su dawo in sha Allahu.
Sun tafi kenan ba jimawa sai ga Salima ta zo ita da Zahra'u da Fathihatu sai ya'yan gidan Baba Tanko su suka rakaso gidan Adda Fatin tunda ba su san gidan ba..ni na ke gayama salima zuwan su Anty Surayya nace mata yanzu suka tafi sai ta kirasu a waya sukace ai sun kama hanya sai ranar suna za su dawo.
Salima sai ta koma gefe da Zahra'u ne da Fathihatu muka yi ta hira suna ta santin yara sai dai abunda na Lura itama Salimar kamar cikin gareta.
Kuma da alamu tana son yara domin haka ta Daukesu ta na ta kallonsu ta na mirmishi.
Kuma ta yi ta daukansu Hoto, Da ta tambaayi sunayensu Habiba ta gayamata, sai tace ga sunan da Anty Surayya tace a rika kiransu ta yi mirmishi tace sunan ya yi.
Sun jima tunda Sai bayan la'asar suka tafi sukace mim sai ranar suna bayan sun gayamin sakon Hajiya Murjanatu tace tana yi min barka kafin tazo.
Zuwa Lokacin nasan haihuwata ta zaga gabadaya dangi, kuma da karin yan Biyun da na haifa yasa gidan Adda Baya Rabo da Jama'a.
Maman suhailat ma bata sani ba bata nan ashe tun washegarin Ranar da su Assadiq suka je ta yi tafiya, sai da ta dawo sannan tazo Dubani ni da twins ta na bani Labarin zuwan su Assadiq.
Ni kuma nace mata ai a ranar aka yi min aiki tunda a asibiti ma suka same mu ka yi ta yi jimami.
Mutanen gidanmu na samaru su mamanboy, sun ta zuwa asibiti Dubani kuma da muka dawo gida ma sun zo sau Biyu, Ramatu kuwa kusan nan ta ke yini sai da yamma ta ke komawa gida Nura baya nan na Haihu ammh ya yi min barka ta waya.
*******
Ana gobe sunan Twins muka yi waya da Assadiq yace yaso ya shigo ammh bazai samu zuwa ba sai bayan suna.
Muna cikin magana sai yace zai kirani in ya gama mgana da Abba.
Ni kuma daman yace kada mu yi shirin komai kudi zai Turomin na shagalin suna da komai da komai.
Abunda ban sani ba Surayya ta same shi sun yi mgana da tagaji da sha mata kamshin da ya ke yi.
Ammh sai da ya nuna mata bacin ran meyasa bata gayamai ga abunda ke Faruwa tun farko ba?
Anty Suraya ta bada uzurin Saboda Halin da ya ke ciki yasa ta boye mganar ammh ba da wata manufa ba ne.
Da haka ya sauko suka yi mgana ya ce ta kara siyamin wasu kayan fitar suna ni da Twins a dinka sannan mganar abunda za'a yi na shagalin suna ita ta bada shawaran a tura mana kudi sai mu yi komai da kanmu Tunda Hakkin mu ne, raguna ne tace ba laifin in ya siya sai su tafi dashi a ranar suna da Safe in kuma yana ganin akwai walaha ko mijin Adda Fati zai iya wakiltawa ya Tura masa kudin a siya Ragunan ya yanka da Safiyar ranar suna.
Sadiq yace zai yi mgana da Abba, Har mganar Umma sai da suka yi yace Umma ko barka bata yi masa ba, shi kuma bai yi mata mgana ko a fuska bai nuna mata wani abu ba ya samu dai ta sauko ta na amsa gaisuwarsa.
Har mallam zakari sai da ya kirasa ya yi masa barka.
Surayya tace ya kyale Umma zata sauko a hankali ammh mganar su Sadiya fa? Ya kamata ya karbo wayar Hasiya da key din dakinta dake wajensu."
Shuru ya yi kafin yace"Kyale su dani, so na ke yi naga iya gudun ruwan su."
Da haka suka rabu a ranar kuma da ya yi mganar da Abba shima ya Goyi bayan haka Shiyasa da rana ya kirani yace na Tura masa lambar mijin Adda Fati da shi suka yi mgana.
Raguna uku yace a siya sannan ya Turo mana isheshen kudin Hidiman suna yace muyi amfani da shi.
Adda Fati da ta gayamin uban kudin da ya Turo sai da na yi hawaye na kirashi ina yi masa godiya.
Sai kawai yace komai zai yi min bai biyamin kwatakwancin karamcin da na yi masa a rayuwa ba.
A ranar da yammah sai ga Goggo Husai tare da babbar yar Goggo Hassu ita baza ta samu zuwa ba sai Matar Baba Sammani uwargida sun taho daga Shinkafi Domin hallatar taron suna.
Assadiq yaji dad'i sosai shi daman bai ce kowa yaje suna ba wanda yaga dama ne yaje, Innani daman tace in taje suna ba mai kara yi mata wayau ya dawo da ita magajin gida shi da kanshi yace a barta acan sannan itama Siyan zai gayamata Innani zata Tsaya ta kwana Biyu in ba haka ba sai ta kara tada wani Fitinan kuma.
Bani da zannuwa Atamfa Adda Fati ta siyamin guda d'aya ta farkamin zannuwa uku ina sakawa, su kuma jarirai Adda Fati ta shiga kasuwa ta kara siyo musu wasu, kuma daman dayan akwatina duka kayan haihuwan da Anty Surayya ta siya ne aciki, Anty surayya washegarin ranar da aka sallamomi ta dawo ita da Anty Sa'ima ta zo min da Ferfesun kayan ciki mai yawa tare da Kayan jarirai sannan kuma ta ce ta zab'o ma ya'yanta sunayen yan gayu, Asif da Asim tace zamu rika kiransu Saboda Sakayawa.
Da ita ma mun yi mganar taron suna tace Sadiq yace sai sati ya zagayo za'a yi taron suna, bayan kuma ita cikin yan'uwan Assadiq ba wacce ta kirani sai Anty Saddiqa daga kebbi sai kuma Saliha da ita ba sau daya ta kirani ba sai Anty Sa'ima ta kirani Lokacin muna asibiti ina jin Anty Surayya ke ba su Lambar Adda ta nan suke mgana da ni.
Sun tafi da cewar sai ranar taron suna za su dawo in sha Allahu.
Sun tafi kenan ba jimawa sai ga Salima ta zo ita da Zahra'u da Fathihatu sai ya'yan gidan Baba Tanko su suka rakaso gidan Adda Fatin tunda ba su san gidan ba..ni na ke gayama salima zuwan su Anty Surayya nace mata yanzu suka tafi sai ta kirasu a waya sukace ai sun kama hanya sai ranar suna za su dawo.
Salima sai ta koma gefe da Zahra'u ne da Fathihatu muka yi ta hira suna ta santin yara sai dai abunda na Lura itama Salimar kamar cikin gareta.
Kuma da alamu tana son yara domin haka ta Daukesu ta na ta kallonsu ta na mirmishi.
Kuma ta yi ta daukansu Hoto, Da ta tambaayi sunayensu Habiba ta gayamata, sai tace ga sunan da Anty Surayya tace a rika kiransu ta yi mirmishi tace sunan ya yi.
Sun jima tunda Sai bayan la'asar suka tafi sukace mim sai ranar suna bayan sun gayamin sakon Hajiya Murjanatu tace tana yi min barka kafin tazo.
Zuwa Lokacin nasan haihuwata ta zaga gabadaya dangi, kuma da karin yan Biyun da na haifa yasa gidan Adda Baya Rabo da Jama'a.
Maman suhailat ma bata sani ba bata nan ashe tun washegarin Ranar da su Assadiq suka je ta yi tafiya, sai da ta dawo sannan tazo Dubani ni da twins ta na bani Labarin zuwan su Assadiq.
Ni kuma nace mata ai a ranar aka yi min aiki tunda a asibiti ma suka same mu ka yi ta yi jimami.
Mutanen gidanmu na samaru su mamanboy, sun ta zuwa asibiti Dubani kuma da muka dawo gida ma sun zo sau Biyu, Ramatu kuwa kusan nan ta ke yini sai da yamma ta ke komawa gida Nura baya nan na Haihu ammh ya yi min barka ta waya.
*******
Ana gobe sunan Twins muka yi waya da Assadiq yace yaso ya shigo ammh bazai samu zuwa ba sai bayan suna.
Muna cikin magana sai yace zai kirani in ya gama mgana da Abba.
Ni kuma daman yace kada mu yi shirin komai kudi zai Turomin na shagalin suna da komai da komai.
Abunda ban sani ba Surayya ta same shi sun yi mgana da tagaji da sha mata kamshin da ya ke yi.
Ammh sai da ya nuna mata bacin ran meyasa bata gayamai ga abunda ke Faruwa tun farko ba?
Anty Suraya ta bada uzurin Saboda Halin da ya ke ciki yasa ta boye mganar ammh ba da wata manufa ba ne.
Da haka ya sauko suka yi mgana ya ce ta kara siyamin wasu kayan fitar suna ni da Twins a dinka sannan mganar abunda za'a yi na shagalin suna ita ta bada shawaran a tura mana kudi sai mu yi komai da kanmu Tunda Hakkin mu ne, raguna ne tace ba laifin in ya siya sai su tafi dashi a ranar suna da Safe in kuma yana ganin akwai walaha ko mijin Adda Fati zai iya wakiltawa ya Tura masa kudin a siya Ragunan ya yanka da Safiyar ranar suna.
Sadiq yace zai yi mgana da Abba, Har mganar Umma sai da suka yi yace Umma ko barka bata yi masa ba, shi kuma bai yi mata mgana ko a fuska bai nuna mata wani abu ba ya samu dai ta sauko ta na amsa gaisuwarsa.
Har mallam zakari sai da ya kirasa ya yi masa barka.
Surayya tace ya kyale Umma zata sauko a hankali ammh mganar su Sadiya fa? Ya kamata ya karbo wayar Hasiya da key din dakinta dake wajensu."
Shuru ya yi kafin yace"Kyale su dani, so na ke yi naga iya gudun ruwan su."
Da haka suka rabu a ranar kuma da ya yi mganar da Abba shima ya Goyi bayan haka Shiyasa da rana ya kirani yace na Tura masa lambar mijin Adda Fati da shi suka yi mgana.
Raguna uku yace a siya sannan ya Turo mana isheshen kudin Hidiman suna yace muyi amfani da shi.
Adda Fati da ta gayamin uban kudin da ya Turo sai da na yi hawaye na kirashi ina yi masa godiya.
Sai kawai yace komai zai yi min bai biyamin kwatakwancin karamcin da na yi masa a rayuwa ba.
A ranar da yammah sai ga Goggo Husai tare da babbar yar Goggo Hassu ita baza ta samu zuwa ba sai Matar Baba Sammani uwargida sun taho daga Shinkafi Domin hallatar taron suna.
Assadiq yaji dad'i sosai shi daman bai ce kowa yaje suna ba wanda yaga dama ne yaje, Innani daman tace in taje suna ba mai kara yi mata wayau ya dawo da ita magajin gida shi da kanshi yace a barta acan sannan itama Siyan zai gayamata Innani zata Tsaya ta kwana Biyu in ba haka ba sai ta kara tada wani Fitinan kuma.