← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 83

Sashe 64

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Nayi masa maganar kayan daki yace na barsu anan acan Abuja komai na kayan more rayuwa an saka bani da matsalan komai, kl daki kuma zai kara Biyan haya na shekara, in na zo garin zan samu wajen sauka.
Shi da ya ke yanzu ba shi da wani abu da garin Zariya ni ce daman kuma yanzu zan koma kusa da shi.
Sai Masters kuma tuni ya gama project ne ma yaso ya bashi matsala ammh daga baya ya shawo kan matsalan.
Saboda Hakkin Zaman tare Maman suhailat da Ummi na fara gayama zan koma Abuja, suka yi min Fatan alheri.
Maman suhailat kuma tace zatayi kewar mu ni da Asim.
Adda Fati kuma da kaina naje na gayamata ranar da naje na kaimata Tsabaranta ita da Habiba.
Ta tayani murna kwarai da gaske Adda Rukayya kuma sai a waya na gayamata.
Ta kwashi gud'a kafin tace"Allahu Akbar yau ga Hasiyan Amma a garin Habuja."
Ina ta Dariya, haka ma Ramatu ta yi da tazo min sannu da zuwa na gayamata suna ta cewa mahakurci mawadaci.
Ina shirina a sannu sannu sannan naje gidan su Safiya itama na kai mata Kayan kwalliya na gaida mamansu, daganan kuma ta rakani makaranta na fara Sreenning.
Kuma Alhamdulillah kwana hudu na yi muna zuwa ma gama gabadaya sai Jiran sakamako..
Itama tamin murna jin zan bi mijina zuwa Abuja, sannan ta yi jajen zan tafi na barta.
Ni kuma nace Allah ya bata miji ma'aikaci a garin Abuja sai tazo can mu had'e tace Ameen.
Assadiq ya Turamin kudi saboda siyan wasu abubuwan sannan yace Adda Fati ko Adda Rukayya cikin su wata ta shirya muje su ga inda muke ko Saboda gaba.
Amma na fara gayamawa, Tunda ita na fara gayama zencen komawata Abuja, ita tace na gaya musu cikin su wacce ke da Sarari sai ta rakani ammh tace a madadinta Inna Talatu ta bi ni itama ta saka albarka.
Haka ko akayi, Adda Fati taso taje ammh Adda Rukayya na ji tace ita zataje sai ta bar mata.
Inna talatu kuma da kaina naje na gayamata tace ta na ta fama da kafa sai dai daga baya zata zo taga inda na koma sai kawai nace Ramatu da Habiba su shirya mu tafi tare.
Mijin Adda Rukayya da tace masa zata rakani Abuja mamaki ya rika yi.
Har yana kara tambayan kuma muna zaune lafiya da mijina ba abunda ya same sa?
Adda Rukayya tace ba gashi har zan koma Abuja inda ya ke aiki ba, kuma ita da kanta da tazo gidana ta ke fad'amin.
Ni sai ya ma ba ni dariya, ni kaina nasan mutane da dama suna can suna shan mamakin jina shuru a gidan aurena a karon da aka Fidda min rai a kan zaman aure.
Adda Fati na ba ma kudi ta siyamin su kuka kubewa, Daddawa, Kuli yaji kayam kamshi sannan na saka aka dakamin garin kunin Alkalama na ke dama su Asim da ni kaina.
Sannan har Fulawa sai da na siya, saboda Dankwake da kayan miya Bushasshe da Tumatur na dai siya duk abunda nasan zan iya nemansa acan.

Kuma daman yace kayan wasan mu kadai zan dauka, ni da Zariya ba yanzu ba in ma munzo sai dai katsina Bikin Tahir sai in kuma wani abu ya faru mara dad'i wanda ba'a fata.
Kayan gyaran jiki kuma na siya wajen Surayya ta aikomin da shi har da Dahuwar kazar Uwayen gida tare da Tsumi da maganin sanyi.
Ni bana wasa da shan maganin Sanyi,ta dalilina na had'a ta da mutane sosai ciki harda yayyen mijina.
Adda Rukayya ma na yi mata Ciniki kuma itama Saboda ingancin mganinta yasa ta kawo mata Mutane sosai.
Sati biyu na yi Assadiq yazo Ranar jumma'a ya kwana Asabar muka dauki hanyar Abuja
Duk wani abun da zai lalace Adda Fati na ba mawa da sauram kayan abincin mu.
Maman suhailat harda hawayenta ammh tace tana shiga Abuja zata nemeni.
Ni dai nace su yafemini in na yi musu ba daidai ba  Ummi tace Babu abunda na yi musu Allah ya yafe mana gabadaya.

Nima nace na yafe musu duniya da lahira, har makota ma da muke huldar arziki. Sannan har makarantar da nayi Tp sun so su rikeni na musu koyarwa su rika Biyana lokacin ma zamu tafi gusau to bayan na dawo ma sai da suka kirani nace musu zan koma Abuja da zama ne.
Da wuri muka fita shiyasa muka isa da wuri, ni ce a gaba tare da Asim sai Adda Rukayya da Habiba da Ramatu a baya tare da ya'yansu da Asif.
Gidajen suna nan a kusa da ma'aikansu a 24 Aminu Crescent Abuja.
Kuma 3bedroom ne da Falo guda biyu sai kitchen sai Tiolet a kowani dakuna sai Kuma haraban wajen ijiye mota.
Kowani gida da nashi Aparment din daidai kowa bazai shiga Hurumin kowa ba.
Kuma duka duka Gidaje Goma ne a waje d'aya a jere  acan kuma gefen shima goma can gaba Wajen dai gidaje talatin ne.
Muna sauka shi ya fita ya barmu muna gyare gyare Adda Rukayya da Ramatu nata santin gidan komai Sabo.
A albashin mutum za'a cire  har kud'in Furnitures.
Sai yamma ya dawo ya kawo mana abincin da ya yi mana Takaway.
Lokacin mun gama gyara gidan Tunda har mopper mun zo da shi na Zab'i dakina da na Assadiq.
Shima na kawo masa wasu kayansa , kuma yace zai kwaso sauran kayansa a inda ya ke zaune.
Kwana daya su Adda Suka yi min suka koma Zariya Habiba kuma Saboda makaranta, Da zai fita Office ya Daukesu zuwa Tasha ya saka su a motar Zariya bayan ya ba su Cikakken kudin mota.
Ni kuma ranar ni kadai na yini dagani sai yara kamar mayya, ban fara girki ba tunda ba kayan abinci da rana da ya fita lunch ya je ya yi min Takeway ya kawomin.
Da daddare ma haka, washegari kuma sai da ya dawo aiki muka fita kasuwa muka yi siyayyan kayan abinci sannan bayan mun dawo gida ya koma yaje ya kwaso kayansa a inda ya ke zaune.
Tare dashi muka jera komai a muhallinsa,
Shi wannan gidan akwai kayan kallo har da Firiza da A.c komai lafiya lau.
Ana ta kirana ana yi min Fatan alheri.
Umma da Mama duk sun kirani, Kaf yayayen Assadiq sun kirani illah ban da Salima da Sadiya da Sajida.
Bansani ba ko shi sun kirashi, ni dai ban matsa kaina ba, ballatan nace masa basu kirani ba.
Muka fara shimfid'a kyakyawan Sabuwar Rayuwa tare da Assadiq da ya'yana.
Mu kad'ai muka fara tarewa a Estate din nan , kullum in Assadiq ya fita ya barni dagani sai ya'yana muyi ta burumtu a cikin gidan.
Ba bu abunda na nema na rasa sannan ga wayata ina waya da yan'uwana tare da yan'uwan mijina.
Ni kaina in na juya naga yadda Allah ya maida Rayuwata sai na daga hannuwa sama na yi ma Allah kirari da Hamdala
Sannan nace"Alhamdulillah."

*Janafty*
*TMWB3K017*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk

Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haɗin mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan.

Sultana dai ta gama makircinta da kokenta kokenta na kada Assadiq ya tafi dani Abuja hak'anta  bai cin ma Ruwa ba.
Na dauka daga wannan Lokacin ta Saduda ashe ba haka ba ne, ta fito da wani Sabon Tsirfa ko nace tsohon ya yi da ba wanda bai san irin wannan abun na masu kishi ba.
Addabarmu ta fara yi sai muna cikin barci ance dare mahutane ga bawa ammh ita a wajenta bamu isa mu huta ba.
Karfe biyu na dare uku haka zata rika Kiran Assadiq kullum kuma mganarta daya ne, abunda ke cikinta sun hanata sukuni sun hanata barci.
Ko tace ta kasa tafiya maranta na Ciwo, karya dai da makirci iri iri sai kuma ta kira ta na kuka.
Kuma abunda ya bani mamaki tana wajen Umma ne ammh ba ta rabo da korafin wani abu na Damunta.
Chapter 64 · 0% Book details