← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 83

Sashe 6

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bani da zabi illah Aminta da Assadiq domin nan duniya bani da wanda ya fisa cikin gyad'a kai nace"Na Aminta da kai Assadiq, na kuma Fahimceka na kuma yarda cewa baka na gudun had'a zuru'a dani saboda Canfi da ke kaina ba ne"
Da Sauri yace"Astagafurullah.! Kada ma ki kara wannan Tunanin, ni ban yarda da Canfi ba , sannan ina da ilimin addini nasan Allah ke yi ba Mutum ba."
Sai na yi masa mirmishi ina jin zuciyata na samun natsuwa kafin na koma saman kirjinsa na kwanta ina Fadin"Assadiq ya kamata ka yi saurin sanar da iyayenka mganata kafin na haihu ko?
Ya na shafa kaina zuwa bayana yace"In sha Allahu, zan sanar da su kada ki damu."
Sai na jinjina masa kai shuru muka yi kafin ya muskuta ya na fadin"Daman Alhaji Jibril baffan ku ne Siya?
Sai na Dago ina kallonsa kafin nace"Na kaduna?
Sai ya gyadamin kai, cikin mele baki nace"Eh kanin babanmu ne, ammh da ya ke sanadina yasa tunda babanmu ya rasu ba su duba bayansa ba, a cewarsu duk wanda ya rabemu shima zai iya rasa komai na shi."
Shuru ya yi kafin yace"Mutane yanzu sun saki Allah sun kama boka da mallam, da kuma Canfe canfan banza da wofi, mutane ba ikilasi ba Tauhidi, sun manta da Allah shi ne Allah, komai baya faruwa sai da cewarsa da kuma Umarninsa."
Ina jikinsa har a Lokacin idanuwana suka kawo kwallah kafin nace"Farkon Rayuwata na taso cikin Farinciki, Daga baya ta juye zuwa kunci da bakinciki na shiga Tsaka mai wuyar da kai ne ka fitar da ni acikinsa Assadiq don Allah ko da iyayenka ba su karbeni daga Farko ba, kada ka Juyamana Baya ni da cikin da ke jikina."
Sai kawai na fashe masa da kuka ina Rokon kada ya zabi sultana ya rabu dani kai tsaye yace"Kamar yadda Saboda ke ban barta ba, ke ma kuma saboda ita bazan barki ba Siya".
Sai na kara kamkamesa ina ta kuka, shi kuma ya na aikin lallashina.
Daganan kuma daga lallashi sai kuma ya fara kokarin nuna min yadda ya yi kewata.

A nan saman kujera mun kasa ko shiga ciki komai ya wakana, ni kaina nasan na yi kewar mijina, shima haka ballatana ga cikin jiki, Sai dai muna Samun natsuwa na mike da gudu sai Tiolet naje zubar da miyau shi na bari da tattara mana kayanmu, ni daga nan tubewa na yi na tsabtace jikina.
Ko da na fito ya shigomin da akwatuna ciki tare kayanmu da muka yi falati da su, shima wanka ya shiga ya Tsabtace jikinsa.
Dagani har shi ba ma jin yunwa, nad'ewa muka yi a gado muna sake Sabon Hira ya kashe wayarsa gabadaya Saboda yace yanzu lokacina ne.
Muna kwance a kan filo daya fuskokin mu na kallon Rufin Dakin, hannayemmu sarke a waje d'aya, Juyawa na yi na rab'i da rabin jikinsa na kira sunansa"Assadiq?
Da sauri yace"Uhm SiyaAssadiq."
Ina shafa gemunsa nace"Ya ku ka kare kai da abokin ka din nan? Domin nasan yasan har yanzu muna tare.?

Assadiq ya yi shuru saboda baya so Hasiya tasan a kanta sukayi fad'an da ba su taba yi da Tahir.
Sun rabu zukata ba bu dadi kuma Daga Lokacin ba su kara neman juna a waya ba.
Ba kuma wani abu ya had'a su ba, sai Tahir da ya ke jifan Hasiya da kalmar Annoba sannan ya na rainata Saboda ita bazawara ce, kuma ya na kokarin nuna masa ya saka Rayuwar Ahalinsa a bala'i tunda ya kasa rabuwa da Hasiya.
Yasan ya yi kuskure da ya yi masa karya ammh Hasiya matarsa ce kuma Sirrinsa bazai taba bari wani ya ci zarafinta ba Shiyasa ya yi ma Tahir Tsawa akan kada ya kara aibata matarsa in kuma ya kara sai ransa ya baci, shikenan Tahir yace yaje tunda ya zabi hasiya sama da shi, ya bar shi duk sanda ya gane kuskurensa ko ta kwabemasa yasan zai nemesa.
Shima a lokacin ransa ya baci shiyasa har yanzu bai ko nemesa ko ta waya ba.
Sai da yaji muryata ina kara fad'in"Uhm ka yi shuru?
Da Sauri yace'Na fad'a masa gaskiyan cewa muna tare yanzu."
Kai Tsaye nace"To me ya ce maka?
Ajiyar rai ya sauke kafin yace"Me kuwa? Abokina ne fa ba Ubana ba Hasiya, ba shi da ikon zab'a min Ra'ayina"
Sai na yi shuru na kasa mgana,Ammh na Fahimci shi da abokin nasa ba su yi Rabuwar dad'i ba.
Gudun kara Tabarb'arewan al'amarin yasa na yi shuru da bakina.
Sai dai na kara lafewa a jikinsa ina fad'in"To ka na Tunanin a yanzu bazai gayama kowa ba?
Sadiq yace"Da zai fad'a da Tuntuni ysa fad'a, nasan Tahir bazai taba fad'an komai a kan ki ba, sai dai in dan ni ne na Bukaci hakan."
Ajiyar rai na sauke kafin nace"Allah yasa komai ya zo da Sauki Assadiq."
Cikin jinjina kai yace"In sha Allahu Khairan Siya ta."
Daga haka ya Rumgumeni yace mu yi barci ya gaji, kamar wasa sai ga shi barci ya kwashemu dagani har shi, sai dai ni miyau ne ya rika tadani da na mike daman ya san miyau ne ya cika bakina.
Muryansa cikin barci yace"Miyan nan ba shi da magani ne Siya?
Ina kara kwanciya ajikinsa nace"Likita yace for now dai babu, ammh yace zuwa gaba zai rage."
Kara rikeni ya yi cikin barci barci yace"Ya na takura min mata ne Shiyasa."

Sai bayan azahar muka tashi muka yi sallar, shi ya fita ya siyo mana abinci da kayan marmari, ni kayan fruit din kadai na sha  suma ba'a wanye lafiya ba na yi ta amai, ya hadamin Tea shima na sha na yi amai, Tuwo nace ina so yaje ya siyomin Tuwon Semo miyar karkashi shi naci ya zauna a cikina.
Duk wasu kayan kwalama sun daina Burgeni, Da daddare kuma Tuwon shinkafa ya siyomin miyar kubewa da ganda, sanda naci lafiyata kalau ammh kwana na yi ina ta faman Amai da miyan yanzu ya yi yawa, shi Assadiq yadda na ke ta bushewa ne damuwarsa da kuma Aman da na ke yi yasa da Safe ya tasani gaba muka koma asibiti ganin Likita.
Bai yarda ba sai da likita ya karanta masa sai hakuri in cikin ya fara girma duk zan daina Aman sannan miyan zai Ragu, Ramar da na ke yi kuma kila Sanadin cikin ne, ammh zuwa gaba in na fara cin abinci sosai zan maida jikina.
Bai bamu komai ba, sai magungunan karin jini na masu ciki ya sake Rubamin, Yace maleria ya rabu dani zazzabin dare da na ke yi cikin ne ya na Tunanin in ya yi kwari duk zan dawo Normal.
Haka muka koma gida, ina kwance jiya da yazo da karfin jikina ammh washegari sai na kwanta kamar ruwa, kuma gashi gobe da Safe zai koma wajen aiki, maganarsa shine bazai barni ni kadai ba, gwara na koma gidan Adda Fati na zauna ko kuma Habiba tazo ta zauna dani.
Ni kaina ina son na Huta sai nace zan je gidan Adda Fati na yi ko sati ne daga baya in zan dawo sai na Dawo da Habiba.
Ga makaranta ma, da ya ke ya kunna min wayata, Safiya ta kira mun yi mgana tace an fara Test ya kamata na zo makaranta, shi kuma yace komai sai da lafiya na bari ko an wuceni na yi Difaring ni ko ina zan bari Yan ajinmu su yi gaba su barni.
Da kansa ya had'amin komai da zan bukata washegari da Safe sai da ya kaini gidan Adda Fati ya kuma barmin isassun kudi sannan ya hau Motar haya Zuwa Abuja.
Ita kanta Adda Fati  taji dadin haka Tun ballatana irin ramar da ta ga na yi, sannan taga laulayin nawa mai zafi ne.
Tunda Assadiq ya tafi a rana ban san adadin sau nawa ya ke kirana yaji lafiyata ni da Baby ba, kullum cikin cewa ya ke da naji wani abu na koma asibiti, ni kenan kullum tuwo da tsaki, Komai baya min dadi, kuma ban daina amai ba ga miyau, maganar gaskiya ina Laulayi mai zafi sosai.
Sati daya na yi gidan Adda Fati ta had'ani da Habiba muka dawo daganan Wajena ta ke zuwa makaranta.

Bayan tafiyar Assadiq sai da na yi sati Biyu sannan na fara farfadowa, na rage Amai sannan na daina zazzabin dare, kuma yanzu zan ci abinci ya tsayamin acikina na wani lokaci a satin ya baro Abuja bisa adalci ya sauka a gusai, ya gayamin ban nuna wani abu ba, Tunda itama matarsa ce kamar yadda na ke da Hakki a kansa itama ta na da Hakki a kansa.
Bai zo zariya ba sai da ya koma Abuja sai weekend Ranar jumma'a ya zo ya ganni, ranar da yazo Habiba ta koma gidan Adda shi kuma ya cigaba da kula dani.
Duk da dai naji sauki sosai, ni kuma na matsa masa ranar litini da ya tafi da Safe ni kuma na Shirya na koma makaranta naje na iske Uban Assigemt sannan an yi abubuwa da dama ba na nan, Sai dai Thanks to Safiya duk ta min wasu abubuwan sannan komawata ta na kokarin koyamin abunda ya wuceni.
Kullum da minti da cingam na ke yawo a jakata ko da kunzo Saboda Miyan bakina, ina shiga cikin jama'a akwai cutarwa saboda wani ya na da kyankyami.
Ramewa kawai na ke yi, sai dai na fara cikar Fuska dagani In ji Adda zan yi girman ciki mai kumburi Domin tun cikina na wata uku da wani abu ya bayyana ajikina, ga shi dai ina da Tsawo ammh Tsawo na bai shanye girman cikina ba, in na saka Hijabi in ban saka hannu na kare ba sai ya bayyana.
Chapter 6 · 0% Book details