Sashe 47
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Umma ta gyara zama ta yi musu nasiha sosai, ita Sultana aka ce ta yi ma mijinta Biyayya. Sannan kada taji ya kawo kararta ta yi masa wani abu.
Shi kuma akace ya yi adalci sannan ya san cewa Sultana Amanqce a wajensa in yaci Amanarta Allah na kallonsa.
Cikin Tattausan lafazi ya kalli Umma kafin yace"Umma ni dai kinsan bani da matsala, diyarki ce ta ke da matsala ki gayamata rashin kunyar da ta koya daga baya bazan dauka ba, in tace bazata bari ba zamu yi ta samun matsala ne Umma."
Da Sauri Umma tace"Kin ji ko? Ke sultana bashi hakuri."
Ta fad'a ta na Hararan Sultana wacce ta sunkuyar da kanta Cikin yaukin baki tace"Kayi hakuri."
Jinjina kai ya yi kafin yace"Na yi hakuri, sai mgana ta gaba Bazan lamunci ta rika aibatamin matata ba, in ita bata san darajan ta ba, ni na sani kuma ni zan zauna da su bisa Amana ne, kamar yadda bazan lamunci ita Siya ta aibatata ba, haka itama bazan taba bari ta aibatata ba."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Hakane, Sultana ki gyara don Allah? Ku zauna lafiya da junan ku tare da hakuri da juna."
Kafin ta tafi sai da ta tabbatar da ta daidaita abunda ita ta yi silar lalacewarsa da kanta.
Sadiq ya rakata har bakin Titi ta hau mashi zuwa gida Abba yaso ya Dauko mota Shi kuma yace sai yaje yaga likita ko zai fara amfani da Mota da kafarsa.
Silar Umma yasa Sadiq ya Sauko ammh sai da Sultana ta kara sauke kai ta bashi Hakuri sannan ya hakura.
Shi namiji ne da mace ta zame masa ginshiki kuma ya dad'e baya tare da mace shiyasa bai gwasale kokarin Sultana ba, bayan kuma tana da hakki a kansa da shima ya sauke shi a wannan Daran.
Ita kuma abunda ke ranta itama ta yi tayi, ta samu ciki ta Haihu domin ta fi Hasiya samun matsayi a wajen Yaya Sadiq.
Da kuma kissanta yasa har washegari bai fita ko'ina ba yana tare da Sultana sannan har yinin ranar bai kira Siya ba sai da ya fita sallar mangariba ya samu ya kirata suka yi mgana tace suna gida sun dawo tun da Rana ita da Inna talatu.
Washegari kuma Big sis ta kirasa tace Umma ta kirata tun a jiya tace ta shirya zata rakata Zariya wajen Hasiya ta yi mata barka.
Har acikin ransa yaji dadi da yaso yaje ammh ganin zai koma ganin likita yasa yace bari ya had'a gabadaya.
Umma da Surayya suka tafi Zariya direban Abba kuma ya tukasu.
Daman kuma Surayya sun yi mgana da Hasiya tace mata ta koma dakinta nan suka wuce kai Tsaye.
********
Tun kafin Anty Surayya ta kirani ta gayamin Umma na tafe Assadiq ya gayamin shiyasa na gayama Inna Talatu, Habiba tare da ita muka taho ita ta tashi ta dora girki.
Wajajen azahar suka iso na yi wanka na Lokacin su Asim ma sun sha gayunsu suna tashin kamshi.
Sai a ranar na taba gaida Umma ta amsa min cikin sakewa kad'an duk da bata washe min baki ba.
Anty Surayya ta kwashi yaran ta zube mata a jikinta.
Sai ga Umma ta kura musu ido ta na kallonsu, duk yadda ta so kada yaran su yi tasiri a ranta sai da suka yi.
Farat d'aya taji sun bala'in Burgeta sun shiga cikin ranta da wani kauna.
Tana kallonsu idanuwanta suka kawo kwallah ta kalli Surayya lokaci d'aya ta na fadin"Surayya yaran nan kamar magajin gida Lokacin yana karami."
Surayya na dariya tace"Wlh nima haka nace Umma, sak Sadiq yana kamar su."
Umma ta rumgumesu a jikinta tana saka musu albarka.
Surayya ce ta waiga bata ga Innani ba shine ta yi mgana.
Ina mirmishi nace"Tana dakin maman Suhailat makociyata."
Inna talatu tace"Ta samu hira, maman suhailat akwai labarai a bakinta."
Surayya tace"An had'u da an dace kenan"
Muka yi dariya gabadayan mu, Habiba na aika ta kira Innanin sai gata da Sandarta da Uban gilashinta, jin muryansu Umma yasa ta washe baki ta na fadin"Salamatu kin huce kenan kin zo ganin jikokin naki? To wa ke fushi da yara? Balle yan Biyu kyautar Allah? Gwara da kika maida komai ba komai ba kin ji rayuwar nan ma nawa ta ke, yarinyar nan Hasiya da danginta duk mutanen kwarai ne, zaune na ke lafiya kamar ina cikin gidan sulaimanu."
Umma dai sai ta sauya mganar ta hanyar gaida Innani.
Surayya ma ta gaisheta ta amsa tana zama kan Kujera Lokaci daya tace"ina magajin gida?
Umma tayi saurin cewa"Yana can kinsan sultana ta koma gidanta."
Ta fad'a ta na satan kallona ni kuma ko a fuskata bata Fahimci wani abu ba.
Duk da naji wani iri, ganin har yau da Safe mun yi mgana ammh bai Fadamin ba, wata zuciyar tace ina Ruwan ki Hasiya?
Innani ta tabe baki kafin tace"Au ta gama koken koken iskancin nata ta koma kenan? Yarinyar haushi ta bani ni fa na ke mata mgana ta min banza yo, ni fa uwarta na haifa ba ita ba kuma Tunda taga ni nan na Saduda na bi Allah itama sai ta Saduda ta bi Allah da monzonsa, ohon mata dai ita ta sani, ke Surayya kiramin magajin gida na yi masa nasiha yana cewa yasan Allah ammh kuma baya adalci yarinyar nan ita da yaran nan suna Bukatarsa ammh ko keyarsa bamu gani ba, gwara shima dai yau na yi masa nasiha."
Surayya na Danne dariyanta tace"Gaskiyarki Innani."
Umma kuma sai ta kasa mgana Inna talatu ne ke fadin"Innani ko dai aiki ne ya yi masa yawa."
Innani tace"Wani aiki? Ya warke ne da ya koma aikin nasa ban sani ba?
Ta fad'a ta na kallon Surayya a Dage.
Da Sauri Umma tace"Bai koma ba ammh yace min ya kusa komawa, kuma zai zo ganin likita litini mai zuwa inaga zai zo ya gansu Innani."
Innani ta yi shuru kafin ta samu zarafin mgana Umma tace Surayya ta bama Hasiya ledan da suka zo da shi.
Ledan Atamfofi ne guda uku sai kayan yara masu kyau da yarari na karb'a cikin murna ima nuna ma su Inna Talatu.
Innani sai washe baki take yi tana fad'in"Lalle ana yi da wayan nan yaran."
Umma dai bata biye mata ba, sallah suka yi sannan suka ci abinci Direba ma an kai masa nasa daga waje, Umma sai da Surayya tace Umma ta ijiye su Asim taci abinci sannan ta ba ma Inna talatu su, suna ta wasan su ba su da rigima da rana sai kukan Dare in daya ya fara daya zai kama sai asuba taimakona daya su inna Talatu ai da na raina kaina shiyasa ko kibar Jegon nan na kasa yi, sai dai cikar Haihuwa kawai da ya ragemin Rama na, sannan kumburin da na yi da Ciki har a lokacin kafafuwana ba su gama Saccewa.
Karfe uku da wani abu suka tafi bayan sun yi sallar la'asar, Umma Kamar kada ta rabu da yaran haka nan take jin kaunarsu na ratsata kamar yaran su dawo wajenta da zama haka taji, innani kuma da Umma tace ko zata bisu su koma ne? Tace haka kurum ita ba ta tashi ba, a bari in tagaji da zama ita da kanta zata yi mgana, jin haka yasa Umma ta kama bakinta
A mota ma Hiran yaran kawai Umma ke yi ma Surayya, ita kuma ta na Biye mata ganin da gaske yaran sun shiga zuciyar Umma ba da wasa ba.
Haka da suka koma ta yi ta ma Abba mganarsu tana fadin kamar magajin gida yana karami.
Abba yace shima yaga haka Lokacin da yaje asibiti ya gansu.
Shifa sai gajiya ya yi ya koma yana kallon Umma yana Dariya a ransa tana ce masa kawai Sadiq ya bar Zariya nan ya Dauko matarsa tasa su dawo kusa da su da zama.
Abba na dariya yace"Jikokin su dawo kusa da ke da zama dai zaki ce."
Sai alokacin ta farga da abunda tace, Tsabar kaunar yara ne yasa bata son su yi nesa da ita, ba ta ki a kullum ta rika ganin su ba.
Sai ta yi shuru da bakinta Abba kuma yana jinjina ma Ubangiji mai kowa da kimai in ba'a yi wasa ba yaran nan sune Jarabatan Umma, tana kaunarsu kamar har sun fi Sadiq din matsayi yanzu acikin ranta.
Har Sadiq sai da ya Fahimci haka, ta kirashi tana ta gayamssa yara nan kamar Shi yana karami kuma ta rika ce masa ya gayama matarsa ta kula da su ta daina barin su ba kayan Sanyi kada sanyi ya kamasu su Umma masu jikoki, kamar ba'a taba Haifa mata jika ba sai akan su.
Shi kuma akace ya yi adalci sannan ya san cewa Sultana Amanqce a wajensa in yaci Amanarta Allah na kallonsa.
Cikin Tattausan lafazi ya kalli Umma kafin yace"Umma ni dai kinsan bani da matsala, diyarki ce ta ke da matsala ki gayamata rashin kunyar da ta koya daga baya bazan dauka ba, in tace bazata bari ba zamu yi ta samun matsala ne Umma."
Da Sauri Umma tace"Kin ji ko? Ke sultana bashi hakuri."
Ta fad'a ta na Hararan Sultana wacce ta sunkuyar da kanta Cikin yaukin baki tace"Kayi hakuri."
Jinjina kai ya yi kafin yace"Na yi hakuri, sai mgana ta gaba Bazan lamunci ta rika aibatamin matata ba, in ita bata san darajan ta ba, ni na sani kuma ni zan zauna da su bisa Amana ne, kamar yadda bazan lamunci ita Siya ta aibatata ba, haka itama bazan taba bari ta aibatata ba."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Hakane, Sultana ki gyara don Allah? Ku zauna lafiya da junan ku tare da hakuri da juna."
Kafin ta tafi sai da ta tabbatar da ta daidaita abunda ita ta yi silar lalacewarsa da kanta.
Sadiq ya rakata har bakin Titi ta hau mashi zuwa gida Abba yaso ya Dauko mota Shi kuma yace sai yaje yaga likita ko zai fara amfani da Mota da kafarsa.
Silar Umma yasa Sadiq ya Sauko ammh sai da Sultana ta kara sauke kai ta bashi Hakuri sannan ya hakura.
Shi namiji ne da mace ta zame masa ginshiki kuma ya dad'e baya tare da mace shiyasa bai gwasale kokarin Sultana ba, bayan kuma tana da hakki a kansa da shima ya sauke shi a wannan Daran.
Ita kuma abunda ke ranta itama ta yi tayi, ta samu ciki ta Haihu domin ta fi Hasiya samun matsayi a wajen Yaya Sadiq.
Da kuma kissanta yasa har washegari bai fita ko'ina ba yana tare da Sultana sannan har yinin ranar bai kira Siya ba sai da ya fita sallar mangariba ya samu ya kirata suka yi mgana tace suna gida sun dawo tun da Rana ita da Inna talatu.
Washegari kuma Big sis ta kirasa tace Umma ta kirata tun a jiya tace ta shirya zata rakata Zariya wajen Hasiya ta yi mata barka.
Har acikin ransa yaji dadi da yaso yaje ammh ganin zai koma ganin likita yasa yace bari ya had'a gabadaya.
Umma da Surayya suka tafi Zariya direban Abba kuma ya tukasu.
Daman kuma Surayya sun yi mgana da Hasiya tace mata ta koma dakinta nan suka wuce kai Tsaye.
********
Tun kafin Anty Surayya ta kirani ta gayamin Umma na tafe Assadiq ya gayamin shiyasa na gayama Inna Talatu, Habiba tare da ita muka taho ita ta tashi ta dora girki.
Wajajen azahar suka iso na yi wanka na Lokacin su Asim ma sun sha gayunsu suna tashin kamshi.
Sai a ranar na taba gaida Umma ta amsa min cikin sakewa kad'an duk da bata washe min baki ba.
Anty Surayya ta kwashi yaran ta zube mata a jikinta.
Sai ga Umma ta kura musu ido ta na kallonsu, duk yadda ta so kada yaran su yi tasiri a ranta sai da suka yi.
Farat d'aya taji sun bala'in Burgeta sun shiga cikin ranta da wani kauna.
Tana kallonsu idanuwanta suka kawo kwallah ta kalli Surayya lokaci d'aya ta na fadin"Surayya yaran nan kamar magajin gida Lokacin yana karami."
Surayya na dariya tace"Wlh nima haka nace Umma, sak Sadiq yana kamar su."
Umma ta rumgumesu a jikinta tana saka musu albarka.
Surayya ce ta waiga bata ga Innani ba shine ta yi mgana.
Ina mirmishi nace"Tana dakin maman Suhailat makociyata."
Inna talatu tace"Ta samu hira, maman suhailat akwai labarai a bakinta."
Surayya tace"An had'u da an dace kenan"
Muka yi dariya gabadayan mu, Habiba na aika ta kira Innanin sai gata da Sandarta da Uban gilashinta, jin muryansu Umma yasa ta washe baki ta na fadin"Salamatu kin huce kenan kin zo ganin jikokin naki? To wa ke fushi da yara? Balle yan Biyu kyautar Allah? Gwara da kika maida komai ba komai ba kin ji rayuwar nan ma nawa ta ke, yarinyar nan Hasiya da danginta duk mutanen kwarai ne, zaune na ke lafiya kamar ina cikin gidan sulaimanu."
Umma dai sai ta sauya mganar ta hanyar gaida Innani.
Surayya ma ta gaisheta ta amsa tana zama kan Kujera Lokaci daya tace"ina magajin gida?
Umma tayi saurin cewa"Yana can kinsan sultana ta koma gidanta."
Ta fad'a ta na satan kallona ni kuma ko a fuskata bata Fahimci wani abu ba.
Duk da naji wani iri, ganin har yau da Safe mun yi mgana ammh bai Fadamin ba, wata zuciyar tace ina Ruwan ki Hasiya?
Innani ta tabe baki kafin tace"Au ta gama koken koken iskancin nata ta koma kenan? Yarinyar haushi ta bani ni fa na ke mata mgana ta min banza yo, ni fa uwarta na haifa ba ita ba kuma Tunda taga ni nan na Saduda na bi Allah itama sai ta Saduda ta bi Allah da monzonsa, ohon mata dai ita ta sani, ke Surayya kiramin magajin gida na yi masa nasiha yana cewa yasan Allah ammh kuma baya adalci yarinyar nan ita da yaran nan suna Bukatarsa ammh ko keyarsa bamu gani ba, gwara shima dai yau na yi masa nasiha."
Surayya na Danne dariyanta tace"Gaskiyarki Innani."
Umma kuma sai ta kasa mgana Inna talatu ne ke fadin"Innani ko dai aiki ne ya yi masa yawa."
Innani tace"Wani aiki? Ya warke ne da ya koma aikin nasa ban sani ba?
Ta fad'a ta na kallon Surayya a Dage.
Da Sauri Umma tace"Bai koma ba ammh yace min ya kusa komawa, kuma zai zo ganin likita litini mai zuwa inaga zai zo ya gansu Innani."
Innani ta yi shuru kafin ta samu zarafin mgana Umma tace Surayya ta bama Hasiya ledan da suka zo da shi.
Ledan Atamfofi ne guda uku sai kayan yara masu kyau da yarari na karb'a cikin murna ima nuna ma su Inna Talatu.
Innani sai washe baki take yi tana fad'in"Lalle ana yi da wayan nan yaran."
Umma dai bata biye mata ba, sallah suka yi sannan suka ci abinci Direba ma an kai masa nasa daga waje, Umma sai da Surayya tace Umma ta ijiye su Asim taci abinci sannan ta ba ma Inna talatu su, suna ta wasan su ba su da rigima da rana sai kukan Dare in daya ya fara daya zai kama sai asuba taimakona daya su inna Talatu ai da na raina kaina shiyasa ko kibar Jegon nan na kasa yi, sai dai cikar Haihuwa kawai da ya ragemin Rama na, sannan kumburin da na yi da Ciki har a lokacin kafafuwana ba su gama Saccewa.
Karfe uku da wani abu suka tafi bayan sun yi sallar la'asar, Umma Kamar kada ta rabu da yaran haka nan take jin kaunarsu na ratsata kamar yaran su dawo wajenta da zama haka taji, innani kuma da Umma tace ko zata bisu su koma ne? Tace haka kurum ita ba ta tashi ba, a bari in tagaji da zama ita da kanta zata yi mgana, jin haka yasa Umma ta kama bakinta
A mota ma Hiran yaran kawai Umma ke yi ma Surayya, ita kuma ta na Biye mata ganin da gaske yaran sun shiga zuciyar Umma ba da wasa ba.
Haka da suka koma ta yi ta ma Abba mganarsu tana fadin kamar magajin gida yana karami.
Abba yace shima yaga haka Lokacin da yaje asibiti ya gansu.
Shifa sai gajiya ya yi ya koma yana kallon Umma yana Dariya a ransa tana ce masa kawai Sadiq ya bar Zariya nan ya Dauko matarsa tasa su dawo kusa da su da zama.
Abba na dariya yace"Jikokin su dawo kusa da ke da zama dai zaki ce."
Sai alokacin ta farga da abunda tace, Tsabar kaunar yara ne yasa bata son su yi nesa da ita, ba ta ki a kullum ta rika ganin su ba.
Sai ta yi shuru da bakinta Abba kuma yana jinjina ma Ubangiji mai kowa da kimai in ba'a yi wasa ba yaran nan sune Jarabatan Umma, tana kaunarsu kamar har sun fi Sadiq din matsayi yanzu acikin ranta.
Har Sadiq sai da ya Fahimci haka, ta kirashi tana ta gayamssa yara nan kamar Shi yana karami kuma ta rika ce masa ya gayama matarsa ta kula da su ta daina barin su ba kayan Sanyi kada sanyi ya kamasu su Umma masu jikoki, kamar ba'a taba Haifa mata jika ba sai akan su.