Sashe 20
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bata dauka mama zatayi haka ba, taso ayi komai cikin sirri a gama sai daga baya kowa sai yaji, Tunda dai kowa ya sani bata da zabi illah ta daga waya ta Kira Sadiya da Sajida da sa'adatu tare da Sajida tace su zo gida yau akwai taro.
Dukkansu ba su yi mamakin kiran ba, a cire Sajida da tasan komai sauran sun ce su Sakeena ne suka kirasu suna fad'a musu abunda ke Faruwa suma kansu ya kulle daman suna Shirin zuwan gidan su ji in da kuma aka Haihu a Ragaya
Tana mgana da Sadiya a waya ta na gani Saddiqa na kiranta ba ta yanke ba.
Kuma suna gama mgana da Sadiya Subai na kiranta sai ta daga suna mgana ta na kara yi mata wasu bayanan ita kam sai fad'a ta ke yi ta na zagin Sadiq daman kuma ta na da fad'a Tun asali ita.
Da surayya ta fad'a mata abunda Mama tayi sai kawai ta yi tsaki kafin tace"Allah ya kara masa uban wa yaja? Da bai aikata ba, wazai yi yawo da mganarsa. Kuma hukuncin Umma da Saddiqa ta fad'amin ya yi daidai sai dai ya zaba don Ubansa."
Jin yadda ta Dauki zafi yasa Jikin Suryyya ya yi sanyi, ta so ayi wannan abu cikin Sirri ne bata Dauka abun zai kwabe haka ba.
Bata kara sarewa ba sai da Subai ta tabbatar mata da ta na hanya itama zata zo, sai ta ci uban Sadiq kuma sai ta kara Zuga Umma saboda yasan abunda ya yi bai kyauta ba.
Da farko Surayya bata damu ba ammh yanzu ta da fahimci gayya ne guda za su had'u masu bambamcin Ra'ayi sai taji tsoron abunda zai Biyo baya.
Ita Asiya take Tausayawama ba Sadiq ba tasan shi Namiji ne kuma duk tsiya dai shi nasu ne.
Falo ta lekoni sai ta iske har na gyara kwanciya sai barci na ke yi sai ta kyaleni ta shiga ciki ta na Tufka ta na faman warwara.
Sadiq ta yi ta kira da farko wayarsa bata shiga sai daga baya ammh kuma baya Dauka.
Sai kuma Hankalinta ya tashi ta Dauko ko wani abu ne ya same shi, sai da ya turo mata sakon ya na kan hanya ya kusa isowa gusau sannan ta samu natsuwa.
*******
11:13am
Karfe sha d'aya na safe Sadiq ya iso Gusau motar haya ya shigo daga Abuja bai zo da Motarsa ba, saboda Halin Fargaban da ya ke ciki bazai iya Samun natsuwar tuki ba.
Farko gidansa ya fara sauka Dake millions Quaters, ammh sai me Sultana bata nan, megadin gidan da Abba ya saka kuma ya ke biyansa albashi ya fad'a masa yace Tun safe suka fita da farko ya dauka Sun tafi makaranta ne.
Ya na da key din gidan a hannunsa dashi ya yi amfani ya Bude gidan ya shiga ya ijiye kayansa ya yi wanka sannan Ya taho nan gidan.
Yazo ya iske Abba baya nan ya fita Mallam Tajudeen ne ya ke fad'a masa Tun daga bakin get.
Shashen Umma ya fara isa, nan ya Iske Saddiqa da Sadiya, a yanayin kallon da suke masa yasa ya san suma susan komai sai kawai ya had'e rai, ya na cin mgani hannayensa suna sarke cikin Aljihun saukakken Farin yadin da ke jikinsa dinki riga da wando na zamani.
Umma na cikin daki, taki fitowa sai daya bita da kansa ammh kuma ya na durkusawa da niyar gaisheta yaga ta mike tsam ta bude kofar Tiolet ta shige da farko ya zata, ta shiga ta kama Ruwa ne zata fito sai da yaga yafi minti ashirin Umma bata fito ba ya zargi wani abu tunda shi dai bai ji karan Ruwa ba, kuma yaganta da wankanta tas ba wanka ta ke yi ba, in ya gane daidai shi ne bata son gani.
Cikin wani yanayi ya fito daga Falon sai kuma ya had'e da Sajida da ta iso ba Dadewa sun had'a kai da juna suna ta kuskus.
Suna ganinsa sai suka yi shuru suna kallonsu kallo daya ya yi musu ya Dauke kai zai fita, daman su Sadiya sun gaisa da shi da ya shigo, Sajida ce dai daman ba su gaisa ba.
Har ya kama hanyar Fita Sajida tace"A'a Sadiq ba mgana ne abun?
Kamar zai wuce sai ya fasa ya Juyo ya na kallonta kafin yace"Sorry ban lura da ke ba ne, Sajida ya gida da yaran?
Bai jira amsawarta ba ya fice suka rakasa da kallon mamaki.
Sajida ta rike Hab'a kafin tace"Wai yasan an san abunda ya aikata kuwa?
Saddiqa tace"Oho masa, zuwa yanzu ai ina jin yasan karyansa ta kare, Big sis ta gayamasaa tunda Abba da kansa yace ta kirasa tace yazo."
Sadiya tace"Ammh shi ko a fuskarsa ba alamun Tsoro ko nadama aciki.'
Sajida tace"Nima ai abunda nagani kenan, uhm baku san Sadiq ba ne yanzu sai ya rufe bakin kowa da Ayoyin Allah tare da Hadisan manzon Allah, Salallahu alaihi wasallam.
Sai Saddiqa da Sadiya suka yi dariya.
Shi ko ya na fita sai ya rasa ina zai nufa, kawai sai ya tsaya nan kofar Bangaren Umma yana Tunanin ta ina mganar auransa da Hasiya ta bayyana?
Duk iya hangensa bai hango masa wata kafar da ya bari a bud'e ba.
Tun jiya ya yi Tunanin ko Tahir ne? Ammh da ya kira Tahir ya yi challaging dinsa ba su kara rabuwar dad'i ba ma wannan karon.
Domin Tahir masifa ya faramai yana fadin da ya shiga tsaka mai wuyar da ya Sanya kansa aciki sai ya Kirasa ya na masa mganar Banza to ya saurara masa chan ya karata Tsuntsun da ya ja Ruwa shi ruwa zai yi ma dukan Tsiya kada ma ya kara kiransa daga karshe ya kashe masa waya.
Daganan ya kara tabbacin ba Tahir bane to waye? Ko dai Siya ce ta gayama Saliha? Ammh kuma ya na da kyakyawan yakini da Tabbacin Siya bazata yi abunda bashi cikin Tsarin sa ba.
Yana nan tsaye ya na wannan Tunanin bai ji ko zuwan Siyama ba sai jin muryanta ya yi ta na gaisheshi.
Cikin Firgigit ya dago ya na kallonta cikin mamakin ganinta.
Bata jira amsawarta sa ba, Saboda sai taji tana jin Haushinsa sannan ta na taya kawarta Sultana kishi.
wacce tun safe Umma ta kira su a waya tace sultana ta kwaso kayanta ta dawo gida.
Sanda suka zo Umma sai taki cewa komai, Siyama ce ta je bangaran Mama ta na fad'a mata abunda ya faru sai Maman ce ke zayyane mata abunda ya Faru, nan take taji ta na jin Haushim Yaya Sadiq tunda yaci Amanar Sultana.
Ita kuma Sultana har Anty Saddiqa kasa gayamata komai tayi, sai ta wuce bangaren Innani chan ne Innani ta zauna ta na kuka kamar an yi wani mugun abu ta warware ma Sultana komai har ta na cewa Hasiya tsohuwar kilaci ce Tunda an ce bazawarace ma ya aura ba yarinya ba, Ta yi tayi ma Sadiq Allah ya isa a gaban Sultana ta na kara fadin bata bashi har abada kuma bai isa ya yi ma Jikarta kishiya ba.
Sultana bata san ya ake jin girman Kishi a cikin zuciya ba sai yau, kasa sarrafa kanta ta yi taji gabadaya zuciyarta na wani irin zafi, wani irin bala'in kishin Sadiq ta ke jin acikin Zuciyarta tare da jin Haushin yadda ya Wulakantata ya iya auran wata mace kafin ita, Sai ta fara kuka ita kuma Innani ba lallashi sai faman Zugata ta ke yi, ta na fadin ta yi hakuri Sadiq fa ko ya zaba ko kuma ya saketa kowa ya yi ta kansa.
Ta na chan bangaren Innani ta na kuka, innani na gefe ta na kara iza Wuta, Farida ce kad'ai taje makaranta Allah yasa su sultana suna kokarin Fara jarabawar Fita ne.
Sadiq ya bi siyama da kallo da ke neman Shigewa bangaren Umma.
Cikin shakewar murya ya saka baki ya Kirata sai ta dawo ta Tsaya a gabansa.
Cikin mamaki yace"Baki je makaranta ba ne!? Ina sultana?
Kanta na kasa tace"Umma ta kira tace mu kawo kayanmu mu dawo gida."
Ido ya zaro kafin yace"Ita Umman ta ce haka?
Sai ta dago ta na kallonsa Lokaci daya ta na gyad'a masa kai.
Cikin Fad'uwar gaba yace"To yanzu ina ita Sultanan?
Kai Tsaye Siyama tace"Ta na bangaren Innani."
Aransa ya Furta Tabdijam, yasan ai kuma komai ya lalace tunda ya na da tabbacin Innani ba ta tab'a gyara abu ba sai dai ta bata.
Kai tsaye yace Siyama taje kawai shi kuma sai ya isa bangaren Mama su gaisa itama ya iske su Anty Sa'im, Sakeena da salima wacce ta iso itama da wuri.
Dukkansu ba su yi mamakin kiran ba, a cire Sajida da tasan komai sauran sun ce su Sakeena ne suka kirasu suna fad'a musu abunda ke Faruwa suma kansu ya kulle daman suna Shirin zuwan gidan su ji in da kuma aka Haihu a Ragaya
Tana mgana da Sadiya a waya ta na gani Saddiqa na kiranta ba ta yanke ba.
Kuma suna gama mgana da Sadiya Subai na kiranta sai ta daga suna mgana ta na kara yi mata wasu bayanan ita kam sai fad'a ta ke yi ta na zagin Sadiq daman kuma ta na da fad'a Tun asali ita.
Da surayya ta fad'a mata abunda Mama tayi sai kawai ta yi tsaki kafin tace"Allah ya kara masa uban wa yaja? Da bai aikata ba, wazai yi yawo da mganarsa. Kuma hukuncin Umma da Saddiqa ta fad'amin ya yi daidai sai dai ya zaba don Ubansa."
Jin yadda ta Dauki zafi yasa Jikin Suryyya ya yi sanyi, ta so ayi wannan abu cikin Sirri ne bata Dauka abun zai kwabe haka ba.
Bata kara sarewa ba sai da Subai ta tabbatar mata da ta na hanya itama zata zo, sai ta ci uban Sadiq kuma sai ta kara Zuga Umma saboda yasan abunda ya yi bai kyauta ba.
Da farko Surayya bata damu ba ammh yanzu ta da fahimci gayya ne guda za su had'u masu bambamcin Ra'ayi sai taji tsoron abunda zai Biyo baya.
Ita Asiya take Tausayawama ba Sadiq ba tasan shi Namiji ne kuma duk tsiya dai shi nasu ne.
Falo ta lekoni sai ta iske har na gyara kwanciya sai barci na ke yi sai ta kyaleni ta shiga ciki ta na Tufka ta na faman warwara.
Sadiq ta yi ta kira da farko wayarsa bata shiga sai daga baya ammh kuma baya Dauka.
Sai kuma Hankalinta ya tashi ta Dauko ko wani abu ne ya same shi, sai da ya turo mata sakon ya na kan hanya ya kusa isowa gusau sannan ta samu natsuwa.
*******
11:13am
Karfe sha d'aya na safe Sadiq ya iso Gusau motar haya ya shigo daga Abuja bai zo da Motarsa ba, saboda Halin Fargaban da ya ke ciki bazai iya Samun natsuwar tuki ba.
Farko gidansa ya fara sauka Dake millions Quaters, ammh sai me Sultana bata nan, megadin gidan da Abba ya saka kuma ya ke biyansa albashi ya fad'a masa yace Tun safe suka fita da farko ya dauka Sun tafi makaranta ne.
Ya na da key din gidan a hannunsa dashi ya yi amfani ya Bude gidan ya shiga ya ijiye kayansa ya yi wanka sannan Ya taho nan gidan.
Yazo ya iske Abba baya nan ya fita Mallam Tajudeen ne ya ke fad'a masa Tun daga bakin get.
Shashen Umma ya fara isa, nan ya Iske Saddiqa da Sadiya, a yanayin kallon da suke masa yasa ya san suma susan komai sai kawai ya had'e rai, ya na cin mgani hannayensa suna sarke cikin Aljihun saukakken Farin yadin da ke jikinsa dinki riga da wando na zamani.
Umma na cikin daki, taki fitowa sai daya bita da kansa ammh kuma ya na durkusawa da niyar gaisheta yaga ta mike tsam ta bude kofar Tiolet ta shige da farko ya zata, ta shiga ta kama Ruwa ne zata fito sai da yaga yafi minti ashirin Umma bata fito ba ya zargi wani abu tunda shi dai bai ji karan Ruwa ba, kuma yaganta da wankanta tas ba wanka ta ke yi ba, in ya gane daidai shi ne bata son gani.
Cikin wani yanayi ya fito daga Falon sai kuma ya had'e da Sajida da ta iso ba Dadewa sun had'a kai da juna suna ta kuskus.
Suna ganinsa sai suka yi shuru suna kallonsu kallo daya ya yi musu ya Dauke kai zai fita, daman su Sadiya sun gaisa da shi da ya shigo, Sajida ce dai daman ba su gaisa ba.
Har ya kama hanyar Fita Sajida tace"A'a Sadiq ba mgana ne abun?
Kamar zai wuce sai ya fasa ya Juyo ya na kallonta kafin yace"Sorry ban lura da ke ba ne, Sajida ya gida da yaran?
Bai jira amsawarta ba ya fice suka rakasa da kallon mamaki.
Sajida ta rike Hab'a kafin tace"Wai yasan an san abunda ya aikata kuwa?
Saddiqa tace"Oho masa, zuwa yanzu ai ina jin yasan karyansa ta kare, Big sis ta gayamasaa tunda Abba da kansa yace ta kirasa tace yazo."
Sadiya tace"Ammh shi ko a fuskarsa ba alamun Tsoro ko nadama aciki.'
Sajida tace"Nima ai abunda nagani kenan, uhm baku san Sadiq ba ne yanzu sai ya rufe bakin kowa da Ayoyin Allah tare da Hadisan manzon Allah, Salallahu alaihi wasallam.
Sai Saddiqa da Sadiya suka yi dariya.
Shi ko ya na fita sai ya rasa ina zai nufa, kawai sai ya tsaya nan kofar Bangaren Umma yana Tunanin ta ina mganar auransa da Hasiya ta bayyana?
Duk iya hangensa bai hango masa wata kafar da ya bari a bud'e ba.
Tun jiya ya yi Tunanin ko Tahir ne? Ammh da ya kira Tahir ya yi challaging dinsa ba su kara rabuwar dad'i ba ma wannan karon.
Domin Tahir masifa ya faramai yana fadin da ya shiga tsaka mai wuyar da ya Sanya kansa aciki sai ya Kirasa ya na masa mganar Banza to ya saurara masa chan ya karata Tsuntsun da ya ja Ruwa shi ruwa zai yi ma dukan Tsiya kada ma ya kara kiransa daga karshe ya kashe masa waya.
Daganan ya kara tabbacin ba Tahir bane to waye? Ko dai Siya ce ta gayama Saliha? Ammh kuma ya na da kyakyawan yakini da Tabbacin Siya bazata yi abunda bashi cikin Tsarin sa ba.
Yana nan tsaye ya na wannan Tunanin bai ji ko zuwan Siyama ba sai jin muryanta ya yi ta na gaisheshi.
Cikin Firgigit ya dago ya na kallonta cikin mamakin ganinta.
Bata jira amsawarta sa ba, Saboda sai taji tana jin Haushinsa sannan ta na taya kawarta Sultana kishi.
wacce tun safe Umma ta kira su a waya tace sultana ta kwaso kayanta ta dawo gida.
Sanda suka zo Umma sai taki cewa komai, Siyama ce ta je bangaran Mama ta na fad'a mata abunda ya faru sai Maman ce ke zayyane mata abunda ya Faru, nan take taji ta na jin Haushim Yaya Sadiq tunda yaci Amanar Sultana.
Ita kuma Sultana har Anty Saddiqa kasa gayamata komai tayi, sai ta wuce bangaren Innani chan ne Innani ta zauna ta na kuka kamar an yi wani mugun abu ta warware ma Sultana komai har ta na cewa Hasiya tsohuwar kilaci ce Tunda an ce bazawarace ma ya aura ba yarinya ba, Ta yi tayi ma Sadiq Allah ya isa a gaban Sultana ta na kara fadin bata bashi har abada kuma bai isa ya yi ma Jikarta kishiya ba.
Sultana bata san ya ake jin girman Kishi a cikin zuciya ba sai yau, kasa sarrafa kanta ta yi taji gabadaya zuciyarta na wani irin zafi, wani irin bala'in kishin Sadiq ta ke jin acikin Zuciyarta tare da jin Haushin yadda ya Wulakantata ya iya auran wata mace kafin ita, Sai ta fara kuka ita kuma Innani ba lallashi sai faman Zugata ta ke yi, ta na fadin ta yi hakuri Sadiq fa ko ya zaba ko kuma ya saketa kowa ya yi ta kansa.
Ta na chan bangaren Innani ta na kuka, innani na gefe ta na kara iza Wuta, Farida ce kad'ai taje makaranta Allah yasa su sultana suna kokarin Fara jarabawar Fita ne.
Sadiq ya bi siyama da kallo da ke neman Shigewa bangaren Umma.
Cikin shakewar murya ya saka baki ya Kirata sai ta dawo ta Tsaya a gabansa.
Cikin mamaki yace"Baki je makaranta ba ne!? Ina sultana?
Kanta na kasa tace"Umma ta kira tace mu kawo kayanmu mu dawo gida."
Ido ya zaro kafin yace"Ita Umman ta ce haka?
Sai ta dago ta na kallonsa Lokaci daya ta na gyad'a masa kai.
Cikin Fad'uwar gaba yace"To yanzu ina ita Sultanan?
Kai Tsaye Siyama tace"Ta na bangaren Innani."
Aransa ya Furta Tabdijam, yasan ai kuma komai ya lalace tunda ya na da tabbacin Innani ba ta tab'a gyara abu ba sai dai ta bata.
Kai tsaye yace Siyama taje kawai shi kuma sai ya isa bangaren Mama su gaisa itama ya iske su Anty Sa'im, Sakeena da salima wacce ta iso itama da wuri.