← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 83

Sashe 33

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Har gabanta ya taka bayan ya sake ni, ya tsaya kam sannan ya daga hannu ya nunani kafin yace"Kinga wannan?
To itace matar da na fara aura kafin ke, saboda haka daga yau ya kamata ki sani tana gaba da ke, ke zaki fara girmamata kafin ita ta girmamaki."
Sultana ta kallesa kafin tace"Tab."
Ta fad'a ta na Tura baki.
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Eh haka nace saboda haka daga yau in kika ganta ke zaki gaisheta ki, ya kamata ki haddace cewa ita na fara aure kafin ke, ni kuma ba sakaran namiji ba ne da zan zauna kina wulakantamin mata ba, Sonta na ke yi shiyasa na aureta kamar yadda kema ina sonki ne yasa na aureki."
Sultana sai hawaye ta na so ta saka kuka.
Sajida ta gaji da shuru tace"Ammh Sadiq baka da kunya wlh."
A fusace ya daga mata Hannu kafin yace"Ban saka da ke ba mallama ki Rufemin baki, ko ina ruwan ki da shiga Hurimin iyalaina.?
Ya karishe fad'a yana nuna ta da yatsarsa.
Ai sai ta kasa mgana ganin ya harzuka Sadiya ma na shirin magana a harzuke yace"Kada wace ta kara sakamin baki acikin magana ta da iyalaina. In ba haka ba  ran mata zai baci na rantse da Allah."
Surayya ta shigo tana gefe ta na mirmishi.
Kan Sultana ya koma yana fadin"Sabosa haka ki shiga taitayinki, in kikace zaki yi ma matata fitsara maganinki zan yi bana son reni kin sani."
Sultana ta mike ta saka kuka ta na Fadin"Ai ba sai ka nun ma duniya baka sona ba, auren hadi aka yi mana shiyasa ka ke kare ma wannan banzar matar taka mai kwacen miji kawai"
Taso mata ya yi kamar zai Daketa ta yi baya sai kawai ga Umma Tsulum a falon.
Shi ya hanasa kara wani motsi ni kaina gabana sai fad'uwa ya ke yi
Sajida na ganin Umma ta Nufeta ta na karanta mata Assadiq ya zagesu saboda ni.
Har yana nufar Sultana zai daketa.
Umma bata wani tsaya Bincike ba ta nuna ma Sadiq kofa tace ya fita ya bata wuri yana Hucin ta hanashi mgana ya fita.

Ni kuma ina Tsaye kafafuna na rawa Surayya ta taso ta wankeni Umma ta d'aga hannu ta na karisowa cikin Falon lokaci daya ta na kallona kafin ta juya ta kalli Sultana tana fadin"Share hawayen ki, matukar ina raye ba wanda ya isa ya Tozarki."
Sultana ko kuka take yi sosai daman ganin kayan mu iri daya yasa su Sajida suka kara Zugata da cewa ita bai Dauketa da Muhimmanci ba muraranta ya ke nuna yafi kaunata sma da ita, ita kuma bakin kishi ke dawainiya da ita.
Umma ni ta kalla a fusace kafin tace"Ai in baki had'a fada tsakanin yan'uwana juna ba baki ci sunan ki  bakar Annoba ba, kin ji kunya kuma kin yi asara ke yanzu a dad'in ki ne ki zo ki raba kan zuru'a? Ki saka d'ana ya na jayayya dani sannan ki sakashi yana Sa'insa da yayyensa to ki saurareni dakyau har Abada bazan taba karbanki a matsayin matar Abubakar ba, Sultana na sani kuma in dai ke ya zaba wlh sai dai na sallama miki shi, shi kadai Annobarki ta kona sa, Fita ki barmin falo kafin raina ya baci na saka ayi miki koran kare."
Daman tun da ta fara mgana na fara kuka ina jin tace na fita na juya ina jin cikina na Juyawa na fita ina kuka.
Surayya ta kalli Umma ba dad'i kafin tace"Umma m."
"Ke ma bita ki fitar min daga falo."
Surayya ta kalli Umma kafin ta kad'a kai kawai ta juya ta bi bayana su Sajida suka rakata da wani kallo aransu suna tunanin Big sis bata kishin Umma.
Ta na fitowa ta ganni ina kuka, sai ta rikeni zuwa mota itama ranta a bace yake Sadiq ta kira tace yazo ya Tukamu zuwa gida.

Ya shiga damuwa ganin yadda nake kuka sai ya fara cewa ita ta lallasheni.
Da damuwa a saman fuskarta tace"Lamarin Umma ya fara nisa, Su Sadiya suna kara zugata ni yanzu kwata kwata ta daina bani fuska."
Sadiq yace"Nima wlh abun duk ya Dameni."
Surayya ta sauke Numfaashi kafin tace"Mallam na gummi zaka je ka sanar ma abunda ke faruwa na tabbata in ya yi mata magana zata ji."
Sadiq yace"Na yi tunanin haka, ammh cewar Abba ne na bata Lokaci Shiyasa ban je na samesa ba"
Surayya tace"Ai kada ka jira, ammh kafin nan gobe ka maida Hasiya gida, zamanta a wajena ni kaina Umma ta fara fushi dani kuma bata da sakewa kwata kwata anan."
Ya aminta da shawaranta yace haka za'ayi in zai kaini Zariya zamu Tsaya anan Gummi din.
Haka ko akayi, tun safe muka tafi Abba kawai da Innani ma yi ma sallama da kanshi ya hanani Shiga wajen Umma, fuskata har ta Kumbura saboda kuka da kuma duka siyayyan da Anty Surayya ta yi min muka taho da su.
Sai da muka fara biyawa Gummi Gidan su Umma kamar yadda yace min suka gana da mallam zakari na wajem awa d'aya.
Da kanshi ya yi mishi bayanin komai, mallam zakariya na ta fad a yace kuma sai ya saba Umma har Abban ma da ya Biye mata.
Sam a gidan ba'a nuna min wani kyama ba nan muka yi azahar muka ci abinci sannan muka dauki hanya.
Sai bayan la'asar muka shigo Zariya ganin yamma tayi yace sai da safe zai wuce Abuja.
A daran ina jinsa ya Kira mahaifin Sultana shima ya karanta masa abunda ke faruwa.
Ran mallan Shitu ya baci yace gobe goben nan zai je ya samu sultana sai ya sab'a mata itama.

Sadiq daman so ya ke daga Umma har Sultanan a yi musu fad'a alokaci daya.
Kwana ya yi yana lallaahina tare da alkwarin  bazai taba barina ba.
Ni na ma b'ata masa Lokaci sai wajen goma ya bar gidan ya kama hanyar Abuja.
Sadiq ya fita cikin Damuwa ga koken koken da na kwana yi.
Ga kuma matsalan su Umma da Sultana gabadaya sun chazamasa kai.
Ya bar kaduna kenan da kad'an baisan yadda aka yi ba motar sa ta kwace masa ba, shi dai yaji mota na Tamaula dashi akan Titi daganan Hankalinsa ya gushe.
Yaji sanda motar ta Tsaya ya kuma san ya jisa zaune a inda ya ke
jini na bin fuskarsa tunda ya saka Seat belt.
Daga nesa nesa yaji ana salati da sallallami tare da mganganun mutane daganan yaji Duniyar ta tsaya masa cak.

*Janafty*
*TMWBK3010*
P

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

Duk sammakon da Mallam Zakari ya buga daga Gummi zuwa Gusau sai da ya zo ya iske Mallam shitu ya rigasa zuwa daga Shinkafi domin ana idar da sallar asuba ya kamo hanya so ya ke ya yi abunda zai yi. In ya gama ya kama hanya koma can har kuma yaje ya yi yan Harkokinsa.
Sultana sai da ta raina kanta, ta sha Fad'a kamar me, dukanta ne kad'ai Mallam Shitu bai yi ba, bata tab'a sanin cewa ya iya fad'a haka ba Tunda wani abu bai taba had'a su ba, sannan kuma ba ta girma a gabansa ba sai dai zuwa ta na dawowa.
Umma kuma sai ta so ta kareta ita ma Mallam Shitu ya kalleta yana fadin"Maganar gaskiya Hajiya ki daina mara ta baya, da ke har ita baku taki gaskiya ba abunda ku ke son ku aikata ba gaskiya ba ne kuma ba Shari'a bace."
Sannan ya kara kallon Sultana da ke gefen Umma ta na ta faman kuka, har Abba na wajen shi da Innani tunda a shashen innanin ne ake zaman.
Cikin daga murya yace"Ke kuma ki sani in dai kika Boyema zuciya kika ce zaki wulakanta mijin ki, ke ce a kasa matukar kika rasa miji kamar Abubakar ba baki na yi miki ba ammh Wlh tallahi bazaki taba samun kamarsa ba, kuma ina so ki sani bai kamata ki zama Butulu ba, in mahaifiyarsa ta nuna fushi a kansa ta na da gaskiya itace uwa a garesa ammh ke baki da wannan Hurumin tunda kina karkarshinsa ne daidai da rana d'aya in kika sab'a masa sai Allah ya Hukuntaki akan laifin da kika aikata."
Sultana na kuka Fuskata duk hawaye ta dago ta na fad'in"Baba aure fa ya yi bansani ba."
Dakuwa ya yi mata kafin yace"Kin ga naki, ana rabaki da kiwon awaki kina kokarin gayamin kyalla ta Haihu? Ya yi auren sai me? Ke ki kiyayi kanki ai ita ya fara aura in yaso sai yace ya fasa auranki kuma ba mai yi masa Dole, ammh bai yi haka ba sai ke ce don rashin Mutumcin ki ke har kara fad'in aure ya yi, to ya yi auren sai ki hanasa abunda Allah yace ya yi, ni ai da ya Burgeni ma da uku ya aura sai ku zama ku hu'du naga yadda zaki yi, banda shashanci ko ni Ubanki bayan mahaifiyarki matana Biyu saboda Rashin adalci irin naki don mijinki ya yi aure sai kice zaki fara yi masa rashin d'a."
Daga Umma har Sultana suka yi shuru, Umma ranta ya gama baci saboda ta da na tabbacin Sadiq ne ya Kirasa ya fad'amasa kuma taci alwashin zai zo ya sameta sai ya raina kansa.
Ita kuma Sultana kukan yadda Babanta ya kasa Fahimtar irin cin Amanar da Yaya Sadiq ya yi mata ne, ammh kuma sai ya zo ya Bige da yi mata fad'a.
Fata fata ya yi ma sultana itama Umma ya yi mata nasiha yajawo Hankalinta, ammh duk bata ji ba ta dai nuna kamar ta fahimce shi kuma zata gyara ne.
Kafin tafiyarsa sai da ya jaddadama Sultana ta koma dakinta mijinta yau ba sai gobw ba, kuma sannan ta girmama ra'ayin mijinta. in kuma yaji Sabanin haka zai kara dawowa ammh ta sani dawowar bazata yi mata kyau ba.
Chapter 33 · 0% Book details