Sashe 80
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da asuba na kasa tashi duk jikina Tsami ya ke yi min, nasan ko irin Hukuncin Assadiq.
Yana gani ina tafiya dakyar yana min Dariya bayan ya dawo sallar asuba.
Ni kuma na yi masa Fuska na kumbura Fuska har na Dauro alwala nazo na yi sallah.
Bayan na idar kuma na zo na kwanta a can gefe na juya masa baya shi kuma yana duba wani abu a wayarsa.
Sai ga shi har ta bayana yazo ya na Leka Fuskata.
Harara na maka masa ina kara Hura Hanci.
Sai kawai ya duka ya sumbaci Goshina kafin yace"I love u My siya. Allah ya yi miki albarka."
Sai naji zuciyata ta yi haske cikin mirmishin jin dad'i nace"Ameen Assadiq mijin Hasiya."
Ina kwance ina jinsa sanda ya yi wanka, sai da ya fito ne yana Shiryawa na lallaba na fita abun mamaki a kitchen naga Amna har ta saka Ruwan zafi a Butar da na ke Dafawa.
Ta na ta goge goge a kitchen din, tana ganina ta yi saurin gaisheni na amsa ina fadin"Eyee Amna an girma, to me zaki dafa muku?
Kin iya soya kwai?
Ta gyad'amin kai, ammh kada na barta ita kad'ai yasa na tsaya ina gayamata abunda zata yi.
Nace ta saka kayan kamshi da albasa saboda karni.
Falo na koma na Tusho hancina da Hijabi ammh kamshin kwan har ya Fara sakamin tashin zuciya.
Assadiq ya fito cikin Shirin fita yana ganina na toshe hanci yace"Siya to haka zaki cigaba da zama baki son kamshin komai?
Shima yana mgana ina jin kamshin Sabulan wankansa tunda na hanashi saka Turare na kwashe gabadaya na boye.
Kamshi daya na ke shaka na zauna lafiya shine na Turaren wuta.
Ganin ina yunkurin Amai yasa na tashi da gudu na koma daki na kwanta ina toshe kaina acikin Filo.
Ko da Assadiq ya gama karyawa ya zo min sallama na yi barci.
Nima zuwan Hauwa'u ya tadani na tashi na iske Amna ta gyara gidan tas yana tashin kamshi.
Kafin Hauwa'u su koma ita ke yi abincin dare saboda su Assadiq, ammh duka duka kwana Hudu suka yi suka tafi.
Ban so tafiyar ta ba ina ta ce ma Assadiq ya roki Tahir ya bar ta su yi ko da sati.
Yana kallona yace"Siya ke fa wani lokacin kina da rigima, mutum da matarsa kuma sai kice ya tafi ya bar miki ita anan?
Da sauri nace"A'a ya zauna shima ya yi sati mana"
Dariya ya fashemin da shi da ya harzukani na juya masa baya.
Ya yi saurin Rumgumeni ta baya yana Fad'in"Tahir fa yana da abubuwan yi Siya, sai ya zo kawai ya tare a wajen mu? Sorry kin ji to ki bari in kin Hauhi sai mu je wajensu mu yi musu wata d'aya tunda baki son Rabuwa da Hauwa'un"
Yadda ya fad'i mganar me yasa nasan zolayata ya ke yi, Bayan hannuna na saka na Tokare masa kirji.
Shi kuma da yaji zafi sai ya matsemin Nono na guda d'aya.
Da naji zafi na make hannunsa ina Fad'in"Assadiq makasata ne fa?.
Yana dariya yace"To ke ma ki rama a nawa makasan mana?
Ya fad'a yana kashemin ido d'aya.
Kallonsa na yi bakina alaikun naja jikina na sauka daga gadon ina fad'in"A'a ba sai na rama ba, na yafe maka Assadiq."
Kokarin tashi ya ke yi ya Biyo ni na zura da gudu ya kira sunana yana fad'in"Siya ki yi a hankali."
Haka muka cigaba gudanar da Rayuwarmu ni da Assadiq cikin rayuwar da muka zab'a ma kanmu.
Ba zan ce ban taba ganin ma'aurata kamar mu ba, ammh dai za'a dade ba'a samu kamar mu ba.
Ba wai bama samun sabani ne bane muna samu, ammh kuma muna kokarin daidaita kanmu.
Tunda musan hallayan junan mu sai muka ci mganin zama tare.
Tausayin junan mu shi ya fara gina zaman aurren mu, sannan daga baya soyayya da kauna suka Biyo baya.
Sannan ni kuma na zauna da shi Cikin Biyayya, Duk abunda na san zai sab'a ma Assadiq ina kauce masa shima duk abunda yasan zai sosa min rai yana kauce ma aikata shi Saboda kada raina ya so su.
Zuwan Amna ya taimakamin sosai ta iya saukakkun girkr girke, Har Assadiq shima mamakin kokarin yarinyar yake yi har ni sai da ya yi min mgana.
Da safe ita zata dafa musu abun karyawa kamar su tea, soya kwai ko doya ko dankali.
Da rana kuma nace ta dafa abunda ta ke so, in kuma wani abu zata sha ko goldemorn ko Cornfl sai ta jika ta sha, da Daddare kuma na kan nuna mata abunda zata yi ko ta Dafa shinkafa jalop ko taliya.
Sai dai ina gefe na toshe hanci watarana na wanye lafiya watarana kuma na yi ta kwarara amai.
Assadiq kan siyo Tuwo watarana da daddare in yaji sha'awan haka.
Wannan watan ganin Amna yasa yace zai je gusau ya Duba Sultana da su Umma nace yakamata.
Ranar jumma'a ya tafi da safe ya barni dagani sai Amna.
Ni fa kwanciya ce aikina kamar wata mai laluran barin jiki.
Wayar ma yanzu in ba kirana aka yi ba, bana bi ta kanta.
Kwana Uku Assadiq ya yi ya dawo ya kawomin Hotunan su Asim da Viedo da ya yi ta daukansu.
Sai suka karamin girma a ido, yace ko damuwa ba su yi sun zama yan gida.
Har Innani sai da tace ya'yan magajin gida sun zo da alheri gidan nan.
D'an zagayen da suke yi a bangarenta tace yana deb'e mata kewa sosai.
Kuma yace da zai tafi ba su yi kuka ba har suna yi masa Bye bye.
Umma na cewa ba za su ku je wajen Mami ba? Suka noke a jikinta.
Ina dariya nace"Shikenan sai mu bar ma su Umma, mu ma zamu haifi namu Allah ya bani yar mace ina so Assadiq."
Yana kallon Wayarsa yace"Allah ya baki, mafi alheri siya."
Na amsa masa da Ameen.
Sai washegari da bai fita aiki ba baya jin dadi zazzabi ya kwana da shi.
Sai nace ya kwanta a gida ya huta sai dai ya kira can wajen aikin su ya gayamusu.
Dani da shi ranar a daki muka yini, muna shan soyayyarmu da Hiran mu.
Muna kwance ya bani wayarsa ina kallon Hotona sai naa ga Ummi an Dauketa ta yi kiba kamar ba ita ba.
Sai na juya ina kallonsa ya na kwance ya Rufe ido ammh ba barci ya ke yi ba.
Tab'osa na yi kafin nace"Na manta ban tambayeka ba ya su sultana da Ummi?
Fata suna lafiya?
Assadiq ya yi shuru kafin can ya mike zaune da sauri yana dariya.
Cikin mamaki nace"Miya faru?
Cikin gyad'a kai yace"Sultana na can na kuka wai na yi sonkai na kara yi miki ciki ita ban yi mata ba."
Ido na zaro ina kallonsa shi kuma sai ya yi dariya kafin ya cigaba da fad'in"Wlh rigimar da naje tarar ta na yi kenan, tace ba na mata adalci ina Fitita ki a kanta, da farko cikin yan Biyu na yi miki ita kuma da ba na kaunarta d'aya na yi mata shine yanzu da son kai da rashin Adalci na yi miki Ciki ita ban yi mata ba to wlh itama bata yarda ba in ina son na zama mai adalci itama na yi mata ciki."
A tare da ni da shi muka Fashe da dariya cikin Dariya nace"Assadiq to kai baka yi adalci ba, me yasa ka dawo ba ka yi mata cikin ba?
Mirmishi ya yi kafin ya koma ya kwanta ya yi filo da hannayensa.
Cikin Tattausan lazafi ya kira sunana"Hasiya."
Na amsa masa sai ya mika Hannun ni kuma na kama ya jawoni jikinsa ya Rumgumeni na yi matashin kaina a saman kirjinsa.
Cikin Sanyin murya yace"Ina so na fad'a miki wata magana."
Cikin ba shi hankalina nace"Ina jinka. Sai ka fad'a"
Kai Tsaye yace"Kin san meyasa na gayamiki wani abu daya danganci sultana game da ni yanzu?
Sai na girgiza masa kai, yana shafa kaina yace"Saboda na nuna miki Sultana bazata taba sauyawa ba. Halinta ne haka zafin kishi zargi da kuma rashin son zaman lafiya, a baya na damu da Fitinarta ammh daga baya da na zauna ma Fahimci halinta har ga Allah lamarinta ya Daina damuna, can u just imaging ta tasani gaba ta na min kuka wai sai na yi mata ciki in ina so na yi adalci.?
Ina yar dariya nace"To sai ka ce mata mene?
Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Me zan ce mata? Tun ta na bani mamaki sai ta dawo bani dariya da Tausayi, yanzu dai na lallasheta nace ta bari itama zan yi mata ciki tunda shi ta ke so"
Mirmishi na yi ban yi mgana ba shi kuma ya Cigaba da fad'in"Shiyasa na ke son na gayamiki ki yi hakuri da ita don Allah kin ji ko? Tunda mun san halinta mu zauna da ita a yadda ta ke"
Ina jinsa sai na gyad'a masa kai ina fad'in"Baka da matsala dani in sha Allahu"
Da bakinsa ya ke fad'amin wasu daga cikin Rigigiman su, wasu na yi ta Dariya sultana yar bala'i ce wlh.
Yace yanzu duk ta b'ata da su Sadiya aammh yasa ta ba su Hakuri.
Yace Har Umma fa in abunta ya tashi sai ta yi mata yaji tace an yi mata gori ko Umma ma nuna son kai.
Yanzu ma zuwan su Asim sai da tace Umma ta yi sonkai.
To itama Ummi zata kawo mata, Umma tace sai ta bari ta yayeta.
Ammh sultana bata ji ba sai ga shi ta had'o kayan Ummi ta kawo ta wajen Umma.
Ina Dariya nace"Kai to wannan jaririyar aka rabata da uwarta ai sai a dauki hakki."
Assadiq yace"Umma tace Shegantakan Sultana ya isheta wlh, sai da Abba ya shiga mganar yana ta lallashi yanzu dai tace itama ta na yayeta Umma zata riketa Tunda ta rike ya'yan kishiyarta."
Yana bani Labarin ina auna wasu abubuwan.
Yana gani ina tafiya dakyar yana min Dariya bayan ya dawo sallar asuba.
Ni kuma na yi masa Fuska na kumbura Fuska har na Dauro alwala nazo na yi sallah.
Bayan na idar kuma na zo na kwanta a can gefe na juya masa baya shi kuma yana duba wani abu a wayarsa.
Sai ga shi har ta bayana yazo ya na Leka Fuskata.
Harara na maka masa ina kara Hura Hanci.
Sai kawai ya duka ya sumbaci Goshina kafin yace"I love u My siya. Allah ya yi miki albarka."
Sai naji zuciyata ta yi haske cikin mirmishin jin dad'i nace"Ameen Assadiq mijin Hasiya."
Ina kwance ina jinsa sanda ya yi wanka, sai da ya fito ne yana Shiryawa na lallaba na fita abun mamaki a kitchen naga Amna har ta saka Ruwan zafi a Butar da na ke Dafawa.
Ta na ta goge goge a kitchen din, tana ganina ta yi saurin gaisheni na amsa ina fadin"Eyee Amna an girma, to me zaki dafa muku?
Kin iya soya kwai?
Ta gyad'amin kai, ammh kada na barta ita kad'ai yasa na tsaya ina gayamata abunda zata yi.
Nace ta saka kayan kamshi da albasa saboda karni.
Falo na koma na Tusho hancina da Hijabi ammh kamshin kwan har ya Fara sakamin tashin zuciya.
Assadiq ya fito cikin Shirin fita yana ganina na toshe hanci yace"Siya to haka zaki cigaba da zama baki son kamshin komai?
Shima yana mgana ina jin kamshin Sabulan wankansa tunda na hanashi saka Turare na kwashe gabadaya na boye.
Kamshi daya na ke shaka na zauna lafiya shine na Turaren wuta.
Ganin ina yunkurin Amai yasa na tashi da gudu na koma daki na kwanta ina toshe kaina acikin Filo.
Ko da Assadiq ya gama karyawa ya zo min sallama na yi barci.
Nima zuwan Hauwa'u ya tadani na tashi na iske Amna ta gyara gidan tas yana tashin kamshi.
Kafin Hauwa'u su koma ita ke yi abincin dare saboda su Assadiq, ammh duka duka kwana Hudu suka yi suka tafi.
Ban so tafiyar ta ba ina ta ce ma Assadiq ya roki Tahir ya bar ta su yi ko da sati.
Yana kallona yace"Siya ke fa wani lokacin kina da rigima, mutum da matarsa kuma sai kice ya tafi ya bar miki ita anan?
Da sauri nace"A'a ya zauna shima ya yi sati mana"
Dariya ya fashemin da shi da ya harzukani na juya masa baya.
Ya yi saurin Rumgumeni ta baya yana Fad'in"Tahir fa yana da abubuwan yi Siya, sai ya zo kawai ya tare a wajen mu? Sorry kin ji to ki bari in kin Hauhi sai mu je wajensu mu yi musu wata d'aya tunda baki son Rabuwa da Hauwa'un"
Yadda ya fad'i mganar me yasa nasan zolayata ya ke yi, Bayan hannuna na saka na Tokare masa kirji.
Shi kuma da yaji zafi sai ya matsemin Nono na guda d'aya.
Da naji zafi na make hannunsa ina Fad'in"Assadiq makasata ne fa?.
Yana dariya yace"To ke ma ki rama a nawa makasan mana?
Ya fad'a yana kashemin ido d'aya.
Kallonsa na yi bakina alaikun naja jikina na sauka daga gadon ina fad'in"A'a ba sai na rama ba, na yafe maka Assadiq."
Kokarin tashi ya ke yi ya Biyo ni na zura da gudu ya kira sunana yana fad'in"Siya ki yi a hankali."
Haka muka cigaba gudanar da Rayuwarmu ni da Assadiq cikin rayuwar da muka zab'a ma kanmu.
Ba zan ce ban taba ganin ma'aurata kamar mu ba, ammh dai za'a dade ba'a samu kamar mu ba.
Ba wai bama samun sabani ne bane muna samu, ammh kuma muna kokarin daidaita kanmu.
Tunda musan hallayan junan mu sai muka ci mganin zama tare.
Tausayin junan mu shi ya fara gina zaman aurren mu, sannan daga baya soyayya da kauna suka Biyo baya.
Sannan ni kuma na zauna da shi Cikin Biyayya, Duk abunda na san zai sab'a ma Assadiq ina kauce masa shima duk abunda yasan zai sosa min rai yana kauce ma aikata shi Saboda kada raina ya so su.
Zuwan Amna ya taimakamin sosai ta iya saukakkun girkr girke, Har Assadiq shima mamakin kokarin yarinyar yake yi har ni sai da ya yi min mgana.
Da safe ita zata dafa musu abun karyawa kamar su tea, soya kwai ko doya ko dankali.
Da rana kuma nace ta dafa abunda ta ke so, in kuma wani abu zata sha ko goldemorn ko Cornfl sai ta jika ta sha, da Daddare kuma na kan nuna mata abunda zata yi ko ta Dafa shinkafa jalop ko taliya.
Sai dai ina gefe na toshe hanci watarana na wanye lafiya watarana kuma na yi ta kwarara amai.
Assadiq kan siyo Tuwo watarana da daddare in yaji sha'awan haka.
Wannan watan ganin Amna yasa yace zai je gusau ya Duba Sultana da su Umma nace yakamata.
Ranar jumma'a ya tafi da safe ya barni dagani sai Amna.
Ni fa kwanciya ce aikina kamar wata mai laluran barin jiki.
Wayar ma yanzu in ba kirana aka yi ba, bana bi ta kanta.
Kwana Uku Assadiq ya yi ya dawo ya kawomin Hotunan su Asim da Viedo da ya yi ta daukansu.
Sai suka karamin girma a ido, yace ko damuwa ba su yi sun zama yan gida.
Har Innani sai da tace ya'yan magajin gida sun zo da alheri gidan nan.
D'an zagayen da suke yi a bangarenta tace yana deb'e mata kewa sosai.
Kuma yace da zai tafi ba su yi kuka ba har suna yi masa Bye bye.
Umma na cewa ba za su ku je wajen Mami ba? Suka noke a jikinta.
Ina dariya nace"Shikenan sai mu bar ma su Umma, mu ma zamu haifi namu Allah ya bani yar mace ina so Assadiq."
Yana kallon Wayarsa yace"Allah ya baki, mafi alheri siya."
Na amsa masa da Ameen.
Sai washegari da bai fita aiki ba baya jin dadi zazzabi ya kwana da shi.
Sai nace ya kwanta a gida ya huta sai dai ya kira can wajen aikin su ya gayamusu.
Dani da shi ranar a daki muka yini, muna shan soyayyarmu da Hiran mu.
Muna kwance ya bani wayarsa ina kallon Hotona sai naa ga Ummi an Dauketa ta yi kiba kamar ba ita ba.
Sai na juya ina kallonsa ya na kwance ya Rufe ido ammh ba barci ya ke yi ba.
Tab'osa na yi kafin nace"Na manta ban tambayeka ba ya su sultana da Ummi?
Fata suna lafiya?
Assadiq ya yi shuru kafin can ya mike zaune da sauri yana dariya.
Cikin mamaki nace"Miya faru?
Cikin gyad'a kai yace"Sultana na can na kuka wai na yi sonkai na kara yi miki ciki ita ban yi mata ba."
Ido na zaro ina kallonsa shi kuma sai ya yi dariya kafin ya cigaba da fad'in"Wlh rigimar da naje tarar ta na yi kenan, tace ba na mata adalci ina Fitita ki a kanta, da farko cikin yan Biyu na yi miki ita kuma da ba na kaunarta d'aya na yi mata shine yanzu da son kai da rashin Adalci na yi miki Ciki ita ban yi mata ba to wlh itama bata yarda ba in ina son na zama mai adalci itama na yi mata ciki."
A tare da ni da shi muka Fashe da dariya cikin Dariya nace"Assadiq to kai baka yi adalci ba, me yasa ka dawo ba ka yi mata cikin ba?
Mirmishi ya yi kafin ya koma ya kwanta ya yi filo da hannayensa.
Cikin Tattausan lazafi ya kira sunana"Hasiya."
Na amsa masa sai ya mika Hannun ni kuma na kama ya jawoni jikinsa ya Rumgumeni na yi matashin kaina a saman kirjinsa.
Cikin Sanyin murya yace"Ina so na fad'a miki wata magana."
Cikin ba shi hankalina nace"Ina jinka. Sai ka fad'a"
Kai Tsaye yace"Kin san meyasa na gayamiki wani abu daya danganci sultana game da ni yanzu?
Sai na girgiza masa kai, yana shafa kaina yace"Saboda na nuna miki Sultana bazata taba sauyawa ba. Halinta ne haka zafin kishi zargi da kuma rashin son zaman lafiya, a baya na damu da Fitinarta ammh daga baya da na zauna ma Fahimci halinta har ga Allah lamarinta ya Daina damuna, can u just imaging ta tasani gaba ta na min kuka wai sai na yi mata ciki in ina so na yi adalci.?
Ina yar dariya nace"To sai ka ce mata mene?
Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Me zan ce mata? Tun ta na bani mamaki sai ta dawo bani dariya da Tausayi, yanzu dai na lallasheta nace ta bari itama zan yi mata ciki tunda shi ta ke so"
Mirmishi na yi ban yi mgana ba shi kuma ya Cigaba da fad'in"Shiyasa na ke son na gayamiki ki yi hakuri da ita don Allah kin ji ko? Tunda mun san halinta mu zauna da ita a yadda ta ke"
Ina jinsa sai na gyad'a masa kai ina fad'in"Baka da matsala dani in sha Allahu"
Da bakinsa ya ke fad'amin wasu daga cikin Rigigiman su, wasu na yi ta Dariya sultana yar bala'i ce wlh.
Yace yanzu duk ta b'ata da su Sadiya aammh yasa ta ba su Hakuri.
Yace Har Umma fa in abunta ya tashi sai ta yi mata yaji tace an yi mata gori ko Umma ma nuna son kai.
Yanzu ma zuwan su Asim sai da tace Umma ta yi sonkai.
To itama Ummi zata kawo mata, Umma tace sai ta bari ta yayeta.
Ammh sultana bata ji ba sai ga shi ta had'o kayan Ummi ta kawo ta wajen Umma.
Ina Dariya nace"Kai to wannan jaririyar aka rabata da uwarta ai sai a dauki hakki."
Assadiq yace"Umma tace Shegantakan Sultana ya isheta wlh, sai da Abba ya shiga mganar yana ta lallashi yanzu dai tace itama ta na yayeta Umma zata riketa Tunda ta rike ya'yan kishiyarta."
Yana bani Labarin ina auna wasu abubuwan.