Sashe 15
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Umma ta kalli Saddiqa na waya da megidanta, tana nazarinta sai taga kamar zuwan nata ya sha bambam da zuwan da ta saba yi, daga gani tafiyar tazo ne babu shiri.
Jin kuma tace zata je wajen Surayya da Daren nan, sai gabanta ya fad'i ta fara Tunanin ko wani matsala ne ya faru da Surayyan ba su sani?
Tunda ta kwana Biyu bata leko su ba, Umman ce ma ta kirata shekaranjiya sai taji muryanta wani iri, da ta yi mata mgana sai tace bata jin dadi ne.
Saddiqa ce ta katse ma Umma Tunani da cewa"Umma bari naje, kada na yi dare na rasa abun hawa."
Umma ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa Surayyan ta na lafiya kuwa? naga daga zuwan ki, baki huta ba kuma kin ce zaki tafi gidan Surayya"
Da sauri Saddiqa tace"Lafiya kalau fa, kawai ina so naje akwai mganar da zamu yi ne, kuma ba dadewa zan yi ba kila jibi zan koma."
Kamar Umma zata kara mgana sai kuma ta fasa, sai kawai ta ce "Allah ya kiyaye hanya, ki kwana achan kawai in dare ya yi."
Saddiqa na daukan wayanta da Jakarta na Hannu tace"Zan dawo Umma ai Bamu gaisa da Abba ba."
Ba'a son ran Umma Saddiqa ta tafi ba ta na fita Haraban suka had'u da Mama zata zo shashen Umma suka gaisa itama da tace mata zata je gidan Surayya sai da ta kalleta kafin tace"Da daddaren nan Saddiqa? Allah yasa lafiya"
Saddiqa tace"lafiya lau Mama, bari dai naje ba dad'ewa zan yi ba."
Daga haka suka rabu, adaidaita ta samu zuwa gidan Surayya, Daman sun yi waya dazu da rana lokacin suna hanya ba ta riga ta iso ba.
Surayya na falonta zaune ita da yaranta suna homework sai ga Saddiqa cikin mamaki ta mike ta na fad'in"Saddiqa"
Cikin irin nayi mamakin ganinki a yanzu.
Saddiqa ta samu kujera ta zauna yaran Surraya suna gaisheta, karamar ta dauka saman jikinta Lokaci d'aya ta na fad'in"Ban dad'e da isowa ba, nace sai nazo ina so mu yi mgana, big sis ta na zamu fara kamo bakin zaren wannan maganar nan?
Surayya ta kalli yaranta lokaci d'aya ta na fad'in"ku shiga ciki khalil."
Sai da suka shiga cikin sannan ta mike ta na fad'in"Bari na kawo miki lemu da ruwa."
Saddiqa tace"Bar ruwan nan Big sis, ki zo mu zauna mu yi mgana."
Ba musu surayya ta dawo gefen Saddiqa ta zauna ta na fad'in"Ina jinki Saddiqa, ta ina ki ke ganin zamu fara?
Saddiqa na fuskantar ta lokaci d'aya ta na fad'in"big sis ni a shawarata ta inda aka hau ta nan za'a sauka."
Surayya tace"Kamar ya?
Saddiqa ta gyara zama ta na fad'in" Nufina anan shine Sadiq ne ya jawo komai saboda haka shi sai ya zo ya sanar ma su Umma da bakinsa, in muka Shiga fad'an da babu ruwan mu fa? Kuma abun haushin ma ba da bakinsa ya fad'a mana ba, shi har yanzu bai samu lokacin sanin bai kyauta gamw da abunda ya aikata ba."
Surayya ta yi shuru kafin tace"Ban ki ta mganarki ba, ammh ni a shawarata tunda kin zo, ni da ke zamu tara su Umma mu sanar da su abunda ke faruwa."
Saddiqa ta zaro ido kafin tace"Mu kuma?saboda mene?
Surayya ta gyara zama lokaci d'aya ta na fad'in"Saboda Sadiq kanin mu ne."
Saddiqa ta katsesta da fad'in"Kina so ki nuna min zamu kare Sadiq a wajen su Umma? Zamu karesa big sis ki ke nufi duk a irin abunda ya aikata? Tabdijan wlh in muka yi haka ma gobe sai ya kara ya ma raina mutane wlh"
Saddiqa ta karishe fad'a ta na Nuna bacin ranta kafin ta cigaba da fad'in"kuma suma su Umman ai su gani, tsabar soyayyar da suka nuna ma yaron nan da Abba da Innani, suna Fifita mganar Sadiq a saman ta su, ba dole ya je ya aikata abu mai girma haka bada sanin kowa ba, ya na Tunanin babu abunda zai faru ne shiyasa kika ga ya yi shurunsa ko ajikinsa fa."
Surayya ta yi mirmishi ba ta yi mgana ba, Saboda ta na Tunanin ba lalle in ta yi mgana kowa ya fahimceta ba.
Sanin tsakaninta da Sadiq yanzu sai ace shi ta ke goyama baya.
Tana cikin wannan Tunanin taji Saddiqa na kara fad'in"Nasan dai tsakanin ku da Sadiq akwai kauna, kin fi shakuwa da shi duk da yana namiji, ammh bai kamata ki goyamasa baya ba, tunda duk yadda ku ke bai iya samun ki ya fad'a miki ba."
Surayya ta kara yin mirmishi kafin ta muskuta ta na fad'in"Ke ma kina Tunanin ina Goyon bayan abunda Sadiq ya aikata ne?
Saddiqa tace"Haka ne mana, tunda kina so ya na chan kwance mu mu yi masa yakin a nan."
Surayya tace"Ba shi zamu yi ma yaki ba, Adalci zamu nema ma Hasiya."
Saddiqa ta yi karamin Tsaki kafin tace"Wacece wata Hasiya kuma? Chan ita ta sani, me ya kaita auran wanda bata sani ba?
Surayya tace"Kada ki manta itama ya yi mata karya, in zamu kalli abun ta fuskar adalci itama bai kyauta mata ba. Kuma ni wlh tallahi bazan kare Sadiq ko na minti d'aya a gaban su Umma ba, Hasiya da na yi ma alkwarin komai zai yi daidai ita zan nema ma adalci.
Saddiq sai kawai ta tab'e baki ta na kallon Surayya kafin tace"Ni bangane manufar manganunki ba, yanzu kina so mu je ma su Umma da mganar sannan mu tsaya ma matar da Sadiq d'in ya aura ko me kike nufi?
Surayya tace"A'a abunda na ke so mu yi shine, mu sanar da su Umma saboda su san halin da ake ciki."
Saddiqa tace"To shi me yasa in ya gane ya yi ba daidai ba bai zo ya fad'a da kansa ba? Ko ba shi da baki ne?
Surayya tace"Sadiq na cikin Tsaka mai wuya, ko ni duk yadda mu ke da shi wlh saddiqa ya kasa fad'amin, nan yazo ya zauna ammh ya kasa iya fad'amin komai."
Saddiqa zata yi mgana Surayya ta yi saurin Dafa kafad'arta ta na fad'in"Ki yi hakuri na yi miki alkwarin ko sau daya bazan boye laifin Sadiq ba ammh ni dai ki tayani sanar da su Umma komai."
Saddiqa ta kalleta a kaikace, itama sai ta langwabar da kanta ta na kara fad'in"Ban san ki da haka ba Saddiqa."
Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace"Shikenan domin kin matsa ne, ammh wlh ni naso ki bari sai matar ta Haihu, naga yadda zai kare, yaro karami ammh ya iya raina ma mutane Hankali."
Surayya ta yi dariya ta na fadin"Ba yaro ba ne karami, namiji ne shi kada ki manta."
Saddiqa tace"Hakane yanzu na Tabbatar da haka."
Sun cigaba Tattauna yadda gobe surayya zata zo domin su sanar da su Umma Halin da ake ciki.
Maganar Dauko Hasiya kuma Saddiqa ta ba da shawaran su dakata su yi mgana da su Umma su gani, yadda suka karbi mganar ta yanayin da za su samu mafita kenan.
Surayya ta gyad'a kai alamu gamsuwa kafin tace"To shikenan Allah ya kaimu, ina fatan komai ya daidaita in sha Allahu."
Saddiqa tace"Ammh ki kira yaron nan, mu zamu kwanto masa kuran da ya Daure, sai ya zo ya san yadda zai yi ya sake Daureta."
Surayya ta saka Dariya kafin tace"Zan kirasa ai mganar boye boye kuma ta kare masa."
Sun cigaba da Tattaunawa har Mijin Surayya ya Dawo, shi kanshi da ya ga Saddiqa ya sha mamaki har yana yi mata tsiyan hausanta ya koma na Sokkatawa.
Karfe goma da wani abu Surayya da Mijinta suka dawo da ita gida ba su shiga ba a kofar gida suka sauketa suka rabu akan sai gobe.
Umma sai da ta ga Saddiqa ta dawo ta ga ba wani abu sannan Hankalinta ya kwanta.
Yadda Saddiqa bata ce mata ba, itama bata matsa mata da mgana ba.
Abba ma sai da safe taje ya ganta suka gaisa saboda a daran Mama ke da Turaka kuma dare ya yi shiyasa bata shiga ba ammh tasan tabbas yasan da Labarin zuwanta.
Da safen ma da taje gaishesa sai da ya tambayeta lafiya ko?
Tace masa lafiya Lau tazo ganinsu ne, ta jima a wajensa suna Hira, saboda Abba mutum ne da ke sakewa da ya'yansa.
Daganan sai shashen Mama, itama sun jima suna Hira da ta ga falon wayam ne ba kowa yasa tace"Shikenan gida ya zama tsit, Siyama ta zama yar gidan Sadiq."
Mama na dariya tace"Wlh gida fa ya yi tsit ba kowa, to sai farida ita kuma ta na barayin Innani, in kin ganta anan sai in aikota ta yi Siyama ai sai Sadiq ya dawo ki ke ganinta a gidan nan, in kuma baya nan sai dai su zo tare da sultana."
Saddiqa tace"Itama Allah ya kawo mata miji nagari ta yi auranta."
Mama ta amsa da Amin sun cigaba da Hiran Salima wacce Mama ke fadin yanzu bata zama sosai tunda ta fara karatun nan.
Jin kuma tace zata je wajen Surayya da Daren nan, sai gabanta ya fad'i ta fara Tunanin ko wani matsala ne ya faru da Surayyan ba su sani?
Tunda ta kwana Biyu bata leko su ba, Umman ce ma ta kirata shekaranjiya sai taji muryanta wani iri, da ta yi mata mgana sai tace bata jin dadi ne.
Saddiqa ce ta katse ma Umma Tunani da cewa"Umma bari naje, kada na yi dare na rasa abun hawa."
Umma ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa Surayyan ta na lafiya kuwa? naga daga zuwan ki, baki huta ba kuma kin ce zaki tafi gidan Surayya"
Da sauri Saddiqa tace"Lafiya kalau fa, kawai ina so naje akwai mganar da zamu yi ne, kuma ba dadewa zan yi ba kila jibi zan koma."
Kamar Umma zata kara mgana sai kuma ta fasa, sai kawai ta ce "Allah ya kiyaye hanya, ki kwana achan kawai in dare ya yi."
Saddiqa na daukan wayanta da Jakarta na Hannu tace"Zan dawo Umma ai Bamu gaisa da Abba ba."
Ba'a son ran Umma Saddiqa ta tafi ba ta na fita Haraban suka had'u da Mama zata zo shashen Umma suka gaisa itama da tace mata zata je gidan Surayya sai da ta kalleta kafin tace"Da daddaren nan Saddiqa? Allah yasa lafiya"
Saddiqa tace"lafiya lau Mama, bari dai naje ba dad'ewa zan yi ba."
Daga haka suka rabu, adaidaita ta samu zuwa gidan Surayya, Daman sun yi waya dazu da rana lokacin suna hanya ba ta riga ta iso ba.
Surayya na falonta zaune ita da yaranta suna homework sai ga Saddiqa cikin mamaki ta mike ta na fad'in"Saddiqa"
Cikin irin nayi mamakin ganinki a yanzu.
Saddiqa ta samu kujera ta zauna yaran Surraya suna gaisheta, karamar ta dauka saman jikinta Lokaci d'aya ta na fad'in"Ban dad'e da isowa ba, nace sai nazo ina so mu yi mgana, big sis ta na zamu fara kamo bakin zaren wannan maganar nan?
Surayya ta kalli yaranta lokaci d'aya ta na fad'in"ku shiga ciki khalil."
Sai da suka shiga cikin sannan ta mike ta na fad'in"Bari na kawo miki lemu da ruwa."
Saddiqa tace"Bar ruwan nan Big sis, ki zo mu zauna mu yi mgana."
Ba musu surayya ta dawo gefen Saddiqa ta zauna ta na fad'in"Ina jinki Saddiqa, ta ina ki ke ganin zamu fara?
Saddiqa na fuskantar ta lokaci d'aya ta na fad'in"big sis ni a shawarata ta inda aka hau ta nan za'a sauka."
Surayya tace"Kamar ya?
Saddiqa ta gyara zama ta na fad'in" Nufina anan shine Sadiq ne ya jawo komai saboda haka shi sai ya zo ya sanar ma su Umma da bakinsa, in muka Shiga fad'an da babu ruwan mu fa? Kuma abun haushin ma ba da bakinsa ya fad'a mana ba, shi har yanzu bai samu lokacin sanin bai kyauta gamw da abunda ya aikata ba."
Surayya ta yi shuru kafin tace"Ban ki ta mganarki ba, ammh ni a shawarata tunda kin zo, ni da ke zamu tara su Umma mu sanar da su abunda ke faruwa."
Saddiqa ta zaro ido kafin tace"Mu kuma?saboda mene?
Surayya ta gyara zama lokaci d'aya ta na fad'in"Saboda Sadiq kanin mu ne."
Saddiqa ta katsesta da fad'in"Kina so ki nuna min zamu kare Sadiq a wajen su Umma? Zamu karesa big sis ki ke nufi duk a irin abunda ya aikata? Tabdijan wlh in muka yi haka ma gobe sai ya kara ya ma raina mutane wlh"
Saddiqa ta karishe fad'a ta na Nuna bacin ranta kafin ta cigaba da fad'in"kuma suma su Umman ai su gani, tsabar soyayyar da suka nuna ma yaron nan da Abba da Innani, suna Fifita mganar Sadiq a saman ta su, ba dole ya je ya aikata abu mai girma haka bada sanin kowa ba, ya na Tunanin babu abunda zai faru ne shiyasa kika ga ya yi shurunsa ko ajikinsa fa."
Surayya ta yi mirmishi ba ta yi mgana ba, Saboda ta na Tunanin ba lalle in ta yi mgana kowa ya fahimceta ba.
Sanin tsakaninta da Sadiq yanzu sai ace shi ta ke goyama baya.
Tana cikin wannan Tunanin taji Saddiqa na kara fad'in"Nasan dai tsakanin ku da Sadiq akwai kauna, kin fi shakuwa da shi duk da yana namiji, ammh bai kamata ki goyamasa baya ba, tunda duk yadda ku ke bai iya samun ki ya fad'a miki ba."
Surayya ta kara yin mirmishi kafin ta muskuta ta na fad'in"Ke ma kina Tunanin ina Goyon bayan abunda Sadiq ya aikata ne?
Saddiqa tace"Haka ne mana, tunda kina so ya na chan kwance mu mu yi masa yakin a nan."
Surayya tace"Ba shi zamu yi ma yaki ba, Adalci zamu nema ma Hasiya."
Saddiqa ta yi karamin Tsaki kafin tace"Wacece wata Hasiya kuma? Chan ita ta sani, me ya kaita auran wanda bata sani ba?
Surayya tace"Kada ki manta itama ya yi mata karya, in zamu kalli abun ta fuskar adalci itama bai kyauta mata ba. Kuma ni wlh tallahi bazan kare Sadiq ko na minti d'aya a gaban su Umma ba, Hasiya da na yi ma alkwarin komai zai yi daidai ita zan nema ma adalci.
Saddiq sai kawai ta tab'e baki ta na kallon Surayya kafin tace"Ni bangane manufar manganunki ba, yanzu kina so mu je ma su Umma da mganar sannan mu tsaya ma matar da Sadiq d'in ya aura ko me kike nufi?
Surayya tace"A'a abunda na ke so mu yi shine, mu sanar da su Umma saboda su san halin da ake ciki."
Saddiqa tace"To shi me yasa in ya gane ya yi ba daidai ba bai zo ya fad'a da kansa ba? Ko ba shi da baki ne?
Surayya tace"Sadiq na cikin Tsaka mai wuya, ko ni duk yadda mu ke da shi wlh saddiqa ya kasa fad'amin, nan yazo ya zauna ammh ya kasa iya fad'amin komai."
Saddiqa zata yi mgana Surayya ta yi saurin Dafa kafad'arta ta na fad'in"Ki yi hakuri na yi miki alkwarin ko sau daya bazan boye laifin Sadiq ba ammh ni dai ki tayani sanar da su Umma komai."
Saddiqa ta kalleta a kaikace, itama sai ta langwabar da kanta ta na kara fad'in"Ban san ki da haka ba Saddiqa."
Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace"Shikenan domin kin matsa ne, ammh wlh ni naso ki bari sai matar ta Haihu, naga yadda zai kare, yaro karami ammh ya iya raina ma mutane Hankali."
Surayya ta yi dariya ta na fadin"Ba yaro ba ne karami, namiji ne shi kada ki manta."
Saddiqa tace"Hakane yanzu na Tabbatar da haka."
Sun cigaba Tattauna yadda gobe surayya zata zo domin su sanar da su Umma Halin da ake ciki.
Maganar Dauko Hasiya kuma Saddiqa ta ba da shawaran su dakata su yi mgana da su Umma su gani, yadda suka karbi mganar ta yanayin da za su samu mafita kenan.
Surayya ta gyad'a kai alamu gamsuwa kafin tace"To shikenan Allah ya kaimu, ina fatan komai ya daidaita in sha Allahu."
Saddiqa tace"Ammh ki kira yaron nan, mu zamu kwanto masa kuran da ya Daure, sai ya zo ya san yadda zai yi ya sake Daureta."
Surayya ta saka Dariya kafin tace"Zan kirasa ai mganar boye boye kuma ta kare masa."
Sun cigaba da Tattaunawa har Mijin Surayya ya Dawo, shi kanshi da ya ga Saddiqa ya sha mamaki har yana yi mata tsiyan hausanta ya koma na Sokkatawa.
Karfe goma da wani abu Surayya da Mijinta suka dawo da ita gida ba su shiga ba a kofar gida suka sauketa suka rabu akan sai gobe.
Umma sai da ta ga Saddiqa ta dawo ta ga ba wani abu sannan Hankalinta ya kwanta.
Yadda Saddiqa bata ce mata ba, itama bata matsa mata da mgana ba.
Abba ma sai da safe taje ya ganta suka gaisa saboda a daran Mama ke da Turaka kuma dare ya yi shiyasa bata shiga ba ammh tasan tabbas yasan da Labarin zuwanta.
Da safen ma da taje gaishesa sai da ya tambayeta lafiya ko?
Tace masa lafiya Lau tazo ganinsu ne, ta jima a wajensa suna Hira, saboda Abba mutum ne da ke sakewa da ya'yansa.
Daganan sai shashen Mama, itama sun jima suna Hira da ta ga falon wayam ne ba kowa yasa tace"Shikenan gida ya zama tsit, Siyama ta zama yar gidan Sadiq."
Mama na dariya tace"Wlh gida fa ya yi tsit ba kowa, to sai farida ita kuma ta na barayin Innani, in kin ganta anan sai in aikota ta yi Siyama ai sai Sadiq ya dawo ki ke ganinta a gidan nan, in kuma baya nan sai dai su zo tare da sultana."
Saddiqa tace"Itama Allah ya kawo mata miji nagari ta yi auranta."
Mama ta amsa da Amin sun cigaba da Hiran Salima wacce Mama ke fadin yanzu bata zama sosai tunda ta fara karatun nan.