Sashe 19
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Acikin cikina nake jin motsin da yasa na Dafe cikin ina yar dariya, sai dai wani abu na bani mamaki ni fa ba Motsin abu daya na ke ji acikina ba, sanda naje awo na karshe na yi musu Complain suka kara yi min scanning suka kuma kara samun Tabbacin Rai d'aya ne aciki sai dai likitan yace ya Danganta da koshin lafiyan jaririn Cikina shiyasa na ke jin motsin kamar yafi rai d'aya.
Ni dai na yi shuru ne, ammh har acikin raina nasan abunda ke cikina yafi guda d'aya saboda nauyin da na ke ji, sannan a tare zan ji suna Taushin Cikina ta bangarori da Dama, na yi dai shuru tunda wannan ne na Farko sannan kuma ban isa na san abunda Allah ya Boye a cikina ba, ko su likitocin ai sai abunda Allah ya ba su ikon sani suke iya sanin.
Ina nan zaune sai ga Anty Surayya da Farantin kayan karyawa ta kawomin.
Tace naci na koshi sai na yi wanka na Shirya in mijinta ya fita aiki zamu tafi chan gidan
Cikin Sanyin jiki na amsa mata, alokacin bata ga idanuwana ba sai da ta dawo bayan na gama karyawa sannan ta lura da fuskata, cikin wani yanayi tace"Asiya ba nace ban da koken koken nan ba?
Sai na dukar da kaina kafin nace"Ban yi kuka ba Anty surayya."
Mirmishi ta yi kafin tace"Kin yi min karya , Saboda ai kinsan Fuskarki bata isa ta Boye kukan ki ba."
Nan ta ke na gane kuskurena da sauri na bata hakuri sai ta kalleni kafin tace"Ni baki yi min laifi ba, saboda kinga halin da kike ciki, matsalane wani abu ya sameki a cikin wannan yanayin naki shiyasa kikaji ina ta miki mganar ki saka natsuwa a ranki in sha Allahu alheri ne zai Faru."
Sai na jinjina mata kai, Tiolet ta shiga tace bari ta dauko Botiki Tankinsu ya lalace baya ba da ruwa sai an kira mai gyara.
Da kanta taje ta juyomin ruwan da ta sanya a gas ya tafasa ta kawomin tace na gasa jikina da kyau, ban mata musu ba na tashi na cire kayana na Shiga wanka kuma kamar yadda tace na gasa jikina sosai kuma naji dadi.
Da na fito man zafin nan da ta barmun na kara mulkema jikina Sai naji duk inda jikina ya Rike daga jiya zuwa yau ya sakeni.
Doguwar rigar Abaya na saka mai Ruwan kasa, tunda kayan Atamfofi sun daina shigata saboda kiban da na kara da kuma cikin jikina.
Nagama saka Rigar kenan ina Dauran gyalen kayan a kaina sai ga Anty Surayya ta shigo itama ta yi wankanta tas ta sha kwalliya sai tashin kamshi ta ke yi.
Kafin ma nayi magana ita tafara washe min baki,ta na fadin"Kin gama Shiryawan Asiya?
Da sauri na gyad'a mata kai alamun Eh, sai ta juya ta na fad'in"To dauko Hijabinki ki biyoni falo zaku gaisa da Dr ne."
Ba musu na dauki hijabina dogo wanda ya kaimin har gwiwa fari na saka nabi bayanta zuwa falo, na iske ta zaune ita da Mijinta da alamu ma yana Shirin fita ne.
Kaina na kasa na kariso tunda naji sanda tace"ka ganta dai Dr."
Nayi kokarin na Durkusa sai na kasa na rike baya ina Cije baki da Sauri yace"Ke zauna kan kujera a bunki, ina ke ina Durkushe a wannan Halin da kike ciki."
Jin haka yasa na zauna saman kujera kaina a kasa ina gaisheshi ya amsa Lokaci d'aya ya na kallona sannan ya na Bina da Sannu sannu.
Surayya ya kallah kafin yace"Allah Sarki itama ai yarinyace kamar Sultanan nan."
Surayya tace"Eh ko zata girmeta da kad'an ne, kila ta yi sa'ar salima."
Sai ya jinjina kai kafin kuma ya murmusa yace"Abubakar Sulaiman Shinkafi i like u Staryle, ina son kanin nan naki Surry, Yana da wani irin Confident da Natsuwa tare da Hankali."
Ta na kallonsa tace"Sadiq ne, Abba kan ce karamin su babbansu."
Ya na yar dariya yace"Gaskiya ya fad'a ko ni da na ninka shekarunsa bazan iya yin abunda ya yi ba, in kika Lura ko magana ki ke da shi farat daya zaki Fahimci ya na Tauhidi da kiyayewa Sabon Allah, ga shi he is so kind Mutum ne Simple Straighth Forward. Kai Tsaye zaka ga ya na yin abu ba shayi bakomai ga Tausayi da zuciyar Taimako."
Surayya na jin dadin kyakyawan Hallayar Sadiq da mijinta ke zayyanowa game da kaninta tace"Duk gidanmu ba kamarsa Sadiq na da kyakyawan zuciya."
Dr yace"Sosai fa, kema wani Lokacin kuna kamanceceniyar Hali shiyasa taku tazo daya sannan Namiji ne fa tsayayye, zai iya rike mata Hud'u kuma su zauna lafiya."
Ya dago ya na kallona kafin yace"Ya sunan ki ne?
Kaina na kasa nace"Hasiya!"
Cikin mamaki ya kalli matarsa kafin ya yi mgana ta Rigasa da cewa"Asiya sunanta."
Ina jinsu kamar zan ce ni ba Asiya sunana ba, sai kuma na fasa kada kuma na fara wuce iyakata.
Cikin Yanayin maganarsa daga gani yana da barkwanci yace"Gaskiya kin yi sa'a Asiya, kin yi sa'ar samun Nagarttacen miji irin Sadiq."
Sannan ya kalli Surayya kafin yace"Kudos to Sadiq, zan so mu had'u na sara ma Namiji Uban maza.".
Hararansa ta yi kafin tace"Sai wani kod'asa ka ke yi ban gane ba ne?
Yana yar dariya yace"Kina jinta ko Asiya? Kwantar da hankalin ki in zan kara aure ke zaki fara sani."
Cikin gatsene tace"in ban sani ba ina ruwana Dr? Ba kaina zata zauna ba, ai ta mallam ba ta wuce Ameen"
Dariya ya sska mata ya na fad'in"Eh kaji ta. Allah yasa to da gaske ki ke."
Ya fad'a Lokaci daya ya na jan hancinta ba ita kadai ba har ni sai da na yi dariyan barkwancinsa.
Ta make hannunsa ta na masa Hararan wasa mikewa ya yi ya na Fadin"Asiya na tafi, kada ki damu You are Welcome in to Shinkafi Family da yardan Allah."
Kaina na kasa ban yi mgana ba sai dai na yi mirmishi nace"A dawo lafiya."
Nan suka barni a falo Surayya ta tafi raka mijinta.
Sai da sukaje haraban gidan bakin motarsa Sannan ya kalleta ya na fadin"Gaskiya Surry kada ki bari a wulakanta yarinyar nan, abar Tausayi ne da labarinta da kika bani, kuma ina da Tabbacin shima Sadiq Tausayinta yaji Shiyasa ya yi auran nan ba wanda ya sani."
Surayya tace"Hakane ai da kanta ta fad'a tace taimakonta ya yi saboda mahaifiyarta."
Dr yace"Nasan ta bangaren Abba game din mai sauki ne, Umma ce da Kakarku nasan sai kun yi ta ban baki da Nuniya."
Surayya tace"Kamar ka sani domin tun ajiyan Umma tace bata yarda da wannan auren ba, ko ya saki Asiya ya zauna da Sultana ko kuma ya saki Sultana ya zauna da abunda ya zab'a, innani kuma kasanta Allah da su Allah ya isa jiya ta yi ta makama Magajin gidan nata."
Dr ya jinjina kai yace"Daman ai za'a sha fama, ku dai ku tsaya mata don Allah, Umma ta Duba maraicinta tare da Rabon da ke tsakaninsu Thank god ma, sun yi aure da ta hanyar zina aka samu wannan cikin fa?
Surayya tace"Nima tunanin da na fara yi kenan a farko naji Tsoron Allah ya kamani nace to yanzu inda ba su yi aure ba fa? karfin Rabon da ke Tsskaninsu yasa ya lalace."
Cikin yar damuwa yace"To kin gani, ya kamata dai a duba lamarin cikin Fahimta sosai."
Surayya ta tabbatar masa da cewa in sha Allahu zata iya bakin kokarinta.
Sun yi sallama ya shiga mota ta mika masa jakarsa ya karb'a ya na fadin"Yanzu Zaku tafi chan gidan ne?
Sai ta girgiza kai kafin tace"Anya! Inaga sai anjuma kada mu je ta ga mutane ta kasa sakewa, kila sai Sadiq din ya iso."
Daga haka Suka yi sallama ya tada Mota ta na daga masa hannu sai da megadi ya Bude masa get ya fita Ssnnan itama ta koma cikin gida, Direba ya tafi kai yara makaranta daganan zai kai motar gareji, tana Tunanin ita zata Tukasu ita da Asiya zuwa gida anjuma.
Tana komawa falo ta ga Asiya har ta yi barci nan saman kujera.
Sai ta kara jin Tausayinta a Fili ta Furta baiwar Allah yanzu haka jiya bata samu barci ba.
Sai ta kyaleta ta koma dakinta ta Dauki wayarta sai ta ga Saddiqa ta kirata wajen sau uku bata kusa sai ta bi bayan kiran.
Taji tsoro da taji saddiqa na gayamata labarin ya bazu a kunnen har wad'anda ke nesa, yanzu haka ma Shahida daga katsina ta na hanya, Salima ma an ce ta taho, Subai'atu ke fad'amata ta kirata da Safe tace zata zo gusai itama zata zo ne? Sai ta nuna mata a'a bazata samu zuwa ba tunda sai adaran jiya ne Surayya ta kira Subai'atun ta na gayamata komai da kanta.
Surayya ta rike baki kafin tace"To duk waye ya fad'a musu?
Saddiqa dagachan bangaran tace"Kema kina da son jin magana wazai gayamusu wacce ta wuce mama"
Surayya sai ta kasa mgana, Saboda Daman Mama irin matan nan ne da komai ya faru sai ta kira ya'yanta ta fad'a musu macece dai mai son hira da ya'yanta akan komai..abunda ba Halin Umma ba kenan wani abun ma sai an jima da yinsa su ke sani a bakin yan Dakin Maman.
Saddiq ta katse mata Tunani da cewa"Saliha ce kawai kila bazata zo ba, ammh tun safe su Sakeena da Anty Sa'im suke gidan nan kuma nasan kan mganar ne."
Surayya tace"Allah ya kyauta."
Sai kuma ta kashe wayar saboda abun ne yazo mata a yadda batayi Tunani ba.
Ni dai na yi shuru ne, ammh har acikin raina nasan abunda ke cikina yafi guda d'aya saboda nauyin da na ke ji, sannan a tare zan ji suna Taushin Cikina ta bangarori da Dama, na yi dai shuru tunda wannan ne na Farko sannan kuma ban isa na san abunda Allah ya Boye a cikina ba, ko su likitocin ai sai abunda Allah ya ba su ikon sani suke iya sanin.
Ina nan zaune sai ga Anty Surayya da Farantin kayan karyawa ta kawomin.
Tace naci na koshi sai na yi wanka na Shirya in mijinta ya fita aiki zamu tafi chan gidan
Cikin Sanyin jiki na amsa mata, alokacin bata ga idanuwana ba sai da ta dawo bayan na gama karyawa sannan ta lura da fuskata, cikin wani yanayi tace"Asiya ba nace ban da koken koken nan ba?
Sai na dukar da kaina kafin nace"Ban yi kuka ba Anty surayya."
Mirmishi ta yi kafin tace"Kin yi min karya , Saboda ai kinsan Fuskarki bata isa ta Boye kukan ki ba."
Nan ta ke na gane kuskurena da sauri na bata hakuri sai ta kalleni kafin tace"Ni baki yi min laifi ba, saboda kinga halin da kike ciki, matsalane wani abu ya sameki a cikin wannan yanayin naki shiyasa kikaji ina ta miki mganar ki saka natsuwa a ranki in sha Allahu alheri ne zai Faru."
Sai na jinjina mata kai, Tiolet ta shiga tace bari ta dauko Botiki Tankinsu ya lalace baya ba da ruwa sai an kira mai gyara.
Da kanta taje ta juyomin ruwan da ta sanya a gas ya tafasa ta kawomin tace na gasa jikina da kyau, ban mata musu ba na tashi na cire kayana na Shiga wanka kuma kamar yadda tace na gasa jikina sosai kuma naji dadi.
Da na fito man zafin nan da ta barmun na kara mulkema jikina Sai naji duk inda jikina ya Rike daga jiya zuwa yau ya sakeni.
Doguwar rigar Abaya na saka mai Ruwan kasa, tunda kayan Atamfofi sun daina shigata saboda kiban da na kara da kuma cikin jikina.
Nagama saka Rigar kenan ina Dauran gyalen kayan a kaina sai ga Anty Surayya ta shigo itama ta yi wankanta tas ta sha kwalliya sai tashin kamshi ta ke yi.
Kafin ma nayi magana ita tafara washe min baki,ta na fadin"Kin gama Shiryawan Asiya?
Da sauri na gyad'a mata kai alamun Eh, sai ta juya ta na fad'in"To dauko Hijabinki ki biyoni falo zaku gaisa da Dr ne."
Ba musu na dauki hijabina dogo wanda ya kaimin har gwiwa fari na saka nabi bayanta zuwa falo, na iske ta zaune ita da Mijinta da alamu ma yana Shirin fita ne.
Kaina na kasa na kariso tunda naji sanda tace"ka ganta dai Dr."
Nayi kokarin na Durkusa sai na kasa na rike baya ina Cije baki da Sauri yace"Ke zauna kan kujera a bunki, ina ke ina Durkushe a wannan Halin da kike ciki."
Jin haka yasa na zauna saman kujera kaina a kasa ina gaisheshi ya amsa Lokaci d'aya ya na kallona sannan ya na Bina da Sannu sannu.
Surayya ya kallah kafin yace"Allah Sarki itama ai yarinyace kamar Sultanan nan."
Surayya tace"Eh ko zata girmeta da kad'an ne, kila ta yi sa'ar salima."
Sai ya jinjina kai kafin kuma ya murmusa yace"Abubakar Sulaiman Shinkafi i like u Staryle, ina son kanin nan naki Surry, Yana da wani irin Confident da Natsuwa tare da Hankali."
Ta na kallonsa tace"Sadiq ne, Abba kan ce karamin su babbansu."
Ya na yar dariya yace"Gaskiya ya fad'a ko ni da na ninka shekarunsa bazan iya yin abunda ya yi ba, in kika Lura ko magana ki ke da shi farat daya zaki Fahimci ya na Tauhidi da kiyayewa Sabon Allah, ga shi he is so kind Mutum ne Simple Straighth Forward. Kai Tsaye zaka ga ya na yin abu ba shayi bakomai ga Tausayi da zuciyar Taimako."
Surayya na jin dadin kyakyawan Hallayar Sadiq da mijinta ke zayyanowa game da kaninta tace"Duk gidanmu ba kamarsa Sadiq na da kyakyawan zuciya."
Dr yace"Sosai fa, kema wani Lokacin kuna kamanceceniyar Hali shiyasa taku tazo daya sannan Namiji ne fa tsayayye, zai iya rike mata Hud'u kuma su zauna lafiya."
Ya dago ya na kallona kafin yace"Ya sunan ki ne?
Kaina na kasa nace"Hasiya!"
Cikin mamaki ya kalli matarsa kafin ya yi mgana ta Rigasa da cewa"Asiya sunanta."
Ina jinsu kamar zan ce ni ba Asiya sunana ba, sai kuma na fasa kada kuma na fara wuce iyakata.
Cikin Yanayin maganarsa daga gani yana da barkwanci yace"Gaskiya kin yi sa'a Asiya, kin yi sa'ar samun Nagarttacen miji irin Sadiq."
Sannan ya kalli Surayya kafin yace"Kudos to Sadiq, zan so mu had'u na sara ma Namiji Uban maza.".
Hararansa ta yi kafin tace"Sai wani kod'asa ka ke yi ban gane ba ne?
Yana yar dariya yace"Kina jinta ko Asiya? Kwantar da hankalin ki in zan kara aure ke zaki fara sani."
Cikin gatsene tace"in ban sani ba ina ruwana Dr? Ba kaina zata zauna ba, ai ta mallam ba ta wuce Ameen"
Dariya ya sska mata ya na fad'in"Eh kaji ta. Allah yasa to da gaske ki ke."
Ya fad'a Lokaci daya ya na jan hancinta ba ita kadai ba har ni sai da na yi dariyan barkwancinsa.
Ta make hannunsa ta na masa Hararan wasa mikewa ya yi ya na Fadin"Asiya na tafi, kada ki damu You are Welcome in to Shinkafi Family da yardan Allah."
Kaina na kasa ban yi mgana ba sai dai na yi mirmishi nace"A dawo lafiya."
Nan suka barni a falo Surayya ta tafi raka mijinta.
Sai da sukaje haraban gidan bakin motarsa Sannan ya kalleta ya na fadin"Gaskiya Surry kada ki bari a wulakanta yarinyar nan, abar Tausayi ne da labarinta da kika bani, kuma ina da Tabbacin shima Sadiq Tausayinta yaji Shiyasa ya yi auran nan ba wanda ya sani."
Surayya tace"Hakane ai da kanta ta fad'a tace taimakonta ya yi saboda mahaifiyarta."
Dr yace"Nasan ta bangaren Abba game din mai sauki ne, Umma ce da Kakarku nasan sai kun yi ta ban baki da Nuniya."
Surayya tace"Kamar ka sani domin tun ajiyan Umma tace bata yarda da wannan auren ba, ko ya saki Asiya ya zauna da Sultana ko kuma ya saki Sultana ya zauna da abunda ya zab'a, innani kuma kasanta Allah da su Allah ya isa jiya ta yi ta makama Magajin gidan nata."
Dr ya jinjina kai yace"Daman ai za'a sha fama, ku dai ku tsaya mata don Allah, Umma ta Duba maraicinta tare da Rabon da ke tsakaninsu Thank god ma, sun yi aure da ta hanyar zina aka samu wannan cikin fa?
Surayya tace"Nima tunanin da na fara yi kenan a farko naji Tsoron Allah ya kamani nace to yanzu inda ba su yi aure ba fa? karfin Rabon da ke Tsskaninsu yasa ya lalace."
Cikin yar damuwa yace"To kin gani, ya kamata dai a duba lamarin cikin Fahimta sosai."
Surayya ta tabbatar masa da cewa in sha Allahu zata iya bakin kokarinta.
Sun yi sallama ya shiga mota ta mika masa jakarsa ya karb'a ya na fadin"Yanzu Zaku tafi chan gidan ne?
Sai ta girgiza kai kafin tace"Anya! Inaga sai anjuma kada mu je ta ga mutane ta kasa sakewa, kila sai Sadiq din ya iso."
Daga haka Suka yi sallama ya tada Mota ta na daga masa hannu sai da megadi ya Bude masa get ya fita Ssnnan itama ta koma cikin gida, Direba ya tafi kai yara makaranta daganan zai kai motar gareji, tana Tunanin ita zata Tukasu ita da Asiya zuwa gida anjuma.
Tana komawa falo ta ga Asiya har ta yi barci nan saman kujera.
Sai ta kara jin Tausayinta a Fili ta Furta baiwar Allah yanzu haka jiya bata samu barci ba.
Sai ta kyaleta ta koma dakinta ta Dauki wayarta sai ta ga Saddiqa ta kirata wajen sau uku bata kusa sai ta bi bayan kiran.
Taji tsoro da taji saddiqa na gayamata labarin ya bazu a kunnen har wad'anda ke nesa, yanzu haka ma Shahida daga katsina ta na hanya, Salima ma an ce ta taho, Subai'atu ke fad'amata ta kirata da Safe tace zata zo gusai itama zata zo ne? Sai ta nuna mata a'a bazata samu zuwa ba tunda sai adaran jiya ne Surayya ta kira Subai'atun ta na gayamata komai da kanta.
Surayya ta rike baki kafin tace"To duk waye ya fad'a musu?
Saddiqa dagachan bangaran tace"Kema kina da son jin magana wazai gayamusu wacce ta wuce mama"
Surayya sai ta kasa mgana, Saboda Daman Mama irin matan nan ne da komai ya faru sai ta kira ya'yanta ta fad'a musu macece dai mai son hira da ya'yanta akan komai..abunda ba Halin Umma ba kenan wani abun ma sai an jima da yinsa su ke sani a bakin yan Dakin Maman.
Saddiq ta katse mata Tunani da cewa"Saliha ce kawai kila bazata zo ba, ammh tun safe su Sakeena da Anty Sa'im suke gidan nan kuma nasan kan mganar ne."
Surayya tace"Allah ya kyauta."
Sai kuma ta kashe wayar saboda abun ne yazo mata a yadda batayi Tunani ba.