← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 83

Sashe 17

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Kafin kowa ya samu zarafin mgana sai sai ihu da kurruwan innani suka ji, har ta na wani tuma da kafafunta kamar karamar yarinya.
Cikin kuka ta ke fad'in"Wai daman da gaske kuke yi Magajin gida ya auri wata matar kafin sulsana? Yanzu Amana ta zai ci ya yi ma Jikata kishiya? Magajin gida ina ganinsa mai Hankali ashe maci amana ne, mara Mutumci to billahillazi bai isa ba, ya yi kad'an jikata ta zauna da kishiya ni da Magajin gida baram baram ko ya saki wacce ya aura ya zauna da jikata ita kada'i ko kuma ya sakar min jikata, sannan ya yi ta kansa nima na yi ta kaina.".
Sai kuma ta kara fasa kuka, har da majina ta na kara fadin"Tsakaninmu da wannan yaron sai Allah ya isa."
Lalle lamarin ya lalace tunda innani ke auna ma Sadiq Allah ya isa.
Umma ta yi kokarin danne abunda ke ranta kai tsaye ta kalli Surayya kafin tace"meyasa tunda bai so mu sani ba ku ke sanar damu yanzu? Na dauka Tunda ya yi auransa a boye baya so mu sani ne, sai mu bar shi a haka tunda shi a wajensa haka ya zab'a."
Surayya tace"Umma saboda matar ne, itama ya yi musu karyan ba shi da kowa  iyayensa duk sun rasu."
Mama tace"Shi Sadiq din?
Saddiqa tace"Shi fa, ai Sadiq ya bani mamaki ban taba Tunanin haka daga bangarensa ba."
Mama tace"Ni kaina, ina ta mamakin wannan lamarin, abu kamar almara."
Umma ta had'iye abunda ke ranta kafin tace"Ni banzan ce komai ba, ramar da yaso mu sani zai zo ya fad'a mana da bakinsa"
Daga haka ta mike zata fita, Da Sauri Surayya tace"Umma kunsan matar fa."
Da sauri Umma ta Juyo cikin mamaki kafin tace"Mun santa?
Ta fad'a ta na kallon Mama, itama ta na kallonta.
Cikin karin mamaki Mama tace"To wacece?
Kafin Surayya ta yi mgana Saddiqa tace"Ina kawar saliha da tazo mata Biki daga zariya? Wace tace sun hadu da bikin salima a kaduna yar'uwan mijin salima wata Fara haka.".

Umma da Mama suka yi shuru suna Tunani, nan da nan suka ganeta Tunda ai sun ganta.
Saliha har falon Umma ta kaita suka gaisa, mama kuma a shashenta ta kwana ta gane, kuma kammninta ba shi da bacewa a fuska.
ita Umma ma har a kaduna ta tuna ganin da ta yi mata Lokacin da ta fito neman Innani.
Cikin mamaki Umma ta kalli Surayya kafin tace"Kuma kikace itama ya yi mata karyan ba shi da kowa? A ina ta san nan gidan?
Surayya ta kalli Umma kafin tace"Umma koma ki zauna na yi miki wani karin bayani."

Ba musu ta koma ta zauna, Innani ma ta daina kuka ta na saurara Abba dai ko a fuska bai nuna wani abu ba.
Surayya ta warware ma Umma komai game da zuwanta Zariya..abu daya ta Boye na canfin da ke bibiyar Rayuwar Hasiya.
Sai kuma na auranta Biyu, ta dai ce bazawara ce, Sadiq ya kama mata haya tana zaune a zariya ya na zuwa ya ganta in ya samu Lokaci.
Sannan ta karishe da fadin"Umma ba wai ina so na kare Sadiq ba ne, A'a ina so ku fahimci namu ne mai laifi, itama ya yi mata karya ne ita da yan'uwanta, sannan dalilinsa na auranta wannan sai shi in yazo ya yi bayani, sannan mganar tasan nan gidan tamin Rantsuwa bata sani ba sai daga baya had'uwarta da Saliha a kaduna da kuma Hoton mu da tagani, tace sai da tazo nan ne taga komai, a yadda ta fad'amin ta na ma sadiq mganar ya kamata ya sanar da mu komai ammh sai yace ta bashi Lokaci yana so ya sanar daku ya na da wata matar kafin Sultana."
Mama ta bude baki kafin tace"Bazawara? Shi Sadiq kamar wanda bakin uwa ke binsa?

Innani ta ja hanci kafin tace"Magajin gida yaci Amana, kuma Amana sai taci sa ja'irin mayaudari kawai yazo ya sakarmin jikata domin bazata zauna da tsohuwar kilaki ba."
Surayya da Sauri tace"Innani ba kilali ba ce fa."
Innani na Hararanta tace"To wacece kuma ta yi aure ta fito ai ta zama kilali yar duniya, ina jikata zata iya zaman kishi da ita? Arhin dinsa sai ya saketa kuma naga abunda da zai hanani ci ma Saddiqu mutumci shi da wannan Dogon abokin nasa mai wuya kamar kauren langa Langa."
Da Sauri Umma tace"Ba ruwan Tahir Innani, Abubakar ne bai Daukemu a bakin komai ba, nima ina goyon bayanki, yadda yaci Amanarmu shima sai Allah ya sa anci tasa, yata bazata zauna da shi ba, tunda wanchan ya zaba sai ya cigaba da zama da ita, Sadiq sai ya saki sultana tun kafin Mahaifinta yaji irin cin zarafin da ya yi ma yarinyar nan "

Kawai sai ta fashe da kuka ta mike ta na fadin"Na yarda dashi, ban taba Tunanin zai karya wannan yardan ba,  Wlh tallahi sai dai ya zaba, ammh har acikin raina ban aminta da wannan auren ba."
Ta na gama fad'in haka ta fice Abba na kiranta bata dawo ba, Innani ma ta tashi ta na dingisa sandarta ta shige dakinta itama ta na shan alwashin idonta idon magajin gida sai taci kwalarsa ya sakar mata jika bazata zauna da bazawarar kilakin matarsa ba.
Abba ne kawai da Mama afalon, shi ta kallah kafin tace"Abban Siyama baka ce komai ba?
Sai Abba ya dago kansa yana kallon Surayya kafin yace"Ki aika a dauko yarinyar nan shima Sadiq din ki gaya maasa yazo gida."
Da haka shima ya tashi ya fice, bai bi bayan Innani ba sanim halinta tunda ta Dauki zafi bazata Sauraresa ba.
Mama kuma sai ta gyara zama ta na kallonsu Surayya kafin tace"Ammh tsakami ga Allah Sadiq bai yi wayau ba, bazawara fa? Kodai farin fatarta ne yaja Ra'ayinsa?
Daga Saddiqa har Surayya ba wacce ta kulata ta gama mganganunta itama ta tashi ta fita.
Suma daga nab Shashen Umma suka koma ta shige dakinta ta Rufe, alamun bata son a dameta.
Sai suka zauna anan falon suka yi shuru kowa da abunda ya ke sakawa.
Saddiqa ta kalli surayya kafin tace"Sai ki kirasa ki fad'a masa ko?
Surayya tace"Zan kira sa, ita Hasiya ina tunanin kawai zan ce ta hau motar haya in tazo tasha sai naje na Daukota."
Saddiqa tace"Duk yadda dai ki ka yi, ni nafi son Sadiaq ya ci Ubansa hannun Umma da Abba saboda gaba"
Surayya dai ba ta ce komai ba, ta na wani Tunani Abba bai nuna wani abu ba, Umma ce ta Dauki zafi ita da Innani kuma a irin kalamansu ba su karbi Hasiya ba.
Kwata kwata su Surayya ba su dauka Mama zata gayama ya'yanta abunda ke faruwa ba, ashe ba haka ba ne ta na komawa daki ta fara kiransu a waya  daya bayan daya Sa'ima ta fara kira ta gayamata sannan Saliha da sauran.
Kuma kowa sai ta yi masa kwatancen Hasiya sannan ta kara da fad'in ance ma bazawra ce, kuma Surayya da Sajida sun je har zariyan sun ganta.
Dukkansu mamaki ya kamasu, Mama ko har da kalaman Umma da Innani sai da ta gayamusu sannan tace su zo gida ayi gabansu Tunda Abba yace a zo da yarinya sannan Sadiq ma yazo gida.
Saliha tafi jin mamaki ta jima tana nanata abun, sai alokacin ta Tuna kiran da Surayya ta yi mata, ashe daman dalilin kenan?
Salima ma Sa'ima ta ke gayamata, da kwatancen yar'uwansu mubarak yasa ta gane wacce Anty surayya ta Turo mata Hoton ta ne, ita ta manta da batun ammh jin haka yasa taji ta na son sanin komai.
Ballatana da Mama ta kirata ta na fad'amata tace an ce yar'uwan mijinta ne, sai ta fad'a mata yadda suka yi da Big sis kwanaki.
Nan ta ke Mama tace salima ta yi musu Binciken wacece Hasiya!
Salima kuma na jin haka a daran ta matsa ma Mubarak sai da suka je gidansu, ta samu zahara'u ta tuna mata, itakuma sai da aka had'u wajen cin abinci ta ke yi ma Abba kwatancen Hasiya.
Hajiya Murjanatu na wajen itace ma tace yar wajen marigayi dan'uwansa mamman ne.

Sai ya tuna, kamar ko yasan Salima na son labarin duka nan ta ke ya fara ba su labarin Hasiya da canfinta na mai farar kafa da tunanin da suke yi ita tayi sanadiyar talauta mahaifinta daga karshe ya rasu da aure aurenta da komai sai da ya fad'a ma yaran kuma agaban Salima.
Hajiya murjanatu na ta kifta masa ido ammh ya yi kamar bai gani ba.
Da ya gama yaga ta na yi masa wani kallo sai kawai ya karkace kai kafin yace"To ko karya na fada? Gaskiya dayace fa daga kinta sai bata Murjanatu"
Chapter 17 · 0% Book details