Sashe 61
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Kuma a bangarensa ne abun ya faru Ranar ma Umma na cikin Dakinta kanta ke ciwo ta samu ta sha mgani ta kwanta shine ya jani bangarensa.
Yaso ma na rika zuwa bangaren nasa in yana gari saboda ya rika Samun Abunda ya ke so.
Ni kuma kunya da kuma ganin girman Lamarin a gidan surukai yasa na ki yarda da mganarsa.
Duk iya wattanin da na yi a Gusau sultana na bar miji ta na cin karanta ba Babbaka.
Ban taba nuna Damuwata ba, kuma ko sau d'aya ban taba yi ma Assadiq korafin nagaji ko zan koma Zariya ba.
Kwatsam dawowar nan da ya yi lokacin ina da wata uku a gusau su Asim har sun fara rarrafe har kuma suna kama abu su Tsaya.
Wattaninsu goma kenan suna samun shan madara kuma Umma ta kara sawa mun dage ma basu kunin ne yanzu ko Babansu sai da Nishi ya ke d'agasu.
Gashi har sun fara Haddace kowa na gidan in suka ga Abba ko Assadiq sun rika mika hannu kenan suna gwaranci haka suke yi ma Umma da Mama da farida su wai sun san su.
Ita Umma bata damu da zama na ba, bataki ma na zauna tare da ita ba saboda bata san yin nesa da jikokinta.
Bansan cewa Abba ya kirasa a waya ya yi masa mgamar bai kyauta ba, in a nan zan cigaba da zama nima a nema min muhallin zama na kamar Sultana.
Har da Umma ya yi mganar ita kuma ta nuna masa in ma hakame sai dai na zauna a bangaren Sadiq din tunda ba kowa aciki yanzu, Saboda yara sun saba da nan d'in.
Abba kuma yace a bari mijina ya yanke abunda ya ke ganin yafi masa Sauki.
Ni duk bansan anyi haka ba sai da Asaadiq ya zo washegarin da ya dawo da yammah ya sameni a cikin dakin da nake kwana ina gyara kayan su Asim da aka wanke a kuma goge musu.
Bayan mun gaisa shi da kanshi ya Dauko Labarin abunda ya faru tunda Farko har karshe.
Ya cike da bani Umarnin na Shirya zan koma Zariya na yi parking d'in sauran kaya na kuma yi sallama da yan'uwana Abuja zai tafi dani Gabadaya.
Cikin mamaki na Bud'e ido kafin yace"Ni kuma? Abuja?
Kai Tsaye ya gy'adamin kai, alamun Tabbacin haka sannan da bakinsa ya ke fad'amim Umma taso na zauna a bangarensa saboda su Asim.
Ni dai ban ce komai ba Tunda mgana na Hannunsa bayan ya tafi ne Umma ta kirani har Dakinta itama ta gayamin Bukatar mijina.
Kaina na kasa nace"Umma tunda kina so mu zauna anan din, sai mu zauna shi sai ya tafi da Sultana."
Umma tace"Da ke yace zai tafi Hasiya, ita Sultana yace ta na makaranta. Bakomai fatana kawai ki kula da su Asim sosai."
Sai naji kwalla sun cika Idona cikin Sauri nace"Umma to dukkan mu ya barmu anan mana, ni kaina bana son zuwa ko'ina na barki."
Umma ta yi wani mirmishi kafin tace"Kada ki damu dani, ai ya kawo min Hujjojinsa kuma na gamsu da su kije ki fara shiri yace sai kin koma ta Zariya ko?
Sai na gyad'a mata kai cikin wani yanayi, mun dad'e zaune kowa na tunani acikin ransa kafin ta sallameni na koma dakin da na sauka.
Sai kuma naji bana son Tafiya Allah Sarki bako Rab'a.
Kuma daman ni komawata Zariya yazo min adaidai, Saboda Safiya ta kirani tace an fara Sreening din Result dinmu tun tuni ni ba na nan, sai na tabbatar mata ina nan dawowa in sha Allahu cikin satin da zai shiga.
Sai gashi kafin kace me, mganar komawata Abuja ya shiga kunnuwan duka yan'uwan Sadiq.
Ban sani ba ashe tunda Assadiq ya Furtama Sultana zai tafi dani Abuja ta Buga Tsalle tace bai isa ba sai dai ya Fara tafiya da ita in kuma ba haka ba, bata yarda nima ya tafi dani ba.
Ni bansan ma sun yi haka ba, sai a bakin Anty Surayya na ke ji sanda ta ke maimaita Umma.
Itama Umma ai su sajida sun zo suna ta kananun maganganun bai kamata ta yi shuru ba, a dalci Sultana ce ya kamata ta bi shi Abuja bani ba.
Umma dai ta yi banza da su ta yi kamar bata ji ba, Su kuma suka kara Zuga sultana da idanuwanta ya Rufe ta mamta cewa ita yanzu karatu ta ke yi, a yadda ta nuna ma zata ijiye karatun ta bisa saboda ni kada naje.
Ni dai ban bi ta kan kowa ba na gama duka shirina Tunda yace a wannan Satin in yazo zai maidani Zariya da kansa.
Kuma har ga Allah sai da Tafiyar ta taso ya ke bani Labarin a ma'aikatansu suka ba su Gida da Mota shi dai bai karb'i mota ba, gida kawai ya karb'a duk wata za'a rika Cirewa acikin albashinsa sannan Estate ne kamfanin ya gina musu na ma'aikantan su ne.
Ranar Jumma'a Assadiq ya Dawo bai kuma zo gidan ba sai da Safe gidansa ya sauka.
Sai dai tare da Sultana suka zo, ni ina wanka Umma ta yi ta lekoni su Asim suna wajen Abba daman tun safe Umma ke wankesu tas ta shirya a bunta.
Sannan Tun ina wankan naji ana ta kiran wayata, ina fitowa naga Assadiq ne sai na bi bayan kiranshi tunda mun yi da shi yau Asabar zamu wuce Zariya ya kwana lahadi, litini da Safe ya koma Abuja zai barni sati Biyu na gama da makaramta da sallama da Yan'uwana sannan sai yazo ya Daukeni.
Yana daukan kirana ko gaisuwata bai amsa ba yace na zo bangaren Abba yanzu.
Sai na fara Tunanin Ko lafiya? Ina cikin Tararradin abunda ya Faru na Shirya cikin Wata bakar Abaya na Maryam's Epytian Abaya sai na yi amfani da wani purple din Hijabi.
Ina zuwa sai naga Sultana Fuskar nan nata duk ta jeme saboda kuka sannan ga ciki tunda har ya fito duk Kishi da zargi bai barta ta yi wani kumari ba.
Gefe na zauna a kasa ina gaida Abba su Asim na ganina suka fara zillo ya Sake su yana fadin"Sun ga mamansu zasu gujeni"
Mirmishi kawai nayi ban yi mgana ba, ko da suka zo kusa dani ban dauke su na, Mama ce da ta shigo daga baya ta Dauki Asif, Umma kuma ta Dauki Asim suka rikesu a jikinsu suna musu wasa.
Yaso ma na rika zuwa bangaren nasa in yana gari saboda ya rika Samun Abunda ya ke so.
Ni kuma kunya da kuma ganin girman Lamarin a gidan surukai yasa na ki yarda da mganarsa.
Duk iya wattanin da na yi a Gusau sultana na bar miji ta na cin karanta ba Babbaka.
Ban taba nuna Damuwata ba, kuma ko sau d'aya ban taba yi ma Assadiq korafin nagaji ko zan koma Zariya ba.
Kwatsam dawowar nan da ya yi lokacin ina da wata uku a gusau su Asim har sun fara rarrafe har kuma suna kama abu su Tsaya.
Wattaninsu goma kenan suna samun shan madara kuma Umma ta kara sawa mun dage ma basu kunin ne yanzu ko Babansu sai da Nishi ya ke d'agasu.
Gashi har sun fara Haddace kowa na gidan in suka ga Abba ko Assadiq sun rika mika hannu kenan suna gwaranci haka suke yi ma Umma da Mama da farida su wai sun san su.
Ita Umma bata damu da zama na ba, bataki ma na zauna tare da ita ba saboda bata san yin nesa da jikokinta.
Bansan cewa Abba ya kirasa a waya ya yi masa mgamar bai kyauta ba, in a nan zan cigaba da zama nima a nema min muhallin zama na kamar Sultana.
Har da Umma ya yi mganar ita kuma ta nuna masa in ma hakame sai dai na zauna a bangaren Sadiq din tunda ba kowa aciki yanzu, Saboda yara sun saba da nan d'in.
Abba kuma yace a bari mijina ya yanke abunda ya ke ganin yafi masa Sauki.
Ni duk bansan anyi haka ba sai da Asaadiq ya zo washegarin da ya dawo da yammah ya sameni a cikin dakin da nake kwana ina gyara kayan su Asim da aka wanke a kuma goge musu.
Bayan mun gaisa shi da kanshi ya Dauko Labarin abunda ya faru tunda Farko har karshe.
Ya cike da bani Umarnin na Shirya zan koma Zariya na yi parking d'in sauran kaya na kuma yi sallama da yan'uwana Abuja zai tafi dani Gabadaya.
Cikin mamaki na Bud'e ido kafin yace"Ni kuma? Abuja?
Kai Tsaye ya gy'adamin kai, alamun Tabbacin haka sannan da bakinsa ya ke fad'amim Umma taso na zauna a bangarensa saboda su Asim.
Ni dai ban ce komai ba Tunda mgana na Hannunsa bayan ya tafi ne Umma ta kirani har Dakinta itama ta gayamin Bukatar mijina.
Kaina na kasa nace"Umma tunda kina so mu zauna anan din, sai mu zauna shi sai ya tafi da Sultana."
Umma tace"Da ke yace zai tafi Hasiya, ita Sultana yace ta na makaranta. Bakomai fatana kawai ki kula da su Asim sosai."
Sai naji kwalla sun cika Idona cikin Sauri nace"Umma to dukkan mu ya barmu anan mana, ni kaina bana son zuwa ko'ina na barki."
Umma ta yi wani mirmishi kafin tace"Kada ki damu dani, ai ya kawo min Hujjojinsa kuma na gamsu da su kije ki fara shiri yace sai kin koma ta Zariya ko?
Sai na gyad'a mata kai cikin wani yanayi, mun dad'e zaune kowa na tunani acikin ransa kafin ta sallameni na koma dakin da na sauka.
Sai kuma naji bana son Tafiya Allah Sarki bako Rab'a.
Kuma daman ni komawata Zariya yazo min adaidai, Saboda Safiya ta kirani tace an fara Sreening din Result dinmu tun tuni ni ba na nan, sai na tabbatar mata ina nan dawowa in sha Allahu cikin satin da zai shiga.
Sai gashi kafin kace me, mganar komawata Abuja ya shiga kunnuwan duka yan'uwan Sadiq.
Ban sani ba ashe tunda Assadiq ya Furtama Sultana zai tafi dani Abuja ta Buga Tsalle tace bai isa ba sai dai ya Fara tafiya da ita in kuma ba haka ba, bata yarda nima ya tafi dani ba.
Ni bansan ma sun yi haka ba, sai a bakin Anty Surayya na ke ji sanda ta ke maimaita Umma.
Itama Umma ai su sajida sun zo suna ta kananun maganganun bai kamata ta yi shuru ba, a dalci Sultana ce ya kamata ta bi shi Abuja bani ba.
Umma dai ta yi banza da su ta yi kamar bata ji ba, Su kuma suka kara Zuga sultana da idanuwanta ya Rufe ta mamta cewa ita yanzu karatu ta ke yi, a yadda ta nuna ma zata ijiye karatun ta bisa saboda ni kada naje.
Ni dai ban bi ta kan kowa ba na gama duka shirina Tunda yace a wannan Satin in yazo zai maidani Zariya da kansa.
Kuma har ga Allah sai da Tafiyar ta taso ya ke bani Labarin a ma'aikatansu suka ba su Gida da Mota shi dai bai karb'i mota ba, gida kawai ya karb'a duk wata za'a rika Cirewa acikin albashinsa sannan Estate ne kamfanin ya gina musu na ma'aikantan su ne.
Ranar Jumma'a Assadiq ya Dawo bai kuma zo gidan ba sai da Safe gidansa ya sauka.
Sai dai tare da Sultana suka zo, ni ina wanka Umma ta yi ta lekoni su Asim suna wajen Abba daman tun safe Umma ke wankesu tas ta shirya a bunta.
Sannan Tun ina wankan naji ana ta kiran wayata, ina fitowa naga Assadiq ne sai na bi bayan kiranshi tunda mun yi da shi yau Asabar zamu wuce Zariya ya kwana lahadi, litini da Safe ya koma Abuja zai barni sati Biyu na gama da makaramta da sallama da Yan'uwana sannan sai yazo ya Daukeni.
Yana daukan kirana ko gaisuwata bai amsa ba yace na zo bangaren Abba yanzu.
Sai na fara Tunanin Ko lafiya? Ina cikin Tararradin abunda ya Faru na Shirya cikin Wata bakar Abaya na Maryam's Epytian Abaya sai na yi amfani da wani purple din Hijabi.
Ina zuwa sai naga Sultana Fuskar nan nata duk ta jeme saboda kuka sannan ga ciki tunda har ya fito duk Kishi da zargi bai barta ta yi wani kumari ba.
Gefe na zauna a kasa ina gaida Abba su Asim na ganina suka fara zillo ya Sake su yana fadin"Sun ga mamansu zasu gujeni"
Mirmishi kawai nayi ban yi mgana ba, ko da suka zo kusa dani ban dauke su na, Mama ce da ta shigo daga baya ta Dauki Asif, Umma kuma ta Dauki Asim suka rikesu a jikinsu suna musu wasa.