← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 83

Sashe 14

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Ganin haka yasa Surayya ta Had'e rai kafin ta cigaba da fadin"kuma da ki ke mganar Umma bazata amince ba, daman bukatar shi ne a bi kadin auran a tabbatar da auran na gaskiya ne, bayan wannan ruwan kowa ne ya karb'i Asiya ko kada ya karb'eta ammh baku isa ku sauya wannan mganar na cewa itace Matar Sadiq ta farko, sannan har Abada ita din iyalinsa kinga shaida ma, tunda ga ciki kin gani a jikinta,ni bazan kara miki magiyan ki kama bakin ki ba, ammh ina so ki sani, ita Rayuwa ta na da Fad'i, kila watarana Asiya zata iya miki wani amfani ta fanni da baki zata ba, ko da ki ke ganin kin rainata."
Daga haka ta kama bakinta, ta koma ta na kallon tagar gefenta ta na ganin Dajukam da suke wucewa.
Sajida kuma ko a ranta ba ta ji zata iya Rufe wannan mganar ba, kuma har acikin ranta bata hango Sadiq ya cigaba da zama da wannan yarinyar ba.
Ta na jin Surayya na magana da Saddiqa ta na kara bata tabbacin da gaske ne Hasiya matar Sadiq ne ita ya fara aura a boye kafin ya auri Sultana, Dagachan Bangaren Saddiqa ta na ta salati, Sai dai surayya tace ta bari su koma gida za su tattauna yadda za su tari su Abba da mganar, ammh ko ita tace kada sauran su ji tukunna dai.
Wajen la'asar suka isa Gusai, har gida Surayya suka kai Sajida sannan Suka wuce gidanta.
Daren ranar ta kwana Tunanim mafitan yadda zata kai mganar nan gida ta kasa, wazhegari da Safe sai ga kiran Sadiq bayan ta Dauka sun gaisa bata nuna masa komai ba.
Sai yace zai shigo wannan Satin in ta na Free akwai mganar da za su yi.
Sai Surayya ta zargi ko daman shine maganar da ya kasa fad'a mata?
Sai ya ba ta Tausayi, da Sauri tace"Ina nan Sadiq, wannan wani irin mganace tun yaushe ka ke cewa zamu yita, ka kasa kuma fad'amin? Ina fatan dai lafiya ko?
Dagachan Bangaren Sadiq ya yi shuru kafin yace"Sai dai na zo big sis, ina fatan zaki fahimceni kamar yadda kika saba Fahimtata a baya."
Sai kawai Surayya taji kwalla ta cika Idanuwamta, sai tace ta na tsumayinsa.

Shi kuma a satin Zariya ya kamata yaje, ammh ya riga ya yi kudurin Fad'ama surayya komai a kan Hasiya, sai ya kirata yace ta yi masa Hakuri yaje Gusai kan mganarta.
Ni kaina ya na gayamin ina share kwallah, bazan iya gayamasa ya yi jinkiri ba, ballatana na sanar da shi abunda ya ke so yaje ya fad'a sun san da shi kafin shi ya Furta musu.
Alkwarin da na yi ma Surayya na bazan fad'a masa komai ba yasa na kasa gayamasa komai.
Sai dai ina ta addu'an Allah yasa koma me zai Faru ya zo da sauki.
Sadiq yaje gusai, ammh kana ganinsa wani sukusuku, Sultana duk yadda ta Shiryamasa Tarba ya kasa sakin jiki, kuma har ita kanta bai wani yi mata rawan jiki da ya kan yi in ya zo ba.
A daran jumma'an duk yadda ta so su kad'aice bai biye mata ba, sai yace mata baya jin dadi, washegari kuma da Safe yaje gaida su Umma.
Ita kanta Ta Fahimci ya rage walwala ta tambayesa ko lafiya? Sai yace gajiyan aiki ne.
Abba ma sai da yace ko ya yi ciwo ne?Sai yace a'a, Abba kai Tsaye yace yaga ya rame ne, kuma ya rage walwala.
Sai ya kasa mgana, Daga Shashen Innani gidan Surayya yaje, sai dai duk kokarinsa da mganganun da ya gama Tsarawa ya kasa fad'a ma Surayya su  kuma bayan ita ba shi da wani Sauran Hope.
Zaune kawai ya yi tsuru a gabanta, ya kasa magana ya rasa ta ina ma zai fara, duk abunda ya shirya ganinsa gaban Surayya sai yaji komai kamar an shafe masa daga kwakwalwarsa.
Surayya ta kallesa shuru ta na nazarinsa, kafin tace"Sadiq me ke faruwa ne? Tun dazu ka yi shuru ka kasa mgana?
Sadiq ya runtse ido sannan ya Bude ya kasa had'a ido da ita, cikin jin nauyi da kunya yace"Big sis na rasa ta ina zan fara ne"
Da sauri tace"Ka fara ko ta ina Sadiq, zan fahimce ka."
Ta fad'a ta na fatan ya fad'a mata da bakinsa.
Ammh Sadiq ya kasa, ce mata kawai ya ke yi"Big sis na yi muku Laifi, a lokacin wlh zuciyata ba ta ganin komai sai na taimako, ku yafe min."
Surayya ta kallesa kafin tace"Me ya faru? Ka gayamin don Allah"
A gefe daya kuma daga shi har Hasiya suka bata Tausayi domin ta hango Tsaka mai wuyar da za su shiga.
Ammh abun Takaici Sadiq tafiya ya yi, batare da iya gayama Surayya komai ba, ya dai ce kawai yaci amanarsu su yafe masa.
Kasa fad'a mata ya yi, yace zai dawo gobe ya na tafiya sai ga  wayar Saddiqa, Surayya ta karanta mata yadda suka yi da Sadiq.
Saddiq tace"Wayyo Sadiq ya shiga Tsaka mai wuya, ni kaina ina fatan su Umma su Fahimcesa."
Surayya ta so ta kara Turke Sadiq in ya gayamata sai ta gayamasa komai ta kuma nuna masa kuskurensa ta yi masa adalci bisa gayamata da ya yi.
Ammh sai me? Ta yi ta kiran wayarsa bata samu sai ta kira Sultana, ita ke gayamata ya tafi zariya yau da safe dagachan zai wuce Abuja.
Surayya ta sauke numfashi, Sadiq me yasa ya ke haka ne?
Wannan fa gudun nasa ba mafita ba ne.
A ranar ta gama yanke shawaran abunda zata yi, ya kamata zuwa yanzu su Umma su san abunda ke faruwa.
Ba sai na nesa sun zo ba, ko da iya na kusa ne sun wadatar, Saddiq ta kira suka yi mgana, ta tabbatar mata da zuwa Jibi zata zo sai su taru su sanar da ma su Umma komai cikin Rukuni. Ba ta yi ta kan Sajida ba
ta lura so ta ke yi ta b'ata al'amarin to gwara tun kafin ta bata lamarin ita ta warware komai.
Sun rabu da Saddiqa akan Surayya zata Tura ma Hasiya Direba gobe ko jibin ya kawota gidanta ta kwana ranar Laraba da zasu taru sai ta taho da ita hakan zai fi sauki.

Bata kirani a ranar ba sai Ranar Litini da safe, lokacin ina makaranta Assadiq ya saukeni ya wuce Abuja.
A yadda ya zo min na yarda cewa yan'uwansa ba su fasa mganar ba.
Ammh mun rabu bayan ya tabbatar min da cikin Satin nan zai fad'ama Ahalinsa komai game da ni.
Bayan mun gaisa kai Tsaye surayya tace"Sadiq ya tafi ko ya na nan?
Cikin jin nauyi nace"Dazu da safe ya wuce."
Sai tace"Ki shirya zuwa gobe zan aiko Direba zai taho da ke wajena, ki shirya kayanki kamar kala uuku haka"
Cikin wani yanayi nace"Ba matsala ko Anty Surayya?
Da sauri tace"In sha Allahu, zan kira ki in zai taho."
Daga haka muka rabu, a cikin raina sai nake jin wani Tsoro.
Tsoron abunda zan je na tarar, abu biyu ne ko su aminta dani ma zauna cikin Tozarci ko kuma su rab'a ni da Assadiq sun yi min koran wulakanci.
In hakan ko ya faru na lalace domim bansan kuma wani mafita zan kama ba.

*Janafty*
*TMWBK3005*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk

Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haɗin mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan.

Washegarin Talata Saddiqa ta baro Kebbi zuwa Gusau, kuma ita kad'ai tazo ba tare da yara ba tace saboda makaranta sai ta barsu a gida tare da Babansu.
Zuwan bazata tayi, tunda ko Umma sai dai ta ganta kwatsam gashi motar haya ta shigo ta sha wuya, ammh abun mamaki ta na isowa sallolin da suka Subuce mata ta fara rankawa kafin ta ci abinci.
Ta na gama cin abincin sallar mangariba tayi, tace ma Umma zata je gidan Surayyah abun sai ya ba ma Umma mamaki, ganin ko hutawa ba tayi ba, kuma tace zata fita.
Taga kuma ko shashen Mama bata je ba, ta dai Leka shashen innani sun gaisa gashi ma Abba bai dawo ba.
Chapter 14 · 0% Book details