← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 83

Sashe 29

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sai dare muka yi mgana da Assadiq yace sun sauka lafiya shima gobe zai koma Abuja Saboda aiki.
Anty Surayya ma ta kirani ta na min bangajiya.
Ranar na yi barci harda makara, wayar Safiya ce ta tadani ma, ta na gayamin an kafa mana Time table zamu fara jarabawar Secomd Semister shine ta ke cemin ta Turamin na duba nagani.
Tashi na kenan ruwan zafi kawai na Dafa nasha Tea sai ga Ramatu tazo.
Naji dadin zuwanta ita ta yi min share share ta dafa mana abincin rana.
Sai bayan mun zauna mun natsa ne na bata Labarin duk abunda ya Faru har na zuwana Gusai da dawowar da su Abba suka yi dani jiya.
Ramatu ta jinjina kai kafin tace"Ni fa daman na yi ta tunanin Mijin ki yafi karfin inda ya saka kanshi, kuma har Nura ya tabamin maganar jikinsa bai nuna Daga kauye ya ke ba."
Cikin gyad'a kai nace"Ni ina na Fahimta na Dauka, duk abunda ya Fadamin gaskiya ne. Sannan bai taba nuna min abunda zan gane wani abu ba"
Ramatu tace"Ammh gaskiya na yi mamaki, sai fa kin yi hakuri kin kuma Dage da addu'a domin kinsan in mata suka yi yawa a gida sai a hankali, fatana dai Allah yasa maman nasa ta yarda ta karbeki."
Na amsa mata da Ameen ina bata Labarin yadda Assadiq ya tsayamin a gaban yan'uwantsa
Ramatu tace"Kaji namijin gaskiya da gaske ya ke yi yana sonki Hasiya."
Ta dade sai la'asar ta tafi bayan mun sha Hira ta yi ta bani Shawaran na kwantar da Hankalina kada na saka Damuwa araina.
Tazo a jiya washegari yau Adda Fati tazo itama yadda na gayama Ramatun haka na maida mata.
Ita kam ta na ta jinjina abun har da zuwan mu gidan Baba Tanko ina fad'amata yadda Baba Tanko ya yi min.
Cikin yar dariya tace"Bai taba Tunanin zaki samu miji kamarsa ba ne, lalle wani aikin sai Ubangiji. allah ya huci zuciyar maman tasa ya Daidaita tsakanin ku gabadaya."
Itama Addu'an tace na Cigaba da yi, kuma tace na kira Amma na yi mganar da ita.
Haka ko akayi a daran na kira Amma na gayamata komai.
Mirmishi kawai ta yi kafin tace"Allah ya kauda Fitina Hasiya, ammh in sha Allahu  ina ji ajikina Asssadiq ne mijinki har mutuwarki."
Acikin raina sai na samu kaina da amsawa da Ameen Ameen.

Itama dai tace min na yi addu'a sannan kada na shiga damuwa Saboda abunda ke tare dani.
Haka na cigaba da kula da kaina Gefe daya Assadiq na kula dani Tunda koda yauahe muna tare a waya.
Tuni mun fara jarabawa hakanan na dage da karatu ba wasa tunda muna gama Jarabawar Nce3 first Semister zamu tafi Tp ne, ina ta Tunanin yadda zan yi Tunda a lissafina na haihu a lokacin.
Anty Surayya ma ta na kira na muna gaisawa, Har Saliha ta kirani mun jima muna mgana da ita, itama ba ta nuna min kyama na ta kuma saka ma lamarin albarka.
Ban kuma karajin yadda suka kare ba, ko shi bai yi min mganar ba.
Ballatana nasan matsayan Umma da kuma ita kanta Sultana.
Shiyasa  nima sai ban yi masa mgana ba abunda ba'a so kaji gwara ka yi shuru da bakin ka kada ka zake kuma da yawa."

********

Baba Tanko da kansa ya kira Alhaji Jibril yana fad'a masa zuwan Alhaji Sulaimam da mganar auren d'ansa da Hasiya.
Ya ji mamaki kai Tsaye ya kira Abba yana tambayansa ko gaskiya ne abunda yaji ?shi kuma yace masa hakane.
Har Abba ya na masa Tsiyan cewa sun had'a zumunci ta bangare biyu.
Alhaji Jibril cikin bakin ciki yace"Alhaji ka kosan labarin yarinyar nan? Ko baka san cewa ta na da bakin jini a tare da ita ba, duk wanda ya aureta ko mutuwa ko rasa lafiya ko Dukiya."
Abba ya yi mirmishi kafin yace"Duk na san da wannan."
Alhaji jibril yacce cikin mamaki"Kuma ka amince da auran Danka da ita?
In wani abu ya same shi fa? Ga shi shi kad'ai gareka namiji."
Abba ya kateshi da Fadin"Babu abunda zai Faru face abunda Allah ya Rubuta mana, kada wannan ya Dameka Alhaji."
Da haka ya kashe bakinsa har suka gama wayarsu Alhaji Jibril ba shi da wata fara'a a yanayinsa.
Har Mubarak sai da ya Turke yana Tambayansa yace shi bai sani ba Salima bata gayamasa ba, yasan dai taje kaduna Saboda ya kara samun Tabbaci yace Mubark yazo da salima gidan.
Bayan sun zo ya zaunar da ita yana mata Bin diggi, ita kuma ta fayyace masa duk abunda ya faru, har ta fadin"Babu wanda ya yarda da auran nan Daddy,  Umma ma tace sai ya zaba ko sultana ko ita wannan Asiyar"
Alhaji Jibril yace"Uhm Ina tsoron abun da zai Faru da Abubakar ne."
Shi har acikin ransa bai yarda da babu Canfi ba
Billhaki da gaskiya shi yana Tsoron kada wani abu ya  faru da Abubakar Alhaji yazo sanadin abun ya rusa shi.
Shi ai da ya shiga uku domin ya fara hango ma kansa abunda ya Dad'e yana Buri.

*Janafty*
*TMWB3K09*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65

Muna cikin jarabawa aka shiga watan azumin Ramadana, ni dai ina ta lallaba Rayuwata tunda yanzu na riga na zama kaya, ina matukar shan wahala na jeka ka dawo saboda makaranta Allah yasa ma ba kullum na ke gwada azumin ba, na fi yi in ina gida shima ba kullum ba, kuma a boye in Assadiq yaji sai ya kama min Fad'an nasan halin da ni ke ciki sai kuma na matsama kaina?
Alhalin Addini ya riga ya saukaka mana.
Assadiq har cewa ya yi ko na hakura da Jarabawar bayan na haihu jariri ya yi kwari sai na koma daga baya sai na yi Difaring ni kuma naga duk wata Sabuwar Wahalace nace ya barshi zan rika kokartawa.

Hakanan na ke zuwa da Katon ciki gaba ina tafiya a tale kamar wata yar kaciya, aikin gidana kam tuni na yaye shi sai in Habiba tazo ne ta kan taimakamin Tunda cikina yana cikin Watannin fitowarsa Duniya ne.
Assadiq duk bayan sati biyu ya ke zuwa ya ganni, in kuma yana wajen aiki ko da yaushe muna tare da juna ta waya.
Ba abunda zan ce ma Anty Surayya sai Godiya domin ta nuna min dukkan kauna, ita ta yi masa maganar Kudin kayan jariri ya ba kuma bata ta sDiyamin komai har da kayan da zan yi Fitan suna dashi.
Kuma sai da ta turomin kayan na zaba duk da kuma nace basai ta yi hakan ba, zata kirani bayan kwana Biyu taji lafiyata ita ta kara karfafan gwiwan ma kada nace zan zauna a gida na cigaba da zuwa makaranta na Saboda hakan zai taimakamin na samu sauki wajen Haihuwa.
Amma na lissafe da wattanin Cikina ta kuma bani tabbacin Adda zata zo ta zauna dani, Da ya ke ma Addan na ta fama da Ciwo yanzu Amma ita kuma sai ta yi lafiya.
Da watan azumin nan babu abunda Assadiq bai ijemin na kayan abinci ba, sai ma ina kyauta da shi kuma sai da na tambayeshi ya bani izini.
Na dibarma Adda Fati kayan abinci har maman suhailat na ba ta, ta na Godiya Ummi dai ban bata ba, tunda Tuni huld'a a tsakanin mu ta jima da yankewa sai dayan matar ne na ba ma wa kawai.
Sannan na Diba nace Habiba ta kai samaru dogon gida wajen maman boy, tunda yace a yi sadaka ga mabukata ne.
Da ya ke ba su yadani ba Lokaci bayan Lokaci suna kawo min ziyara ne, ni ce ma dai sau daya na taba zuwa anguwan tun bayan aurena da komawar Amma gadan mallam mamman.
Bamu muka gama jarabawa ba sai da aka shiga goman karshe na watan azumin Ramadan, Assadiq yazo sau biyu ya dubani ya kuma yi min Weekend, sai dai abun da ke bani mamaki ya rage zuwa Gusai Kamar baya ina tsoron kada ace saboda ni Umma ta raba shi da matarsa.
Ina so na tambayesa ammh kuma wata zuciyar na hanani ganin kamar ba Hurumina ba ne, kada kuma yaga na tsallako abunda bai shafeni ba.
Hatta kayan Sallar da zan yi fitar Idi da shi yace yana Gusai Big sis duk ta karba kudi ni da Sultana tace zata siyamana.
Jin ya ambaci sunan Sultana sai na samu salama araina nace suna tare kenan har yanzu, na manta ko basa tare kanwa take a garesa zai iya yi mata komai da yaya ke yiwa kannensa.
Salla saura kwana uku Assadiq ya kirani yace gobe yana tafe na shirya tare zamu wuce gusai chan zamu yi sallah.
Duk da har acikin Raina ban so hakan ba , sai dai ban iya ce masa komai ba da yaga na damu sai ya fara lallashina yana nuna min kada na damu yan'uwansa ne ya zama Dole mu'amala ta irin wannan salla ko wata Hidima ta rika had'amu ta hakane har watarana zamu samu Fahimtar juna.
Chapter 29 · 0% Book details