← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 83

Sashe 34

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Ko karyawa bai tsaya ya yi ba wajen Goma na safe ya Juya ransa bace shi kam Abba lamarin ya yi masa daidai.
Innani kuwa kamar an tsaface bakinta bata yi mgana ba sai dai Mallam Shitu ya sha tabe baki da Harara ta zata zai sako sunanta ne ta yi masa wankan Tsarki duk dai tace ta yafe ammh dai duk da haka dai, sai kuma aka yi sa'a bai sako sunanta ba to ina zai sakota Tunda yasan Halinta.
Sultana kuwa bayan tafiyar mahaifinta ta kalli Umma lokaci d'aya ta na fadin cikin kuka"Umma yanzu sai na koma?
Umma ta kalleta ita tsabar takaicin da ta ke ciki ya hanata mgana, ta na ganin Sultana na gunjin kuka ammh ta kasa ce mata ci kanki ballatana ta iya lallashinta
Tafiyarsa ko awa daya ba'a yi ba sai ga Maallam zakari d'aya daga cikin jikokinsa ya rakosa.
Tunda Abba ya kira Umma a waya ya gayamata zuwan mahaifinta nata gabanta ya fad'i saboda tasan halin Mahaifin na su yana da zafi, shifa ba ruwansa komai girman ki kika aikata ba daidai ba gaban ya'yanki zai yi miki Kaca kaca bai damu ba.
Shiyasa tunda Umma taji Labarin zuwansa jikinta ya yi sanyi sannan a gefe daya kuma na zuciyarta ta kara Kullatan Sadiq wato itama bai barta haka ba sai da ya had'ota da mahaifinta lalle zai gane ba shi da wayau in suka had'u.

Shima a bangaren Innani ya sauka daman ta so tazo d'aya da Innani, itama sosai take jin dadin Hira da shi, mutun ne mai fara'a da barkwanci gashi yana Biye ma duk abunda Innani ta zo da shi baya kusheta Shiyasa da ta gansa ta rasa ina zata sakashi Saboda Murna.
Kamar an bude famfo haka ta shiga labarta masa abunda ya kawosa, har da sauran Labaran da bai sani ba na game da Hasiya.
Kai Tsaye mallam Zakari ya kalli Innani kafin yace"Naga matar jiya tare da ita ya biya wajena, yace Zariya zai kwana yau tun safe zai kama hanyar Abuja"
Sai Innani ta rike baki ta kasa mgana, Shigowar Umma da Abba ya hanata wata mgana.
Umma ta duka zata gaishe shi ya daga mata hannu da sauri yana fadin"mike kawai abunki salamatu yau bazan karbi gaisuwarki ba, sai kin gayamin babban Dalilin ki na kin sakama auran da Abubakar ya yi albarka? Ke shad'aniya ce da ki ke ja da Hukuncin Ubangiji salamatu.?
Yadda ya ke fad'an ne yasa Umma durkushewa a gabansa cikin rawan murya tace"Baba ka tsaya ka Saurareni."
Cikin daga murya yace"To ina sauraranki, fad'i abunda ke bakin ki."
Gatse ya yi mata ammh bata gane ba cikin Rawan baki ta fara fad'in"Baba yaron nan fa aure yaje ya yi a Boye bamu sani ba?
Kai Tsaye yace"Shine mene?
Kallonsa ta yi cikin mamaki bakinta na Furta"Baba.!
"Nace shine menene don ya yi aure baki sani ba, sai daga baya kika sani?
Sai Umma ta maida kanta kasa ta riga daman tasan mahaifin nata bayan Sadiq zai bi.
Chapter 34 · 0% Book details