← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 83

Sashe 18

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Salima kuwa suma komawa gida ta kira Mama ta kwashe komai ta fad'a mata, ita kuma duk a daram ta kira yaranta ta fesa musu, suna ta faman Tattauna lamarin yan kusa sun ce gobe suna nan zuwa ayi komai a gabansu.
Ita kuma Hasiya Surayya ta kirata tace in da kudi a hannunta ta shirya ta hayo motar haya in zata iya.
Tace mata zata iya.
A ranar na baro zariya na zo gusai, gwara kawai nazo ayi wacce za'ayi, a tasha Surayya ta zo ta Daukeni zuwa gidanta ta bani daki kuma ta karraamani.
Ta kuma zaunar dani tamin bayanin komai da ya faru yau da safe, ammh bata fad'amin furucin Umma da Innani ba.
Tadai ce Abba yace na zo sannan Sadiq ma a kirashi.
Ta bar ni a dakin da ta saukeni ta fita falo da niyar kiran sadiq.
Sai taga ya kirata ma wajen sau Hudu. Ta na kokarin bin bayan kiran ne sai ga shi ya sake kira.
Sai da ta dauka suka gaisa, ta yi shuru shi kuma dagachan bangaran yace"Big sis mganar nan da na yi ta cewa ina so mu yi, shine yanzu na ke so in ba wani abu kike yi ba mu yi mganar"
Kawai sai tace"ka makara Sadiq na riga nasan  mganar"
Cikin firgici yace"Kin sani?
Mirmishi ta yi kafin tace"Ba na kayi aure a zariya ba? Sunan matar taka Hasiya kuma ma yanzu ta na da ciki ko?
Ai sai Sadiq yaji kamar a cikin kankara ya sandare a zaune.
Yana kwaso in'inan mgana Surayya ta katseshi da fad'in"Umma da Abba da Mama hadda Innani suma sun sani, Sadiq gobe kome ka ke yi ka barshi ka taho gida, in kuma ka ki zuwa ina mai tabbatar maka komai zai lalace."
Cikin rawan baki da na zuciya Sadiq yace"In sha Allahu zan taho da Sassafe.'
Daga haka ta katse wayarta, ta na Tunanin abunda zai iya faruwa a goben.

Abunda bata sani ba suna gama waya ya kira Hasiya, ta dauka kuma Daman Surraya tace kada na bari yasan ina Gusai.
Cikin tashin hankali ya ke gayamin yadda suka yi da surayya sai naji ya bani Tausayi, barin ma da ya ke cewa"Gobe zan tafi gusai siya, ki tayani da addu'a Umma da Abba su Fahimceni, ina son ki har abada ba na fatan Rabuwa da ke. Ki zama cikin shiri akwai yuyuwar ki taho gusai in bukatar hakan ya taso."
Ya yi ta kokarin ya nuna min kada na Damu in sha Allahu bakomai.
Shi tunaninsa daya ina suka san da wannan labarin? Duk da na sani ammh na kasa iya gayamasa yadda abun ya fara ba.
Muna waya ina sharan kwalla, na yi ma kaina alkwarin zan yi duk abunda Assadiq ya ke so, tunda wannan Halin Tsaka mai wuyar da ya ke ciki ba saboda kowa ya shiga ba sai saboda ni.

*Janafty*
*TMWBK3006*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65

Daren ya kasance mai tsawo a gareni, na kasa barci sai faman juye juye na ke yi, ga ciwon kai sannan ga cikina ya karamin nauyi.
Domin na sha wahala a motar da na shigo zuwa gusau.
Duk yadda Surayya ta rika lallashina da nacin na huta kada na damu babu abunda zai faru, sai naji na kasa jikina ya yi sanyi gabadaya gabbaina sun saki, in na kalli cikin jikina sai naji Rauni ya Rufeni, ba na so abunda muka aikata ya shafi d'an da ke Cikin mu, sannan gefe d'aya ina jin Matukar Tausayin Assadiq duk abunda ya faru ko zai faru saboda ni ce.

Da naga na kasa barci sai na rarrafa na tashi ina jan kafa na fad'a Tiolet din dake cikin dakin na Dauro alwala nazo na daidaici in da Anty Surayya tace min gabas ne na tada salla.
Dakyar na iya yin raka'a hud'u ina tsaye, da naji nagaji sai na koma na zauna saboda girman cikina kamar ana hurashi sai kuma ya koma kasan marata ya yi tulu kamar wacce ta shiga watan haihuwarta, alhalin kuma wattanin cikin wata bakwai ne.
Na yi addu'a sosai acikin daran nan da Fatan duk abunda zai Faru gobe kada ya zama mai Tsauri ga Rayuwata sannan kada ya zama mai kuntata ga Assadiq.
Sai wajen uku na dare na yi barci, kuma kiran sallar asuba a kunnina Tunda daren ne gabadaya ya yi min Tsawon da na kasa samun natsuwa ballatana na iya yin cikakken barci.
Ko da Surayya ta shigo ta tasheni sai ta iskeni ina salla a zaune, tunda da asuba da jan kafa na iya shiga bayi, kafafuna daman tun jiya suka kara Kumbura saboda zaman mota, sannan ga sallar da na yi a zaune da safen sai suka kara hayewa dakyar na ke tafiya.
Sai bayan na idar da sallah ta dawo mu ka gaisa cikin sakewa da Fara'arta kamar yadda na Fahimceta macece mai girmama Dan adam kamar irin Assadiq dina.
Ganin yadda na mike kafafun ne yasa ta kalli kafafun sannan ta koma ta na kallon Farar Fuskata lokaci d'aya ta na fadin"Sannu naga kafar ta tasa ne"
Mirmishi nayi ban yi mgana ba saboda jin nauyi sai itace ta cigaba da fadan"Allah yasa kada wannan yar mganan da za'ayi yau ya taso da naguda fa"
Ta karishe fad'a cikin sigar Zolaya, sai na kalleta kafin nace"Ban kai ga watan haihuwata ba, cikina wata bakwai ne fa."
Sai ta zaro ido ta na kara kallona kafin tace"Wata bakwai fa kikace Asiya.?
Sai na gyad'a mata kai alamun hakane cikin mamaki tace"Ikon Allah gaskiya kina da girman ciki ni da Randami, ni wlh na dauka cikin ya shiga wata na Tara ne"
Sai kawai na sunkuyar da kaina cikin Sanyin murya nace"Haka kowa ke tunani, ana ta mamakin girman cikina shiyasa nake jin nauyinsa a jikina da kafafuna."
Cikin Tausayawa Surayya tace"Sannu dole zaki ji kam, bari na samo miki man zafi ki shafa. Ya samu su sauka kafin mu tafi chan gidan."

Da Toh na amsa mata sai ta tashi ta fita ba jimawa sai gashi ta dawo ita da yaranta ta saka su, suka gaisheni na amsa ina tambayan sunayensu.
Namijine ke ma uwar rad'a sai tayi dariya kafin ta kalleni ta na fad'in"Matar Uncle din ku ce Sadiq, sunanta Asiya."
Sai ya waro ido kafin yace"Mommy ita Anty Sultanan fa?
Batare da wata Damuwa ba tace"Dukkansu  matansa ne Khalil"
Zai kara mgana ta dakatar dashi da cewa su je su yi shirin makaranta.
Sai da suka fice ne sannan ta duka ta na fadin"Bari na taimaka miki."
Ita ta shafemin kafafuna da man zafin nan, tace zuwa anjuma zai saki yadda bazai takurani ba.
Ina tayi mata godiya kamar na yi kwallah ganin yadda ta karbeni batare da ta kyamaceni ba.
Kafad'ata ta dafa cikin sigar lallashi ta na fad'in"Kada ki damu Asiya, ni a wajena da ke da Sultana duk d'aya ne Sadiq dai shine kanina duk da itama Sultanan kanwata ce, ammh a Ture wannan bangaran kuna da tudun matsayin matan kannena ne, kuma nice Babba a gidanmu in ban zama mai gyara ba, bazan so na zama mai barna ba kuma Dan adam ai ya na da Daraja bai kamata wani mutum ya kasance mai dariya ko wulakanta kaddaran wani wanda ba shi ya yi kansa ba."
Har ta fice ina jin kalamanta a raina sannan a gefe d'aya ina kara jin na samu natsuwa a cikin raina.
Kuma man zafin da ta shafamin naji dadinsa sosai, Assadiq ke raina shi na kira ammh sai wayarsa bata shiga ina da kyakyawan zato kila ya taso ya na kan hanya ne.
Adda Fati na kira, a raina nace gwara na fara fad'a mata kada Lamarin ya Rikice na koma da wani Labari wanda su ba su san dashi ba.
Da ta dauki wayata sai da tace min"Lafiya Hasiya?
Saboda taga kiran wayata da Sassafe, cikin Boye yanayina nace"Lafiya lau Adda Fati ya yara?
Ta amsa min Lokaci d'aya ta na tambayata ya nauyin jiki nace mata da Sauki sai tabini da addu'an Allah yasa na sauke lafiya acikin raina na amsa mata da Ameen.
Shuru muka yi na wani Lokaci ita kuma sai ta Fahimci akwai mgana a bakina cikin Wani yanayi tace"Hasiya..! Menene ke faruwa ne?
Cikin karfin hali nace"Adda ina gusau fa Tun jiya."
Cikin mamaki Adda Fati Dagachan bangaren tace"Gusai kuma?
Ta fad'a cikin Sigar Tambaya.
Cikin gyad'a mata kai kamar ta na ganina nace"Eh Adda, ina Gusai yanzu haka ina gidan yayar Assadiq a nan na kwama ma"
Cikin wani karin mamakin Adda Fati tace"Yayarsa kuma? Ke Hasiya yi min gwari gwari ni bangane ba."
Sai na gyara zama na muskuta saboda na gaji da yadda na zauna.
Cikin ajiyar zuciya nace"Labarin mai Tsawo ne Adda, ammh mafi muhimmanci ne shine Assadiq ba maraya ba ne, ya na da uwa da uba a raye sannan shi din d'an Dangi ne. A takaice dai iyayensa ba su san ya aureni ba sai yanzu da yayyensa mata suka gano hakan."

Adda Fati baki ta Bud'e cikin mamaki da Al'ajabi kafin ta samu zarafin magana na katseta da fad'in"Na kiraki ne na fad'a miki Saboda ki sani, ba lalle na dawo da aurena a kaina ba, in komai ya rikice ba su aminta dani ba zan sake dawowa a sakakkiyar bazawara a karo na uku."
Ban jira cewarta ba na kashe wayar Saboda kukan da ke neman kwacemim.
Ina jinta ta na ta sake kira ban bi ta kanta ba, sai ma kaina da na kwantar saman gadon dakin na fashe da kuka, sai da na yi ma ishi sannan na share hawayena, na koma gefe ina sauke ajiyar zuciya.
Chapter 18 · 0% Book details