Sashe 24
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana ganin kimar Alhaji Jibril tun bayan da suka had'a auratayya a Tsakaninsu, ammh kuma wannan Labarin da yaji sai yaji kwata kwata ya raina masa ta ina zaka Biye ma wannan Abun da baka da Tabbaci a kansa? Kawai sai yaji kamar ya raina masa kwata kwata Tunda a baya yana ganinsa mai ilimi ne.
Falon ya kaure da hayaniya Umma kuka kawai ta ke yi ta na Hango kilama ta kusa rasa d'anta.
Surayya bata da mgana Saboda su Shahida da Sadiya suna kara ma Umma Famfo kar ma Sajida ta ji labari.
Sadiq sai kawai ya koma ya Dukar da kansa ya na kuma neman mafita ammh acikin ransa Hasbullahi ya ke ta maimaitawa.
Ba wanda ya san lokacin da Innani ta tashi sai da akaji muryan Abba na fad'in"Subhanallahi Innani lafiya?
Sai aka juyo nan fa aka ga Inanni ta Daga sandarta zata makama Hasiya dake zaune ta na kuka.
Fad'i ta ke yi"Ka bari na Rafketa Sulaimanu, wannan ai bakar dakace ta Shigo Cikin zuru'ata na bani ina jin ma ko mayyace zata lashe kurwan Magajin gida, namiji kwara d'aya kwal da Sulaimanu ya mallaka in wani abu ya sameshi ai mun lalace, ni Dije ina zan saka kaina, yau naga Bala'i ganin idona da maita."
Ta ke fad'a ta na kuka ta na kokarin kwace sandar ta daga hannun Abba.
A tare Surayya da Sadiq suka mike, sai dai ya Rigata isa kaina, tunda Innani ta saki sandarta da Hannu ta saka ta kaimin Dundu sai gadon bayan Assadiq Tunda ya yi min Rumfa.
Bata ma Fahimci shi ta ke duka ba idanuwanta ya Rufe fad'i ta ke yi"Mayya Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu, kurwan jikana Qur wlh, fita ki barmin gidana ki kuma Rabu da zuru'ata gabadaya."
Ta ke fad'a ta na kuka, Sadiq ya Dago a fusace ya Rike Hannun Innani yana fadin"Kada ki kara kiran matata da Mayya. SIYA ba mayya bace itama Mutum ce kamar kowa."
Ya fad'a cikin Tsawa kafin ya wancakar da Hannun Innani ya Dagoni jikinsa ya Rumgumeni kamkam, ni ko ina ta kuka ina fad'in"Assadiq don Allah kada ka rabu dani."
Ya na rike dani yace"Babu wanda ya isa ya rabani da ke Siya."
Sai jin muryan Umma ya yi ta na fadin"Har ni nan Abubakar.?
Idanuwanta Jajir ya ke kallonta kafin ya mike ya rikoni nima na mike ya Rikemin hanmu gam gam.
Sannan ya fara takawa dani har gaban Sultana itama ya mika mata Hannunsa guda daya sai taki kamawa ta kauda kai ta na kuka.
Da kansa ya Duka ya Riko hannunta itama ya mikaar da ita.
Ya kuma Jimke hannunta acikin hannunsa na Hagu, muna gefe da gefensa cikin karfin gwiwa yace"Na karbi duka zab'in Umma, da zabin da kuka yi min da wanda Ubangiji ya yi min da siya, ni na aureta ba ita ta aureni ba Umma ki yi hakuri kada kice zaki Rabani da matana."
Gadan gadan Umma kamar kabubuwa ta isa gabammu ta warce hannun Sultana ta na fadin"Ita wannan Annobar ka zaba kenan?
Shuru ya yi ya kasa mgana Umma ta daka masa tsawa lokaci daya ta na fadin"Ka bani amsata mana."
Kai Tsaye yace"Umma dukkansu ina son su, bazan iya barin d'aya saboda daya ba, ki yi hakuri."
Umma sai taji kanta ma ya fara Juyawa, ta kure Sadiq da ido kawai ta na kallonsa ganin haka yasa na fashe da kuka ina fadin"Don Allah ki yi hakuri Umma"
Ganin haka yasa Surayya ta rike Umma ta na fadin"Umma mu bi komai a sannu don Allah, mu godema Allah aure ya yi, in kuma ba auren ba ne fa! Zaki so ace Sadiq lalacewa ya rika yi achan? Ko kuma wannan Rabon fa ina za'a same shi?
Ta fad'a ta na nuna cikin jikina, ni kuma sai kuka na ke yi ina kara Fadin"Ki yi hakuri Umma ammh don Allah kada ki saka Assadiq ya sakeni."
Shahida ta katse ni da tsawa kafin tace"Dilla Rufema mutane baki Annoba kawai, ke har kina da bakin magana? Rabuwa kuma ai ya zama Dole sai dai kuma ki bi wani sarkin ba kanin mu ba."
Sadiya ta karbe da cewa"Ahto muna zaman zaman mu kada tsiya ta Fara Bibiyan mu."
Sajida tace"Kuma fa kuna ji fa bazawara auranta biyu, wannan ai bai yi ba kwata kwata."
Sakeena ta Dorawa da cewa"To kuna dai ji su kansu dangin su sun gujesu Saboda ita, Sai shi zai rumgumota?
Innani na gefe a had'a kai da Gwiwa sai kuka ta ke yi, ta na fadin sai an yi Turaren maita tunda ko na bar gidan Tunda na kwallafa rai sai na Bibiya kurwan jikanta.
Abba ko na zaune bai yi mgana ba, so ya ke magajin gida ya tsaya ma matarsa da kansa, in ya yi hakan shi kuma sai ya tabbatar da nashi Hukuncin kamar yadda ya yi a Farko.
Kowacce sai fadin albarkacin bakinta take yi a kaina suna aibatani da fadin dukkan kalaman da suka Fito daga bakinsu a kaina.
Sun kirani da suna Annoba, da kuma mai bakin jini, mayya shi yafi Dagamin Hankali ba bazawaran da suke ta Jifana dashi ba.
Sadiq ya gama jin iya abunda zai ji, yaga abun nasu ya yi yawa sai kawai ya kara Damke hannuna sannan ya Daka musu tsawa.
Sai kowacce ta yi shuru suna kallonsu ya na faman zare ido.
Hannunsa d'aya yasa ya na nuna su, Tunda Umma Surayya ta maidata saman kujera ta zauna ta na sharan kwallah.
Sai da ya nuna su da hannunsa kowacce a saman Fuskarta sannan cikin Kaushin murya yace"Ya ishe ku, kun yi na kudin ku, kada wacce a cikin ku ta kara aibatamin mata Ya isa nace.!"
Ya karishe fad'a a Fusace Subai'a ce ta taso masa ta na fadin"Bai isa ba, nace bai isa ba me zaka yi, Wlh kayi kad'an wannan Annobar ta zauna acikin mu"
A fusace"Ina Ruwan ki? a kan ki zata zauna?
Nace a kan ki zata zauna ko mijin ki ne zai rike min ita ballatana abun ya Dameki?
Ya fad'a cikin kaushin murya, baki gabadayansu suka Bude suna kallonshi.
Sa'ima tace"Sadiq ba dai rashin kunya zaka yi ma Anty subai ba?
Idanuwansa sun kad'a saboda bacin rai ya sakar mata wani kallo kafin yace"in ma nayi mata ai ita taja, domin kun fara Tsallake abunda ba Hurumin ku ba, babu wacce zata gayamin yadda zan tafiyar da Rayuwata sannan acikin ku ban ga wacce na taba mata katsalanda a abunda ya shafi gidan auranta ba, Saboda haka kada na kara jin kun tsoma min baki, wannan mganace tsakanina da iyayena da abunda zuciya ta zaba ku fitar da kan ku aciki."
Ya karishe fad'a cikin Tsawa har kuma Lokacin bai saki Hannuna ba.
Sadiya ta saka salati kafin tace"Kai yanzu Sadiq akan wannan yarinyar mai kama da zubin mayu ka ke jayyayya damu? Wannan Shegen cikin na jikin nata ko shi ka sani bazmu karb'esa ba."
"SADIYAAA...!
Sadiq ya wani Kira sunanta a Firgice cikin Tsawa da yasa har Umma sai da ta Dago ta na kallonsa.
A fusace ya saki hannuna ya taka har gaban Sadiya ya daga hannunsa manuniya ya nunata da shi kafin yace"Kada ki kuskura ki ce zaki aibatamin mata sannan ki shegantamin gudan jinina, kada ki kuskura na gaya miki."
Kawai sai tace"In ba haka ba fa? Ance shegen cikin, waya sani ma cikin ba naka bane Tunda tayi yawon dakuna sannan an san dadin zawar..'
"Sadiya..!"
Sadiq.."
Alokacin da ya Kira sunanta ya Daga hannu zai kai mata mari, Surayya ta kira sunanshi itama a tsawace.
Sai ya dakata lokaci d'aya yana Dunkule hannunsa sannan ya naushi iska.
Cikin Tsabar Fushi da yadda Jijiyon kansa ke tashi Saboda bacin rai.
Surayya cikin bacin rai tace"Ka bi a hankali mana wannan wani irin hauka ne, kai da ka ke kokarin gyara kuskurenka sai kuma ka bata shi da sake yin wani laifin?
Ta fad'a cikin bayyana bacin ranta kafin ta kalli Sadiya ta na fadin"ke kuma Sadiya kin fara Tsallake iyakarki, in bazamu fad'i alheri ba sai mu yi shuru."
Kawai sai Sadiya ta saka kuka ta na fadin"Mu ne yanzu Saboda mace Sadiq kana kanin bayanmu kana gaya mana magana, sannan har kana neman daga hannu ka maremu?
Sa'ima ta karbe da cewa"Ko domin darajan mun girmesa ai ya raga mana."
A fusace ya juya ya na kallonta kafin yace"Naji kun girmeni, ammh ai baku Haifeni ba sannan baku halliceni ba Allah ne ya Halliceni kuma shi kadai nake jin Tsoro kuma garesa kad'ai nake ninka bibbiyata, cikin ku ba wacce ta taba Daukan Ragamar Rayuwata, Saboda haka ku Rufemin bakin ku ku yi min shuru anan wajen."
Cikin Kaushin Murya ya fad'a sai gashi sun yi shuru cikin sarkewar murya yace"Duk da ina karamin ku ina da girman da Ubangiji ya bani kaf din ku da Harkarina aka hallice ku, kuma iyayena Ubangiji bai ce na yi musu biyayya kan abunda nasan ya saba ma addina ba, kuma ina so na Fad'a muku wani abu game da Kaddaran Siya da kuke ta aibata ta akan haka to ku saurareni da kunnen basira ku ji wani abu."
Ya dan dakata sai da ya kallesu d'aya bayan d'aya kafin ya fara fadin"Dukkan ku nan baku da iko a cikin kaddaran ku, kamar yadda itama Hasiya ba ta da wannan ikon a hannunta. In da ace Littafin kaddaramu a hannumu ake bamu mu zabi kalar Rayuwar da muke so mu yi a duniya na rantse da wanda raina ke Hannunsa cikin mu ba wanda zai yi kansa a yadda ya ke, kema bazaki saka kanki a wannan matsayin ba, nima haka to itama Hasiya haka bazata taba saka kaddaranta a haka ba, to ina so ku gane cewa Littafin Rayuwarmu da komai namu ubangiji ne ya ke Tsara mana komai, Hasiya ba Mayya bace sannan ita ba Annoba ce ba, duk abunda ya faru da ita ba ita bace ta yi silar Faruwarsu ba, Face Ubangiji da ya shiryama kowa kaddaransa sai dai ace itace Sanadi, kuma ku sani kuna wasa da Tauhidi sannan kuma hakan da kuka nuna ya kara tabbatar min da cewa baku san Qur'ani ba."
Sai gabadaya suka fara kallonsa cikin mamakin kalamnsa.
Falon ya kaure da hayaniya Umma kuka kawai ta ke yi ta na Hango kilama ta kusa rasa d'anta.
Surayya bata da mgana Saboda su Shahida da Sadiya suna kara ma Umma Famfo kar ma Sajida ta ji labari.
Sadiq sai kawai ya koma ya Dukar da kansa ya na kuma neman mafita ammh acikin ransa Hasbullahi ya ke ta maimaitawa.
Ba wanda ya san lokacin da Innani ta tashi sai da akaji muryan Abba na fad'in"Subhanallahi Innani lafiya?
Sai aka juyo nan fa aka ga Inanni ta Daga sandarta zata makama Hasiya dake zaune ta na kuka.
Fad'i ta ke yi"Ka bari na Rafketa Sulaimanu, wannan ai bakar dakace ta Shigo Cikin zuru'ata na bani ina jin ma ko mayyace zata lashe kurwan Magajin gida, namiji kwara d'aya kwal da Sulaimanu ya mallaka in wani abu ya sameshi ai mun lalace, ni Dije ina zan saka kaina, yau naga Bala'i ganin idona da maita."
Ta ke fad'a ta na kuka ta na kokarin kwace sandar ta daga hannun Abba.
A tare Surayya da Sadiq suka mike, sai dai ya Rigata isa kaina, tunda Innani ta saki sandarta da Hannu ta saka ta kaimin Dundu sai gadon bayan Assadiq Tunda ya yi min Rumfa.
Bata ma Fahimci shi ta ke duka ba idanuwanta ya Rufe fad'i ta ke yi"Mayya Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu, kurwan jikana Qur wlh, fita ki barmin gidana ki kuma Rabu da zuru'ata gabadaya."
Ta ke fad'a ta na kuka, Sadiq ya Dago a fusace ya Rike Hannun Innani yana fadin"Kada ki kara kiran matata da Mayya. SIYA ba mayya bace itama Mutum ce kamar kowa."
Ya fad'a cikin Tsawa kafin ya wancakar da Hannun Innani ya Dagoni jikinsa ya Rumgumeni kamkam, ni ko ina ta kuka ina fad'in"Assadiq don Allah kada ka rabu dani."
Ya na rike dani yace"Babu wanda ya isa ya rabani da ke Siya."
Sai jin muryan Umma ya yi ta na fadin"Har ni nan Abubakar.?
Idanuwanta Jajir ya ke kallonta kafin ya mike ya rikoni nima na mike ya Rikemin hanmu gam gam.
Sannan ya fara takawa dani har gaban Sultana itama ya mika mata Hannunsa guda daya sai taki kamawa ta kauda kai ta na kuka.
Da kansa ya Duka ya Riko hannunta itama ya mikaar da ita.
Ya kuma Jimke hannunta acikin hannunsa na Hagu, muna gefe da gefensa cikin karfin gwiwa yace"Na karbi duka zab'in Umma, da zabin da kuka yi min da wanda Ubangiji ya yi min da siya, ni na aureta ba ita ta aureni ba Umma ki yi hakuri kada kice zaki Rabani da matana."
Gadan gadan Umma kamar kabubuwa ta isa gabammu ta warce hannun Sultana ta na fadin"Ita wannan Annobar ka zaba kenan?
Shuru ya yi ya kasa mgana Umma ta daka masa tsawa lokaci daya ta na fadin"Ka bani amsata mana."
Kai Tsaye yace"Umma dukkansu ina son su, bazan iya barin d'aya saboda daya ba, ki yi hakuri."
Umma sai taji kanta ma ya fara Juyawa, ta kure Sadiq da ido kawai ta na kallonsa ganin haka yasa na fashe da kuka ina fadin"Don Allah ki yi hakuri Umma"
Ganin haka yasa Surayya ta rike Umma ta na fadin"Umma mu bi komai a sannu don Allah, mu godema Allah aure ya yi, in kuma ba auren ba ne fa! Zaki so ace Sadiq lalacewa ya rika yi achan? Ko kuma wannan Rabon fa ina za'a same shi?
Ta fad'a ta na nuna cikin jikina, ni kuma sai kuka na ke yi ina kara Fadin"Ki yi hakuri Umma ammh don Allah kada ki saka Assadiq ya sakeni."
Shahida ta katse ni da tsawa kafin tace"Dilla Rufema mutane baki Annoba kawai, ke har kina da bakin magana? Rabuwa kuma ai ya zama Dole sai dai kuma ki bi wani sarkin ba kanin mu ba."
Sadiya ta karbe da cewa"Ahto muna zaman zaman mu kada tsiya ta Fara Bibiyan mu."
Sajida tace"Kuma fa kuna ji fa bazawara auranta biyu, wannan ai bai yi ba kwata kwata."
Sakeena ta Dorawa da cewa"To kuna dai ji su kansu dangin su sun gujesu Saboda ita, Sai shi zai rumgumota?
Innani na gefe a had'a kai da Gwiwa sai kuka ta ke yi, ta na fadin sai an yi Turaren maita tunda ko na bar gidan Tunda na kwallafa rai sai na Bibiya kurwan jikanta.
Abba ko na zaune bai yi mgana ba, so ya ke magajin gida ya tsaya ma matarsa da kansa, in ya yi hakan shi kuma sai ya tabbatar da nashi Hukuncin kamar yadda ya yi a Farko.
Kowacce sai fadin albarkacin bakinta take yi a kaina suna aibatani da fadin dukkan kalaman da suka Fito daga bakinsu a kaina.
Sun kirani da suna Annoba, da kuma mai bakin jini, mayya shi yafi Dagamin Hankali ba bazawaran da suke ta Jifana dashi ba.
Sadiq ya gama jin iya abunda zai ji, yaga abun nasu ya yi yawa sai kawai ya kara Damke hannuna sannan ya Daka musu tsawa.
Sai kowacce ta yi shuru suna kallonsu ya na faman zare ido.
Hannunsa d'aya yasa ya na nuna su, Tunda Umma Surayya ta maidata saman kujera ta zauna ta na sharan kwallah.
Sai da ya nuna su da hannunsa kowacce a saman Fuskarta sannan cikin Kaushin murya yace"Ya ishe ku, kun yi na kudin ku, kada wacce a cikin ku ta kara aibatamin mata Ya isa nace.!"
Ya karishe fad'a a Fusace Subai'a ce ta taso masa ta na fadin"Bai isa ba, nace bai isa ba me zaka yi, Wlh kayi kad'an wannan Annobar ta zauna acikin mu"
A fusace"Ina Ruwan ki? a kan ki zata zauna?
Nace a kan ki zata zauna ko mijin ki ne zai rike min ita ballatana abun ya Dameki?
Ya fad'a cikin kaushin murya, baki gabadayansu suka Bude suna kallonshi.
Sa'ima tace"Sadiq ba dai rashin kunya zaka yi ma Anty subai ba?
Idanuwansa sun kad'a saboda bacin rai ya sakar mata wani kallo kafin yace"in ma nayi mata ai ita taja, domin kun fara Tsallake abunda ba Hurumin ku ba, babu wacce zata gayamin yadda zan tafiyar da Rayuwata sannan acikin ku ban ga wacce na taba mata katsalanda a abunda ya shafi gidan auranta ba, Saboda haka kada na kara jin kun tsoma min baki, wannan mganace tsakanina da iyayena da abunda zuciya ta zaba ku fitar da kan ku aciki."
Ya karishe fad'a cikin Tsawa har kuma Lokacin bai saki Hannuna ba.
Sadiya ta saka salati kafin tace"Kai yanzu Sadiq akan wannan yarinyar mai kama da zubin mayu ka ke jayyayya damu? Wannan Shegen cikin na jikin nata ko shi ka sani bazmu karb'esa ba."
"SADIYAAA...!
Sadiq ya wani Kira sunanta a Firgice cikin Tsawa da yasa har Umma sai da ta Dago ta na kallonsa.
A fusace ya saki hannuna ya taka har gaban Sadiya ya daga hannunsa manuniya ya nunata da shi kafin yace"Kada ki kuskura ki ce zaki aibatamin mata sannan ki shegantamin gudan jinina, kada ki kuskura na gaya miki."
Kawai sai tace"In ba haka ba fa? Ance shegen cikin, waya sani ma cikin ba naka bane Tunda tayi yawon dakuna sannan an san dadin zawar..'
"Sadiya..!"
Sadiq.."
Alokacin da ya Kira sunanta ya Daga hannu zai kai mata mari, Surayya ta kira sunanshi itama a tsawace.
Sai ya dakata lokaci d'aya yana Dunkule hannunsa sannan ya naushi iska.
Cikin Tsabar Fushi da yadda Jijiyon kansa ke tashi Saboda bacin rai.
Surayya cikin bacin rai tace"Ka bi a hankali mana wannan wani irin hauka ne, kai da ka ke kokarin gyara kuskurenka sai kuma ka bata shi da sake yin wani laifin?
Ta fad'a cikin bayyana bacin ranta kafin ta kalli Sadiya ta na fadin"ke kuma Sadiya kin fara Tsallake iyakarki, in bazamu fad'i alheri ba sai mu yi shuru."
Kawai sai Sadiya ta saka kuka ta na fadin"Mu ne yanzu Saboda mace Sadiq kana kanin bayanmu kana gaya mana magana, sannan har kana neman daga hannu ka maremu?
Sa'ima ta karbe da cewa"Ko domin darajan mun girmesa ai ya raga mana."
A fusace ya juya ya na kallonta kafin yace"Naji kun girmeni, ammh ai baku Haifeni ba sannan baku halliceni ba Allah ne ya Halliceni kuma shi kadai nake jin Tsoro kuma garesa kad'ai nake ninka bibbiyata, cikin ku ba wacce ta taba Daukan Ragamar Rayuwata, Saboda haka ku Rufemin bakin ku ku yi min shuru anan wajen."
Cikin Kaushin Murya ya fad'a sai gashi sun yi shuru cikin sarkewar murya yace"Duk da ina karamin ku ina da girman da Ubangiji ya bani kaf din ku da Harkarina aka hallice ku, kuma iyayena Ubangiji bai ce na yi musu biyayya kan abunda nasan ya saba ma addina ba, kuma ina so na Fad'a muku wani abu game da Kaddaran Siya da kuke ta aibata ta akan haka to ku saurareni da kunnen basira ku ji wani abu."
Ya dan dakata sai da ya kallesu d'aya bayan d'aya kafin ya fara fadin"Dukkan ku nan baku da iko a cikin kaddaran ku, kamar yadda itama Hasiya ba ta da wannan ikon a hannunta. In da ace Littafin kaddaramu a hannumu ake bamu mu zabi kalar Rayuwar da muke so mu yi a duniya na rantse da wanda raina ke Hannunsa cikin mu ba wanda zai yi kansa a yadda ya ke, kema bazaki saka kanki a wannan matsayin ba, nima haka to itama Hasiya haka bazata taba saka kaddaranta a haka ba, to ina so ku gane cewa Littafin Rayuwarmu da komai namu ubangiji ne ya ke Tsara mana komai, Hasiya ba Mayya bace sannan ita ba Annoba ce ba, duk abunda ya faru da ita ba ita bace ta yi silar Faruwarsu ba, Face Ubangiji da ya shiryama kowa kaddaransa sai dai ace itace Sanadi, kuma ku sani kuna wasa da Tauhidi sannan kuma hakan da kuka nuna ya kara tabbatar min da cewa baku san Qur'ani ba."
Sai gabadaya suka fara kallonsa cikin mamakin kalamnsa.