Sashe 30
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ba ni da yarda zan yi, hakanan na kira su Adda Fati ina gayamusu ita kuma tace miye aciki naje cikin Dangin mijina na yi sallah Tunda haka ya ke so, Adda Rukayya ce da muka yi waya ta rika masifan kada naje a wulakantani fa, tunda ai Adda Fati ta gayamata yadda komai ya Faru.
Sai na nuna mata ba wanda zai min wulakanci matukar Assadiq na tare dani, har Amma sai da na kira na gayamata ita dai Fatan alheri kawai ta yi mana. Kafin ya iso duk na had'a abunda zan Bukata da yamma ya iso dakyar na iya Dama masa kuni, shima sai ya tsinke zubarwa na yi Maman Suhaihat ce ta bashi abun bude baki tunda ni azumin da na yi duka duka bai wuce goma ba.
Washegari kuma Tun safe muka Dauki Hanya Tunda da Motarsa ya zo, da na gaji da zama yaga ina ta faman Mutsu mutsu sai muka Tsaya ya Budemin baya na shiga yace na kwanta na Huta shi kuma ya koma gidan Gaba yacigaba da Tukinsa.
Da wuri muka isa gusai Shashen Umma muka fara sauka, kuma kamar yadda na Lura kowa yasan da zuwana Tunda shi Assadiq din ya tabbatar musu anan zamu yi sallah.
Na dauka zuwa wannan Lokacin Umma ta sauko ashe abun ba haka ba ne, da muka shigo ta na zaune afalonta ita da Sultana suna Sauraran wa'azi a tashar Sunna Tv.
Sultana na Sanye da Atamfa Doguwar riga ta na ganinmu mun shigo Umma tace ta tashi ta shiga ciki.
Zan durkusa na gaisheta Assadiq yace na zauna saman kujera daman kuma in nace zan duka to aiki ne babba na jama kaina.
Dagani har Assadiq Umma bata amsa gaisuwarmu ba.
Sai ma wani kallo da ta yi mana ta Dauke kai.
Dagani har shi sai muka yi shuru muka kasa mgana , ni kaina a kasa ina ta fama da faduwar gaba.
Shi kuma yana Tunanin Fushin Umma zuwa yanzu ya yi yawa gaskiya.
Shi a ganinsa tunda ya gane kuskurensa to ta yafe masa kamar yadda Abba ya yi, sannan ta zaunar da shi su yi mgana ta Fahimtar juna.
Zuwa lokacin Har chan shinkafi su san da Labarin auransa kuma sun kikkirasa sun yi masa Fatan alheri.
Baba Shitu kuma mahaifin Sultana shi da kanshi ya kirasa ya fad'a masa abunda Sadiq bai sani ba ita Sultanan ta kirashi ta na kuka ta na fad'amai wai Sadiq yaci Amanarta sai da ya yi mata Fata fata sannan.
Kuma ba wanda yasan Umma ta barota da gidan mijinta ta dawo gabanta da zama ya'yanta na zugata.
Abba kuma har alokacin bai ce mata komai ba Sadiq ya kirasa ya na gayamasa Umma bata Daukan wayansa ko zai yi mata mgana?
Abba yace ya kara bata Lokaci ta Huce Tukunnah.
Kamar daga sama naji Umma tace"Ke bakar Annoba tashi ki fita zan yi mgana da d'ana."
Haka ta fad'a kai Tsaye Lokaci d'aya ta na Hararana.
Da Sauri na mike har sai da bayana ya amsa, Shima mikewar ya yi Umma ta dakamai Tsawa kafin tace"Koma to ka zauna Bita zai zai."
Ba shi da yadda zai yi sai ya koma ya zauna sannan ya kalleni ya na fad'in"Ki shiga bangaren Innani ko bangarem mama"
Ban ce komai ba na kama Hanyar Fita shi kuma sai ya daga murya ya na fadin"Kin ji ko?
Sai na juyo ina daga masa kai idanuwana fal da kwallah.
Na jima a haraban gidan na rasa ina zani sai da na gama kukana na share kwalla sannan na nufi bangaren Mama.
Kaamar Daga sama ta ganni farko Siyama ce zaune a falo ammh yarinyar nan kallo wulakanci ta yi min sai ni ce na gaisheta sannan nace mata wajen Mama nazo, shima sai da taga dama sannan ta tashi ta shiga ciki ta yi ma Maman mgana sai ga su sun fito tare.
Ita da Fara'a muka gaisa fad'i ta ke yi" yanzu kuka iso kenan? Ina shi magajin gidan?
Kaina na kasa nace"Ya na wajen Umma, shi yace na zo nan na zauna."
Mama ta jinjina kai kafin tace"Allah sarki sannun ku da zuwa ya nauyin jiki? Kai wannan cikin naki akwai girma wa ya ga Runduna."
Kaina na kasa ban yi mgana ba, sai faman hira take min ta min Tambayoyi ni kuma bani da sakewa yasa na ke amsata daya daya.
Ni ce naga ko ruwa ba ta bani ba sai nace mata zan sha ruwa.
Cikin yake tace"Af nafa manta ku bakwa azumi, Siyama"
Sai ta fara kwalama Siyama kira sai gashi ta fito ta na wani Tura baki Mama tace ta kawomin Ruwa.
A wulakance ta kawomin Ruwan gora kuma don mugunta mai sanyi, ba ta ko Duba Halin da ni ke ciki ba.
Kuma babu ko karamin kofin da zan sha, Kuma gashi ina jin kishi hakanan na sha kad'an na ijiye.
Daga karshe da Mama taga na kasa sakin baki na bata labari sai ta shige ciki su ka barni anan kamar wata almajira.
Gashi Fitsari ya matseni na rasa yadda zan yi, ina zaune kawai ina ta sharan kwallah na tausayin kaina a baya ina Murnan na fita daga cikin Tsaka mai wuya ashe tsuguuno bata karemin ba.
******
A falon Umma kuwa bayan Fitata sai da Umma ta gama shanya Sadiq zaune a gabanta sannan ta gyara zama ta kalleshi Lokaci d'aya ta na fadin"Abubakar dago nan ka kalleni."
Ba musu ya dago yana kallonta Fuskarta ba Fara'a tace"Wacece ni hala a wajen ka?
Cikin mamakin Tambayarta yace"Ke din mahaifiyata ce."
Wani mirmishi Umma ta yi kafin ta daga baki ta kira sunan Sultana ta amsa sai gashi ta fito.
Gaban Umma ta durkusa ta na cewa gata, Umma ta kalleta yadda duk ta rame a tsaye, suma cikin satin da ya fita suka gama WEac Sai neco.
Duk ta rame ta Lalace sannan ba ta da wani Walwala bata da aiki sai kuka.
Itace ya kamata ta share mata hawaye Tunda dai ba ta da wata Uwar da ta wuceta.
Nuna masa ita ta yi kafin tace"Ita kuma miye nata matsayin a wajen ka?
Sai da ya dago ya na kallon sultana wacce ta kauda kai gefe kamar bata son kallonsa.
Cikin sanyin murya yace"Ita d'in kanwata ce sannan kuma matata."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Shine ka maida maganata banzaa ko Sadiq? Ba na gayamaka ka zaba ko sultana ko wanchar bakar Annobar ba? Ammh Saboda Alhaji ya baka Dama sai ka saka kafa ka shure mganata ka yi tafiyarka tare da matarka kana so ka nuna min abunda ka ke nufi ko?
Zai yi mgana ta daga masa hannu a Fusace ta na cigaba fad'in"Bana son jin komai daga bakin ka, yanzu zaka gayamin meneme manufarka? Tunda ka tafi ka barni da yarinya kuma baka min wata mgana ba, in ka zab'i wancan ne sai ka sakarmin yarinya domin tasan ta fara Iddarta."
Baki ya saki kafin yace"Me ya kawo kuma mganar Saki anan wajen kuma Umma?
Umma ta balla masa Harara kafin tace"Bansani ba, sallamamme mara Tunani ai na riga na fada maka baka isa ba. Indai ka zabi zama da wannan Annobar to sai ka sakarmin y'a kaji ma na gayamaka."
Shuru ya yi kansa na kasa kafin yace"Umma ba maganar saki Tsakanina da Sultana ballatana Siya, dukkansu ban aure su domin na sake su ba."
Umma ta harzuko kamar zata dakesa ta na fadin"To wlh ahir dinka, kai da dauko bala'in sai dai ya kare maka ammh bazan bari diyata ta zauna da kai ba, tunda ka zabi Ita Bakar Annoba to ka shirya sakar min yarinya kaji ma na rantse."
Cikin mamaki yace"Umma kada ki yi saurin Rantsuwa fa?
Umma tace"Nace wlh tallahi Rantsuwan d'an musulmi in baka saki wannan annobar matar da ka jajibo ba, to auren ka da Sultana na Haramtashi."
Baki sake yace"Umma kada ki zo ki yi kafarra gwara ki janye rantsuwan ki domin na baki tabbacin dukkansu ina son su ba kuma zan iya Rabuwa da d'aya saboda d'aya ba."
Mamakinsa ya kama Umma daman ai tasan halinsa ba'a kadashi a mgana.
A fusace tace"Sai kuma ka yi, tashi ka bani waje ni na riga na gama mgana."
Kin tashi ya yi sai ma ya gyara zama yana fadin"Umma ki yi hakuri don Allah, nasan na yi ba daidai ba ammh tunda nagane kuskurena sai ki yi min afuwa don Allah."
Umma saboda ma tagaji da jin mganarsa sai kawai ta kallo sultana ta na fadin"Ke tashi ki karamin karan Tibin nan ki shiga ciki."
Ba musu Sultana ta mike Idanuwanta har sun tasa saboda kuka ta kara karan talabijin din ta wuce salau salau ta koma cikin daki Sadiq ya bita da kallo.
Sai na nuna mata ba wanda zai min wulakanci matukar Assadiq na tare dani, har Amma sai da na kira na gayamata ita dai Fatan alheri kawai ta yi mana. Kafin ya iso duk na had'a abunda zan Bukata da yamma ya iso dakyar na iya Dama masa kuni, shima sai ya tsinke zubarwa na yi Maman Suhaihat ce ta bashi abun bude baki tunda ni azumin da na yi duka duka bai wuce goma ba.
Washegari kuma Tun safe muka Dauki Hanya Tunda da Motarsa ya zo, da na gaji da zama yaga ina ta faman Mutsu mutsu sai muka Tsaya ya Budemin baya na shiga yace na kwanta na Huta shi kuma ya koma gidan Gaba yacigaba da Tukinsa.
Da wuri muka isa gusai Shashen Umma muka fara sauka, kuma kamar yadda na Lura kowa yasan da zuwana Tunda shi Assadiq din ya tabbatar musu anan zamu yi sallah.
Na dauka zuwa wannan Lokacin Umma ta sauko ashe abun ba haka ba ne, da muka shigo ta na zaune afalonta ita da Sultana suna Sauraran wa'azi a tashar Sunna Tv.
Sultana na Sanye da Atamfa Doguwar riga ta na ganinmu mun shigo Umma tace ta tashi ta shiga ciki.
Zan durkusa na gaisheta Assadiq yace na zauna saman kujera daman kuma in nace zan duka to aiki ne babba na jama kaina.
Dagani har Assadiq Umma bata amsa gaisuwarmu ba.
Sai ma wani kallo da ta yi mana ta Dauke kai.
Dagani har shi sai muka yi shuru muka kasa mgana , ni kaina a kasa ina ta fama da faduwar gaba.
Shi kuma yana Tunanin Fushin Umma zuwa yanzu ya yi yawa gaskiya.
Shi a ganinsa tunda ya gane kuskurensa to ta yafe masa kamar yadda Abba ya yi, sannan ta zaunar da shi su yi mgana ta Fahimtar juna.
Zuwa lokacin Har chan shinkafi su san da Labarin auransa kuma sun kikkirasa sun yi masa Fatan alheri.
Baba Shitu kuma mahaifin Sultana shi da kanshi ya kirasa ya fad'a masa abunda Sadiq bai sani ba ita Sultanan ta kirashi ta na kuka ta na fad'amai wai Sadiq yaci Amanarta sai da ya yi mata Fata fata sannan.
Kuma ba wanda yasan Umma ta barota da gidan mijinta ta dawo gabanta da zama ya'yanta na zugata.
Abba kuma har alokacin bai ce mata komai ba Sadiq ya kirasa ya na gayamasa Umma bata Daukan wayansa ko zai yi mata mgana?
Abba yace ya kara bata Lokaci ta Huce Tukunnah.
Kamar daga sama naji Umma tace"Ke bakar Annoba tashi ki fita zan yi mgana da d'ana."
Haka ta fad'a kai Tsaye Lokaci d'aya ta na Hararana.
Da Sauri na mike har sai da bayana ya amsa, Shima mikewar ya yi Umma ta dakamai Tsawa kafin tace"Koma to ka zauna Bita zai zai."
Ba shi da yadda zai yi sai ya koma ya zauna sannan ya kalleni ya na fad'in"Ki shiga bangaren Innani ko bangarem mama"
Ban ce komai ba na kama Hanyar Fita shi kuma sai ya daga murya ya na fadin"Kin ji ko?
Sai na juyo ina daga masa kai idanuwana fal da kwallah.
Na jima a haraban gidan na rasa ina zani sai da na gama kukana na share kwalla sannan na nufi bangaren Mama.
Kaamar Daga sama ta ganni farko Siyama ce zaune a falo ammh yarinyar nan kallo wulakanci ta yi min sai ni ce na gaisheta sannan nace mata wajen Mama nazo, shima sai da taga dama sannan ta tashi ta shiga ciki ta yi ma Maman mgana sai ga su sun fito tare.
Ita da Fara'a muka gaisa fad'i ta ke yi" yanzu kuka iso kenan? Ina shi magajin gidan?
Kaina na kasa nace"Ya na wajen Umma, shi yace na zo nan na zauna."
Mama ta jinjina kai kafin tace"Allah sarki sannun ku da zuwa ya nauyin jiki? Kai wannan cikin naki akwai girma wa ya ga Runduna."
Kaina na kasa ban yi mgana ba, sai faman hira take min ta min Tambayoyi ni kuma bani da sakewa yasa na ke amsata daya daya.
Ni ce naga ko ruwa ba ta bani ba sai nace mata zan sha ruwa.
Cikin yake tace"Af nafa manta ku bakwa azumi, Siyama"
Sai ta fara kwalama Siyama kira sai gashi ta fito ta na wani Tura baki Mama tace ta kawomin Ruwa.
A wulakance ta kawomin Ruwan gora kuma don mugunta mai sanyi, ba ta ko Duba Halin da ni ke ciki ba.
Kuma babu ko karamin kofin da zan sha, Kuma gashi ina jin kishi hakanan na sha kad'an na ijiye.
Daga karshe da Mama taga na kasa sakin baki na bata labari sai ta shige ciki su ka barni anan kamar wata almajira.
Gashi Fitsari ya matseni na rasa yadda zan yi, ina zaune kawai ina ta sharan kwallah na tausayin kaina a baya ina Murnan na fita daga cikin Tsaka mai wuya ashe tsuguuno bata karemin ba.
******
A falon Umma kuwa bayan Fitata sai da Umma ta gama shanya Sadiq zaune a gabanta sannan ta gyara zama ta kalleshi Lokaci d'aya ta na fadin"Abubakar dago nan ka kalleni."
Ba musu ya dago yana kallonta Fuskarta ba Fara'a tace"Wacece ni hala a wajen ka?
Cikin mamakin Tambayarta yace"Ke din mahaifiyata ce."
Wani mirmishi Umma ta yi kafin ta daga baki ta kira sunan Sultana ta amsa sai gashi ta fito.
Gaban Umma ta durkusa ta na cewa gata, Umma ta kalleta yadda duk ta rame a tsaye, suma cikin satin da ya fita suka gama WEac Sai neco.
Duk ta rame ta Lalace sannan ba ta da wani Walwala bata da aiki sai kuka.
Itace ya kamata ta share mata hawaye Tunda dai ba ta da wata Uwar da ta wuceta.
Nuna masa ita ta yi kafin tace"Ita kuma miye nata matsayin a wajen ka?
Sai da ya dago ya na kallon sultana wacce ta kauda kai gefe kamar bata son kallonsa.
Cikin sanyin murya yace"Ita d'in kanwata ce sannan kuma matata."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Shine ka maida maganata banzaa ko Sadiq? Ba na gayamaka ka zaba ko sultana ko wanchar bakar Annobar ba? Ammh Saboda Alhaji ya baka Dama sai ka saka kafa ka shure mganata ka yi tafiyarka tare da matarka kana so ka nuna min abunda ka ke nufi ko?
Zai yi mgana ta daga masa hannu a Fusace ta na cigaba fad'in"Bana son jin komai daga bakin ka, yanzu zaka gayamin meneme manufarka? Tunda ka tafi ka barni da yarinya kuma baka min wata mgana ba, in ka zab'i wancan ne sai ka sakarmin yarinya domin tasan ta fara Iddarta."
Baki ya saki kafin yace"Me ya kawo kuma mganar Saki anan wajen kuma Umma?
Umma ta balla masa Harara kafin tace"Bansani ba, sallamamme mara Tunani ai na riga na fada maka baka isa ba. Indai ka zabi zama da wannan Annobar to sai ka sakarmin y'a kaji ma na gayamaka."
Shuru ya yi kansa na kasa kafin yace"Umma ba maganar saki Tsakanina da Sultana ballatana Siya, dukkansu ban aure su domin na sake su ba."
Umma ta harzuko kamar zata dakesa ta na fadin"To wlh ahir dinka, kai da dauko bala'in sai dai ya kare maka ammh bazan bari diyata ta zauna da kai ba, tunda ka zabi Ita Bakar Annoba to ka shirya sakar min yarinya kaji ma na rantse."
Cikin mamaki yace"Umma kada ki yi saurin Rantsuwa fa?
Umma tace"Nace wlh tallahi Rantsuwan d'an musulmi in baka saki wannan annobar matar da ka jajibo ba, to auren ka da Sultana na Haramtashi."
Baki sake yace"Umma kada ki zo ki yi kafarra gwara ki janye rantsuwan ki domin na baki tabbacin dukkansu ina son su ba kuma zan iya Rabuwa da d'aya saboda d'aya ba."
Mamakinsa ya kama Umma daman ai tasan halinsa ba'a kadashi a mgana.
A fusace tace"Sai kuma ka yi, tashi ka bani waje ni na riga na gama mgana."
Kin tashi ya yi sai ma ya gyara zama yana fadin"Umma ki yi hakuri don Allah, nasan na yi ba daidai ba ammh tunda nagane kuskurena sai ki yi min afuwa don Allah."
Umma saboda ma tagaji da jin mganarsa sai kawai ta kallo sultana ta na fadin"Ke tashi ki karamin karan Tibin nan ki shiga ciki."
Ba musu Sultana ta mike Idanuwanta har sun tasa saboda kuka ta kara karan talabijin din ta wuce salau salau ta koma cikin daki Sadiq ya bita da kallo.