← Book details Tmw Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 83

Sashe 10

Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai gashi kafin ma ta tambayeta Saliha ta fara gayamata Hasiya ta ja baya da ita, ba kamar farkon fara kawancen su ba.
Surayya ta koma ta zauna Dafe da kai bayan sun gama mgana da Saliha a waya.
Jikinta gabadaya ya saki bata so ma ta yi wani Tunani sai kawai ta fara maimaita"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un" a cikin zuciyarta.
Wacece wannan yarinyar Tare da Sadiq? Me ye alaqarsu da za su yi Hoto rike da juna haka?
A ina zata samu amsar Tambayoyinta?
Kiran Saddiqa ya katse mata Tunani da Sauri ta daga kiran ta na fadin"Saddiqa Sadiq ne a wannan Hoton."
Saddiqa tace"Innalillahi Sadiq ne?
Surayya tace"Ba tabbaci gareni ba, yakini ne da cewa shi ne Saddiqa"
Saddiqa ta share zufa kafin tace"To in dai shine to miye alakarsa da wannan yarinyar?
Surayya tace"Sunanta Hasiya, kuma yar'uwar mijin Salima ce, itace kawar da Saliha ta yi a kaduna, ta kuma zo bikin su Sultana Shiyasa ki ke Tunanin kin santa"

Saddiqa ta saki baki kafin tace"Tabbas an yi haka sai da kika fad'a na gane? Wacce Saliha tace ta tafi ba ta yi mata sallama ba?
Surayya tace"Saddiqa ki bar mganar nan a tsakanin ni da ke, zan yi yadda zan yi na binciko komai  ammh kema ta bangaranki ina so ki samo min address din in da yarinyar ke zaune."
Saddiqa tace"Big sis Khairiya tace min fa matar aure ce kuma a yadda abun ya ke, Sadiq shine mijinta wai"
Surayya tace"Duk da haka muna so mu san inda ta ke, ki kace a zariya ko?
Saddiqa tace"Eh haka tace"
Kawai sai Surayya ta yi wani Dariya takaici kafin tace"No wonder"
Daga haka ta katse wayarta, ta fara safa da marwa a tsakar falonta.
Ta na sake maimaita sunan Hasiya da Zariya.
Sai kawai ta fara Tunano yadda Sadiq ya nace ma karatu a zariya, ya gama yace bautar kasa, ya gama yace aiki zai yi achan sai ya fake da karatu, ta tuna ya na yawan ambaton wata ASIYA da sunan abokiyar aikinsa, kenan in ta hasaso daidai su Sadiq ya maida kananun yara ya ke wasa da Hankalinsu?
Koma wacece wannan yarinyar akwai alaqar da ta yi karfi a tsakaninsu wacce ba su sani ba, ita ko kadan bata bari Tunaninta ya bata wani mugun abu Sadiq ya ke yi ba, Tunanin ya fi karkarta kan abunda Sauran ba su hasaso ba.
Wayarta ta sake Dauka da Sauri ta Kira Salima ta na tambayanta ko ta na ina? Sai tace mata ta na makaranta.
Kai Tsaye Surayya tace"Salima me kika sani kan wannan yar'uwan mijin naki kawar Saliha?
Salima tace"Wacce Big sis? Ban ganeta ba?
Surayya tace"Wacce suka had"u lokacin bikin ki, ta kuma zo bikin su sultana.".
Salima da ke tare da Zahra'u a makaranta domin ta fara karatu a kasu, kaduna State University.
Tace"Oh na tuna me ya faru da ita?
Surayya tace"Kinsan ta sosai ne?
Salima tace"a'a ni ban kara ganinta ba, hala me ya faru?
Surayya tace"Taimako na zaki yi, ina son sanin labarinta ne, ko shi Mubark din ki tambayeshi mana."
Salima tace"Ok!
Sai Surayya tace zata Tura mata Hoton ta, Tunda ta lura kamar Saliman ba ta maida kai kan mganar da ta ke yi mata ba.
Da Sauri ta Bude data sai ga Hotunan Saliha ta Turo mata harda wanda ta yi mata ita kad'ai Tabbas wannan yarinyar ce.

Da Sauri ta Dauka ta Turama Salima, ta kuma kara kiranta tace ta bincika mata da Sauri don Allah.
Jin haka yasa Salima cikin Tunanin to lafiya? Ta dai san me ya had'a Big sis da neman Labarin wata!?
Sai dai sanin kawar Anty Saliha ce sai bata damu ba nan ta ke ta Bude datan ta, ta shiga ta ga Hoton da Big sis ta Turamata sai a lokacin ta kara gane Matar da ake mgana a kanta.
Zahra'u ce ta leka ta na ganin Hoton sai taga Hasiya da Sauri tace"Hala wannan ai Hasiya ce"
Salima sai ta kalleta kafin tace"Eh itace kinsan ta ne sosai?
Sai zahra'u ta girgiza kai kafin tace"Gasiiya ba sosai ba, ni ma da Bikin ku ne na santa, da ya ke Baba bai cika barin mu, muna zuwa zariya ba, sai dai su zo"
Sai salima tace"To ki tambayan min ko Baba ne kin ji ko?
Sai Zahra'u tace to shikenan zata tambayan mata, ammh sai da tambayeta me yasa ta ke son sanin Labarin Hasiya? Sai tace kawar yayarta ne ita ke son karin sani akanta.
Sai zahra'un ta gamsu da maganar Salimar kamar yadda, itama Salima ta gamsu da cewa dalilin da ya sa Big sis din ke son ta sani kenan.

Ita kuma ta bangaren Surayya, sai da ta gama Tunaninta gabadaya sannan ta daga waya ta kira Sajida tace anjuma tazo gidanta ta na nemanta.
Sajida kuma daman uwar son jin mgana ne da zence, ba jimawa sai ga ta tazo, itama Hoton Surayya ta nuna mata tace ko ta gane waye?
Da sauri ta Mike ta na kwalalo ido Lokaci daya ta na fadin"Mun shiga uku, kamar Sadiq?
Surayya tace"ai ba kama bace shine."
Sajida ta dafe kirji da karfi kafin tace"Shi ne? To ita wannan macen da ke tare da shi fa! Wacece?
Surayya tace"Shi na ke son sani yanzu, ki kara kallonta dakyau zaki ganeta, kin taba ganinta kawar Saliha da ta zo bikin sultana wacce tace yar'uwan mijin salima ce."

Sajida sai ta kara zooming din Hoton ta na gani kafin tace"Tabbas ba musu itace, kinsan ai fara ce sosai shiyasa na ga neta. Big sis sadiq me zai ja mana? Ba dai ya koma Bin matan aure ba ne?
Ta fad'a cikin tashin Hankali, Surayya ta Girgiza mata kai kafin tace"Ba na wannan Tunanin Sajida, a sanin da na yi ma Sadiq mutum ne mai ilimi da sanin ya kamata, ba zai aikata haka ba."
Sajida ta koma ta zauna da yarta a hannu lokaci d'aya ta na fad'in"Big sis kaina ya Daure? Ko da bikin ne suka had'u da juna?
Surayya na kallon wani gefe tace"Ba'a lokacin ba ne, sun jima da sanin juna Sajida."
Sajida ta yi shuru kafin tace"Big sis wlh na shiga Rud'u, me ke shirin Faruwa ne?
Surayya ta koma ta zauna gefen Sajida Ta na fadin"Koma wacece to alaqar da ke tsakaninsu ba ta haramci ba ne."
Sajida tace"To alaqar uwar menene tunda ba aure suka yi ba?
Surayya ta kalleta kafin tace"In kuma ace sun yi auren fa? In kuma ace ita din MATARSA CE.!"
SAi Sajida ta zabura kafin tace"Matarsa?
Cikin Dimuwa, surayya ba ta sami zarafin magana ba, kiran Saddiqa ya shigo wayarta da Sauri ta Daga.
Mirmishi kawai ta ke yi na dacin zuciya da takaici, Saddiqa na gayamata ta tura mata adireshin inda Hasiya ke zaune, kuma har da karin Shedar mijinta ma'aikaci ne a garin Abuja.
Surayya ta yi ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa mu bar mganar nan a tsakanin mu uku, bayan mu kada najita a waje, ni da Sajida gobe in sha Allahu zamu tafi zariya domin mu kara Tabbatar da zargin mu."
Saddiqa tace"Gaskiya ya kamata, ni wlh duk na Rude, Umma kawai na ke tunawa, fata na Allah yasa ba Sadiq din mu ba ne"
Surayya bata ce komai ba ta katse wayar, a ranta ta na tunanin suna ma yaudaran kansu ne in suka ce wai ba Sadiq din su ba ne.
Sadiq ne shine ajikin wannan Hoton ba wani ba.
Sajida ta katse mata Tunani da fadin"Me zamu je yi a zariya?
Surayya ta mike ta na fadin"Sanin gaskiya, da kuma sanin abunda ke Boye game da Rayuwar kanin mu da bamu sani ba Sajida."
Sajida sai ta kasa mgana itama har taji idanuwanta ya kawo kwallah.
Me sadiq ya ke aikatawa ne a wannan garin? Daman shiyasa ya nace ma garin, har Sa'insa ya fara yi da su saboda haka ashe ashe.

Allah yasa ba abunda suke zargi ba ne Allah ma yasa kama ce ba shi ba ne.
Surraya tace bayan su uku kada wani yaji wannan mganar sai ta gama Bincikan gaskiyan Lamarin
Sannan tace ko Sadiq kada su bari ya Fahimci wani abu.
Za su je zariya kuma zasu tono abunda Sadiq ya dad'e ya na Boye musu.
Daman kuma ta Fahimci hakan Tuntuni, rashin Hujja ce yasa ba ta taba Furtama kowa ba.
Sun Rabu da Sajida akan sai goben, Direban mijin Surayya zai tukasu zuwa zariya, ita kuma Saddiqa daga bangaranta surayya tace ta jira su Dawo daga zariyan
Saddiq ita kanta hankalinta a tashe ya ke, Wayau ta yi ma Khairiya tace ashe Hasiya kawar wata kanwarta ce, sai daga baya ta ganeta, daman kuma ta rasa lambarta ta na son adireshin Hasiya saboda kanwar nata na son in ta shiga zariya taje wajen Hasiya.

Shine khairiyan tace bari ta yi ma kanwar nata mgana, sai gashi har da lambar Hasiyan aka Turo mata.
Daga khairiya har Safiya ba su san abunda hakan zai haifar ba.
Ballatana Hasiya da ke chan bata san abunda ke faruwa ba.
Uwa uba Uban gayya Sadiq da ke chan Abuja kan aikinsa bai taba kawo ma kansa abubuwa zasu lalace masa batare da ya sani ba.

*Janafty*
*TMWBK3004*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65

*LAME NIG!*

*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*

Washegari.
Zariya.
Chapter 10 · 0% Book details