Sashe 45
Tmw Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Umma ta gaji da jin mganganunsa ta mike ta daka masa tsawa kafin tace"Kaji kunya, kai yanzu Saboda Mace ka ke zagin yan'uwan ka?. Mace ma wata bakar Annoba wacce ta so kashe ka."
Kafin Sadiq ya yi magana ya Rigasa da cewa"Salamatu ki koma ki zauna."
Cikin mamaki Umma tace"Abban siyama."
Kallonta ya yi yasa bata karisa mgana ba ta koma ta zauna.
Shi kuma Abba sai ya kalli Sadiq kafin yace"Kyalesu hakanan ai ka yi musu iyaka, nima kuma na shata musu layi matukar ba alheri ne zai kai ku kusa da iyalamsa ba kada ku kara zuwa, sannan mgana ta karshe duk abunda kuka san kun amsa daga Hannunta ku taka da kafarku kuje ku maida mata sannnan ku tabbatar da kun bata Hakuri, in kuma ba haka ba wlh dukkan ku sai na yi mummunan saba muku"
Suna jin abunda Abba yace suka fashe da kuka gabadaya wannan karon na gaske ne.
Tunda ba su dauka har Abba zai Bud'e musu wuta haka ba, Umma kuma da suka Dogara da ita Abba ya hanata mgana.
Sajida cikin kuka tace"Don Allah ka yi hakuri, mu fa Umma ce ta ce mu je mu koreta ba laifin mu ba ne."
Umma ta kallesu ta na Hararansu Abba ya ya hade rai kafin yace"Ya rage naku, ni dai kun ji matsayata itama wacce ta saka kun zata karbi nata Hukuncin daidai da abunda ta aikata."
Zasu fara magiya yace su tashi su bar masa falo.
Shi daman Sadiq yana gama mganarsa ya fita ransa bace.
Suka tashi suna sharan kwallah suka Fice, suna fita Umma ta kalli Abba tana fadin"Abban Siyama ai ba laifi ba ne domin na saka an kori wannan bakar Annobar, wacce ta so ka kashe mana d'a daya Tilo namiji da muka Haifa"
Ko kallonta Abba bai yi ba taga ya Dauki waya ya na Dannawa ba ta ankara ba sai da taji suna gaisawa da Mallam zakari ta Rude.
Tana rokonsa da ido da Hannu ammh Abba ya yi kamar bai ji ba.
Ya kwashe duk abunda ta aikata ya sanar ma da mallam zakari.
Dagacan bangaren ransa ya baci cikin Fushi ya fara magana Abba na jin haka ya saka mata a amsa kuwwa.
Cikin ba da Umarni Mallam zakari yace"Sulaimanu ka fattake ta daga gidanka Tunda Salamatu ta zama zakka, ni kuma ka sanar da ita Tunda ni Uban banza nake gareta ta bid'i wani gidan Uban ba dai nau gidan ba ka hid'i mata haka Tunda Shawaran ki uwa take mara lissafi."
Abba ya kalleta alamun kinjin dai ko sannan yace ai tana jinsa.
Nan yace a bata waya ya yi ta bacinta Umma tana kuka tana bashi Hakuri ya kashe wayarsa.
Abba kuma ya karbi wayarsa ya mike yana fadin"Bazan kore ki ba, ammh ki sani itace damarki ta karshe, nagaji da d'aga miki kafa salamatu."
Daga haka ya tashi ya bata waje, Sai ga Umma da kuka har shashenta.
Su Sajida da suka zauna ta dawo su kara zugata sai kuma suma suka ga ba Dama.
Sultana dai suka gama zaunarwa suna kara zugata, Umma kam ciki dakinta ta shiga ta maida kofa.
Me ta saka me ta saka oho, ta ga dai bata da mafita su Sajida ma bata san tafiyarsu ba.
Tun safe ta je bangaren Abba bayan Mama ta koma shashenta ta Durkusa ta na bashi Hakuri shi kuma yace bakomai.
Fatansa ta sakama auran magajin gida albarka sannan ta maida masa matarsa tace duka zatayi.
Daga karshe yace bayan suna taje taga Jikokinta ta yi ma matar Sadiq barka taje to.
Ta rokesa ya kira Mallam Zakari yace masa ta bashi hakuri, shi kuma yace sai in yaga da gaske ta ke yi hakurin da ta bashi Sannan zai kirashi ya gayamasa.
Tana komawa bangaranta ta kira Sajida da Sadiya da Sa'adatu tace su shirya suje Zariya suna.
Sannan ta kira Surayya tace ta zo gida tana nemanta.
Daman kuma Surayyan zata Biyo Tunda Abba yace har da Mutanen shinkafi za su tafi Sakeena ta kira ta tace itama zata je.
Ta d'an bata Lokaci tunda ta siya wasu kaya aka kawo mata daga kasuwa, Suba'atu da Saddiqq sun turo kudi a siya ma maijego kaya ita da Twins.
Ta yi mamaki da ta zo Umma na bata Hakurin ta jira sauran yan'uwanta su tafi tare, sai ba ta ja ba tace su yi sauri saboda kada su yi dare kuma sai Gobe za su dawo.
Bata gama mamaki ba sai da Sadiq ya Shigo Umma ta yi masa Barka da kuma saka albarka ya amsa bakinsa har Kunne yaci fararan kaya ya Fito sak angon karni karni.
Kuma nan ta ke Umma ke tambayansa bayan suna Sulatana zata koma dakinta kafin dai ya koma wajen aiki.
Shi yace duk yadda ta yanke daidai ne a wajensa.
Sai dai bai yi kasa a gwiwa ba ya kalli Umma yana fadin"Ita Sultanan na son komawa da gaske?
Umma tace"Eh mana, ni ce daman na hana kuma yanzu na saki Allah ya baku zaman lafiya gabadayan ku."
Sai amswa ya ke da Ameen yana mamakin Umma.
Ita kuma Surayya sai take ganin kamar Umma ta yi sanyi ne na d'an Lokaci.
Saboda jiram su Sajida sai sha Biyu na rana suka tafi tashar Sharon suka yi gabadayan su, Mama bata samu zuwa ba diyar kanwarta ta rasu, Siyama ma bata je ba suna da Jarabawa.
Sakeena ce kad'ai a dakin mama sai Sajida Sadiya, Sa'adatu bata samu zuwa ba wai mijinta ya hanata.
Surayya sai su Goggo Hassu sai Hajiya Innani.
Ba su isa ba sai karfe uku saura na Rana koda suka isa gidan suna ya Tumbatsa da Mutane.
Gida cike fa, nan suka iske Saleema sun zo tun safe daman ta yi ta kiran su sukace suna hanya
Saukar ban girma aka yi musu daman Tunda an sam suna hanya an tanadar musu nasu abincin na musammam.
Shinkafa jallop da alala har da nama sai kunin aya da Zobo.
Ni da kaina nazo har falo muka gaisa na kuma saka Ramatu da Safiya suka kai mu su yaran.
Sun zo sun samu har anyaka Raguna Uku,har an gyara su ma tunda za'a soya da wuri a ba su nasu su tafi da shi.
Sun sameni na yi kunshi sannan na yi kitso, kuma sun iske ni da wata Atamfa da muka yi anko da su Adda Fati har da Ramatu da Safiya.
Na saka less ma da Safe Cikin kudin da Assadiq ya Turomin na siya.
Sannan Maman suhailat ta bani materila na dinka shi shima.
Sai Anty Surayya ta bani leda shake da kaya, akwai dinkakku da wad'anda ba'a dinka ba sai na jarirai da su pamparrs da sabulan wanka tace daga gare su ne.
Turmin Atamfa yafi goma leshi guda Biyu har da mayafai da Hijabai, kayan yaran ma masu kyau da su fin kala goma, kuma damam an kara siya musu wasu, Ramatu da Safiya duk sun gwangwaje ya'yan na su da kayan yara har da takalma da safuna masu kyau.
Su Adda na nuna mawa suna ta Godiya, taro ya yi armashi Sosai duka matan Baba saminu da na Baba Tanko duk sun zo min, su salima da la'asar suka dauki hanyar kaduna.
Ita man jiki ta kawomin na yara Hajiya Murjanatu kuma ta aikomin da Atamfa da kayan yara Fathihatu kuma ta bani kudi.
Kai hatta yan gidanmu ma samaru sun kawo sabulai, Ummi ma tazo ta kawomin kayan yara har Fadila sai gata tazo min suna tare da Ummin suka zo, na kuma san harda gulma ya kawota.
Saboda gidan ya yi kad'an ga baki yasa Adda Fati ta Shiga makotan ta inda suke mutunci gidan maman hanna ta roka aka kai su Anty Surayya can suka kwana da Sassafe kuma aka tashi da aikin suya nama Saboda sun ce da wuri za su kama Hanya.
Sai da Safen ne Sajida da Sadiya suka shiga har dakin da na ke Lokacin mun dawo wanka ni da Inna Talatu.
Ita fita ta yi ta bamu waje, suka nemi gafarata nace musu ya wuce.
Sannan suka bani wayata da Key din dakina tare da Atm din bankina.
Sadiya ce ke sakin Fuska Sajida kuma tunda tace na yi hakuri ta kauda Fuska ni kuma na nuna musu komai ai ya wuce ni dai Tunda suka barni da dan'uwansu ai sun gama min komai.
Misalin sha Biyu na rana suka tafi, Suka bar mim Innani kamar yadda Assadiq yace ta na ko kamkame da ya'yan magajin gida ta bakinta.
Ta dankgwali Hancin wancan tace sulaimanu, sai ta dangwali hancin wancan tace muhammadu, ba ruwanta ita fa Imnani in za'a zauna ta yi ta Hira ba'a gwasaleta shikenan su Adda na shan Labaran su Assadiq da Abba.
kuma ba sakaya komai da komai ta ke fad'a ni dai ina Ta tsoron kada ta je ta fad'i abunda ya faru tsakanina da su Sajida sai kuma aka ci sa'a Hirarta bai kaita can ba.
An diba musu nama da yawa sun tafi da shi, Amma na Abba dabam na Assadiq ma dabam, sai kuma na Umma shima Dabam na su ne aka had'a waje d'aya.
Naji dadin zuwan su kuma hakan ya kara tabbatar min da cewa da gaske ne Assadiq na sona kuma ya Tsayamin.
Su Adda kuma suna ta Hiran sun fara Saukowa, suna ta kuma bani shawarwarin yadda zan kara jawo su gareni a sannu ko Saboda yan yaran nan.
Ni dai jin su kawai na ke yi, zan yi dai iya bakin kokarina ammh ba lalle ne na Burge wasu daga cikin su ba.
Ni dai na sakama raina zan zauna da Assadiq cikin Amana na yi masa Biyayya har karshen Rayuwata.
Saboda ya yi min komai a Rayuwata ko nace ya na kan yi mini mana.
*Janafty*
*TMWB3K013*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65
Kafin Sadiq ya yi magana ya Rigasa da cewa"Salamatu ki koma ki zauna."
Cikin mamaki Umma tace"Abban siyama."
Kallonta ya yi yasa bata karisa mgana ba ta koma ta zauna.
Shi kuma Abba sai ya kalli Sadiq kafin yace"Kyalesu hakanan ai ka yi musu iyaka, nima kuma na shata musu layi matukar ba alheri ne zai kai ku kusa da iyalamsa ba kada ku kara zuwa, sannan mgana ta karshe duk abunda kuka san kun amsa daga Hannunta ku taka da kafarku kuje ku maida mata sannnan ku tabbatar da kun bata Hakuri, in kuma ba haka ba wlh dukkan ku sai na yi mummunan saba muku"
Suna jin abunda Abba yace suka fashe da kuka gabadaya wannan karon na gaske ne.
Tunda ba su dauka har Abba zai Bud'e musu wuta haka ba, Umma kuma da suka Dogara da ita Abba ya hanata mgana.
Sajida cikin kuka tace"Don Allah ka yi hakuri, mu fa Umma ce ta ce mu je mu koreta ba laifin mu ba ne."
Umma ta kallesu ta na Hararansu Abba ya ya hade rai kafin yace"Ya rage naku, ni dai kun ji matsayata itama wacce ta saka kun zata karbi nata Hukuncin daidai da abunda ta aikata."
Zasu fara magiya yace su tashi su bar masa falo.
Shi daman Sadiq yana gama mganarsa ya fita ransa bace.
Suka tashi suna sharan kwallah suka Fice, suna fita Umma ta kalli Abba tana fadin"Abban Siyama ai ba laifi ba ne domin na saka an kori wannan bakar Annobar, wacce ta so ka kashe mana d'a daya Tilo namiji da muka Haifa"
Ko kallonta Abba bai yi ba taga ya Dauki waya ya na Dannawa ba ta ankara ba sai da taji suna gaisawa da Mallam zakari ta Rude.
Tana rokonsa da ido da Hannu ammh Abba ya yi kamar bai ji ba.
Ya kwashe duk abunda ta aikata ya sanar ma da mallam zakari.
Dagacan bangaren ransa ya baci cikin Fushi ya fara magana Abba na jin haka ya saka mata a amsa kuwwa.
Cikin ba da Umarni Mallam zakari yace"Sulaimanu ka fattake ta daga gidanka Tunda Salamatu ta zama zakka, ni kuma ka sanar da ita Tunda ni Uban banza nake gareta ta bid'i wani gidan Uban ba dai nau gidan ba ka hid'i mata haka Tunda Shawaran ki uwa take mara lissafi."
Abba ya kalleta alamun kinjin dai ko sannan yace ai tana jinsa.
Nan yace a bata waya ya yi ta bacinta Umma tana kuka tana bashi Hakuri ya kashe wayarsa.
Abba kuma ya karbi wayarsa ya mike yana fadin"Bazan kore ki ba, ammh ki sani itace damarki ta karshe, nagaji da d'aga miki kafa salamatu."
Daga haka ya tashi ya bata waje, Sai ga Umma da kuka har shashenta.
Su Sajida da suka zauna ta dawo su kara zugata sai kuma suma suka ga ba Dama.
Sultana dai suka gama zaunarwa suna kara zugata, Umma kam ciki dakinta ta shiga ta maida kofa.
Me ta saka me ta saka oho, ta ga dai bata da mafita su Sajida ma bata san tafiyarsu ba.
Tun safe ta je bangaren Abba bayan Mama ta koma shashenta ta Durkusa ta na bashi Hakuri shi kuma yace bakomai.
Fatansa ta sakama auran magajin gida albarka sannan ta maida masa matarsa tace duka zatayi.
Daga karshe yace bayan suna taje taga Jikokinta ta yi ma matar Sadiq barka taje to.
Ta rokesa ya kira Mallam Zakari yace masa ta bashi hakuri, shi kuma yace sai in yaga da gaske ta ke yi hakurin da ta bashi Sannan zai kirashi ya gayamasa.
Tana komawa bangaranta ta kira Sajida da Sadiya da Sa'adatu tace su shirya suje Zariya suna.
Sannan ta kira Surayya tace ta zo gida tana nemanta.
Daman kuma Surayyan zata Biyo Tunda Abba yace har da Mutanen shinkafi za su tafi Sakeena ta kira ta tace itama zata je.
Ta d'an bata Lokaci tunda ta siya wasu kaya aka kawo mata daga kasuwa, Suba'atu da Saddiqq sun turo kudi a siya ma maijego kaya ita da Twins.
Ta yi mamaki da ta zo Umma na bata Hakurin ta jira sauran yan'uwanta su tafi tare, sai ba ta ja ba tace su yi sauri saboda kada su yi dare kuma sai Gobe za su dawo.
Bata gama mamaki ba sai da Sadiq ya Shigo Umma ta yi masa Barka da kuma saka albarka ya amsa bakinsa har Kunne yaci fararan kaya ya Fito sak angon karni karni.
Kuma nan ta ke Umma ke tambayansa bayan suna Sulatana zata koma dakinta kafin dai ya koma wajen aiki.
Shi yace duk yadda ta yanke daidai ne a wajensa.
Sai dai bai yi kasa a gwiwa ba ya kalli Umma yana fadin"Ita Sultanan na son komawa da gaske?
Umma tace"Eh mana, ni ce daman na hana kuma yanzu na saki Allah ya baku zaman lafiya gabadayan ku."
Sai amswa ya ke da Ameen yana mamakin Umma.
Ita kuma Surayya sai take ganin kamar Umma ta yi sanyi ne na d'an Lokaci.
Saboda jiram su Sajida sai sha Biyu na rana suka tafi tashar Sharon suka yi gabadayan su, Mama bata samu zuwa ba diyar kanwarta ta rasu, Siyama ma bata je ba suna da Jarabawa.
Sakeena ce kad'ai a dakin mama sai Sajida Sadiya, Sa'adatu bata samu zuwa ba wai mijinta ya hanata.
Surayya sai su Goggo Hassu sai Hajiya Innani.
Ba su isa ba sai karfe uku saura na Rana koda suka isa gidan suna ya Tumbatsa da Mutane.
Gida cike fa, nan suka iske Saleema sun zo tun safe daman ta yi ta kiran su sukace suna hanya
Saukar ban girma aka yi musu daman Tunda an sam suna hanya an tanadar musu nasu abincin na musammam.
Shinkafa jallop da alala har da nama sai kunin aya da Zobo.
Ni da kaina nazo har falo muka gaisa na kuma saka Ramatu da Safiya suka kai mu su yaran.
Sun zo sun samu har anyaka Raguna Uku,har an gyara su ma tunda za'a soya da wuri a ba su nasu su tafi da shi.
Sun sameni na yi kunshi sannan na yi kitso, kuma sun iske ni da wata Atamfa da muka yi anko da su Adda Fati har da Ramatu da Safiya.
Na saka less ma da Safe Cikin kudin da Assadiq ya Turomin na siya.
Sannan Maman suhailat ta bani materila na dinka shi shima.
Sai Anty Surayya ta bani leda shake da kaya, akwai dinkakku da wad'anda ba'a dinka ba sai na jarirai da su pamparrs da sabulan wanka tace daga gare su ne.
Turmin Atamfa yafi goma leshi guda Biyu har da mayafai da Hijabai, kayan yaran ma masu kyau da su fin kala goma, kuma damam an kara siya musu wasu, Ramatu da Safiya duk sun gwangwaje ya'yan na su da kayan yara har da takalma da safuna masu kyau.
Su Adda na nuna mawa suna ta Godiya, taro ya yi armashi Sosai duka matan Baba saminu da na Baba Tanko duk sun zo min, su salima da la'asar suka dauki hanyar kaduna.
Ita man jiki ta kawomin na yara Hajiya Murjanatu kuma ta aikomin da Atamfa da kayan yara Fathihatu kuma ta bani kudi.
Kai hatta yan gidanmu ma samaru sun kawo sabulai, Ummi ma tazo ta kawomin kayan yara har Fadila sai gata tazo min suna tare da Ummin suka zo, na kuma san harda gulma ya kawota.
Saboda gidan ya yi kad'an ga baki yasa Adda Fati ta Shiga makotan ta inda suke mutunci gidan maman hanna ta roka aka kai su Anty Surayya can suka kwana da Sassafe kuma aka tashi da aikin suya nama Saboda sun ce da wuri za su kama Hanya.
Sai da Safen ne Sajida da Sadiya suka shiga har dakin da na ke Lokacin mun dawo wanka ni da Inna Talatu.
Ita fita ta yi ta bamu waje, suka nemi gafarata nace musu ya wuce.
Sannan suka bani wayata da Key din dakina tare da Atm din bankina.
Sadiya ce ke sakin Fuska Sajida kuma tunda tace na yi hakuri ta kauda Fuska ni kuma na nuna musu komai ai ya wuce ni dai Tunda suka barni da dan'uwansu ai sun gama min komai.
Misalin sha Biyu na rana suka tafi, Suka bar mim Innani kamar yadda Assadiq yace ta na ko kamkame da ya'yan magajin gida ta bakinta.
Ta dankgwali Hancin wancan tace sulaimanu, sai ta dangwali hancin wancan tace muhammadu, ba ruwanta ita fa Imnani in za'a zauna ta yi ta Hira ba'a gwasaleta shikenan su Adda na shan Labaran su Assadiq da Abba.
kuma ba sakaya komai da komai ta ke fad'a ni dai ina Ta tsoron kada ta je ta fad'i abunda ya faru tsakanina da su Sajida sai kuma aka ci sa'a Hirarta bai kaita can ba.
An diba musu nama da yawa sun tafi da shi, Amma na Abba dabam na Assadiq ma dabam, sai kuma na Umma shima Dabam na su ne aka had'a waje d'aya.
Naji dadin zuwan su kuma hakan ya kara tabbatar min da cewa da gaske ne Assadiq na sona kuma ya Tsayamin.
Su Adda kuma suna ta Hiran sun fara Saukowa, suna ta kuma bani shawarwarin yadda zan kara jawo su gareni a sannu ko Saboda yan yaran nan.
Ni dai jin su kawai na ke yi, zan yi dai iya bakin kokarina ammh ba lalle ne na Burge wasu daga cikin su ba.
Ni dai na sakama raina zan zauna da Assadiq cikin Amana na yi masa Biyayya har karshen Rayuwata.
Saboda ya yi min komai a Rayuwata ko nace ya na kan yi mini mana.
*Janafty*
*TMWB3K013*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65